Thursday, April 5, 2007

Dadadan Dadin Saniya; Daga Dr Aliyu Aqilu

Malam Aliyu Aqilu dai ba bako bane ga wanda yasan wakokin Hausa. Asalinsa mutumin Sakkwato ne, duk da yake a Kano yafi shahara, kuma anan iyalinsa suke, ana kuma Allah yayi masa rasuwa. An haife shi a shekara 1918, a garin Jega na kasar Gwandu, wanda a yanzu ke jihar Kebbi. Cikin malaman da yayi karatun alqur'ani a gunsu sun hada da ; mahaifinsa Aliyu Madaha, da kuma Alhaji Muhtar Tsoho, da Malam Muhammadu dan Takusa, da M Ban-Allah, da kuma malam AbdulMumini. Ya fara zuwa Kano tun yana da kamar shekaru 15, babban malaminsa a Kano shine: Malam Mahmudu na malam Salga, kuma Muqaddaminsa na Tijjaniya shine Malam Salga. Ya zauna a Borno shekara 23. Malam Akilu Aliyu gogaggen dan siyasa ne, kuma mai bin akidun siyasar NEPU, kuma sana'ar da aka fi saninsa da ita, itace dinki. Ya samu Digirin girmamawa (Honorary Doctorate Degree) daga Jamiar Bayero ta Kano, kafin rasuwarsa. Ya wallafi wakoki da dama, cikinsu kuwa sun hada da na addini, siyasa, zaman tare, tafiye-tafiye dss. To acikinsu ne na zabo mana daya daga ciki, kafin in Allah ya yarda mu kawo muku sauran, wannan waka kuwa itace wadda fasihin Sha'irin yayiwa Saniya. Ga dai wakar;

Ya mai ni'ima mayawaiciya
Ya mai kudura makadaiciya

Haske da basira naka ne
Ya Rabbu ka buden zuciya

Domin inyi waka yar kadan
Mai yar magana mashahuriya

Amma a takaice a dan mu san
Dimbin amfanin Saniya

Sunce mata dadi goma wai
Wannan magana na dai jiya

Wato maganar na ji ta ne
Karba tata sai na waiwaya

A'a karbarta da lokaci
Sai na juya na waiwaya

Ba goma bama wane dari
Metan suke har da guda daya

Wa za shi iya shi kididdige
Dadadan dadin Saniya

Nan dai a takaice guda darin
Zan zo muku yanzu da dai daya

To sai muyi tsit domin mu ji
Zan fara bayanin Saniya

Mamaki ne da tu'ajjibi
acikin sha'anonin saniya

Tirkashi! O'oi, wane mutum
Sanbarka dau duka saniya

Kin dau kaya kin dau mutum,
Da abinci mutum ya rataya

Kallonta shi sanya farinciki
Kukanta shi sanyaya zuciya

Shafarta shi sa maka walwala
Dubarta idonka shi sanyaya

Ba'a samu guda ba na yasuwa
Daga kowane sashin saniya

Madara, Kindirmo, Dakkashi
Kangar da Cukui daga Saniya

Kassanta ana Alli dasu
Ya kyautu anan in waiwaya

Kashinta ana shafe dashi
Losonmu na da Nijeriya

Kirginta ana wasaki da shi
Mun san haka duk Nijeriya

Har gobe ana kiri da shi
Da gareshi ake bulaliya

Na lura ana Waga dashi
Da gareshi ake yin tsirkiya

Shike daure karaga da shi
Tsani, Barho da Takobiya

shike yin takalma da shi
Kwakkwaran kirgin Saniya

Na lura da shi ke yin kube
Na wuka, Barho da Takobiya

Ka tuna fa da shi ke Janjami
Sai mai girma kan rataya

Baza na yawaita maganganu
Ga yar sa'at magajarciya

Ba nuna gadara ko isa
Ko kasaita matsananciya

Daga nan ya zuwa can ko ina
Acikin duka sassan duniya

Na hanga, zaune a hankali
Kuma na maka duba na tsaya

Wai ko zan gano na yasuwa
Wani dan gutsure daga Saniya

Anya kuwa a same shi dai?
Amsa naka so na tambaya

Shin ko ko akwai abu ne daban
Marashin fa'ida daga saniya

Indai da akwai a fada muji
Daga Sa ya zuwa kan Saniya

Guzuma ta zamo ko Dangwala
Ko Karsana ce ma Sauraya

Amsa a'a ai babu shi
Abu yasasshe daga Saniya

Wannan kuwa ta gamsar da ni
Amsa ke nan makatarciya

Mai haske gata a wartsake
Har yau mai dada zuciya

Wakar sunan dana bata shi
Dadadan dadin Saniya

Wannan jin dadin ya isa
Daga kowane sashin Duniya

Kar wai ku cane gefe guda
Daga kowane barin kun jiya

Me zamu kwatanta ne da shi
Ga misali, sai dai lafiya

Wannan itace duk kan gaba
Daga duk jin dadin duniya

Amma a wadata kowace
Daga kowane fannin duniya

Jama'u-Jama'u duk an hadu
Cewa dai babu ya saniya

Fifiko nata yana gaba
ga na dabbobi duka saniya

Yai nisa basu tara da shi
Ko sunyi gudu sun garzaya

Ba za fa su shawo kan sa ba
Ko sun zaga sun kewaya

Kai ban zaci sa riske shi ba
Ko sun tafiya matsananciya

Abu ne mawuyaci dankari!
Har yanzu wuyar mawuyaciya

Gaba dai, gaba dai, gaba dai, gaba
Gaba, Nagge, da aiki saniya

Ja al'amarinki madaukaki
Gaba dai ba baya ba Saniya

Ja dai sha'aninki na arziki
Ke baki shiga sha'anin tsiya

Madalla, madalla dake
Tsarinki da kyawo saniya

Sannunki nace na gaida ke
ni na yabi aikin saniya

Girman daraja, girman isa
Sannan darajar mayawaiciya

Taure yace a sanar dake
sakon akuya da na Tunkiya

Sun mika wuya sun sallama
Cewa a nada ki sarauniya

Sun sa hannu da guda-guda
Sun lamunce daga zuciya

Rago tuni shi ya sallama
Dauke shi jakada saniya

Dabbar da ta ja gaba dake
Ta dau wahala matsananciya

Gurbin riba sai faduwa
Sai rarraba hajjar mujiya

Tsini akaje nema gaba
Kunda ta gagara tun jiya

Wannan magana bata fadi ba
Wa zaya gaya mini "Kai tsaye"

Jama'a daga nan zan dakata
In sanya alama in tsaya

Ni naku Aliyu Aqilu ne
amsa a wajen maitambaya.

3 comments:

Anonymous said...

Assalam, naji dadin samun wannar wakar. Don ALLAH kusa mana wadda yake cewa.

Yaro nemi diyar dattawa
sanda kake zaka neman aure

Bame gemu ko saje ba
bame gogeggen wando ba
.....................
me magana tasa takar kaure
wanda yace E baya a'a
........................

Anonymous said...

Allah Ya saka da aiheri, don Allah a yi kokari a sa mana wasu wakokin nasa da na sauran mawakan Hausa (rubutattu).

Anonymous said...

Menene ma’anar wasaki