Wednesday, April 4, 2007

Begen Yakin Shuhadar Hadejia; Daga M Ibrahim Katala

Acikin shekara ta 1906 ne, Turawan mulkin mallaka tare da sojojinsu dauke da muggan, makamai suka yiwa birnin Hadejia tsinke. Inda hakan tayi sanadiyyar gwabza wani mummunan fada tsakanin Turawan mulkin mallaka da kuma Jaruman kasar Hadejia masu gwagwarmayar kwatar yancin kai. Hakan yayi sanadiyyar yiwa mutanen Hadejia kisan kiyashi, inda aka kissima cewa, dubban mutane ne suka rasa rayukansu a sanadiyar hakan. Babban abin lura shine, dukkan wadannan dubban bayin Allah da suka rasa rayukansu, sun rasa ne a rana guda, cikinsu kuwa harda Sarkin na Hadeja a wannan zamani, Wato Sarkin Hadejia Muhammadu. Wannan waka ta tattare dukkan abinda ya faru a ranar, ta kuma yi cikkakken bayani gameda yadda Shahidan Hadeja suka jajircewa abinda suka kira, bautar dasu acikin kasarsu. Koba komai, wannan ya nuna yadda yan Afrika suka dauki yancinsu da muhimmanci. Da fatan Allah ya jikansu, nake cewa ga abinda ya samu;

Allahu sarki Shi kadai yake Wahidun
Sammai da kassai, Jallah bashi da kishiya

Shi ba fari, shi ba Baki ba Ubangiji
Ba ja ba, ba alkashi ba, shi ba rawaya

Ba sake-sake ba, ba kamar yarani ba
Shudi da kore Jalla bashi da mai kama

Zatinsa baya tattara, ba rarraba
Da kawai da motsi babu yayi ko daya

Sarkin da ba na biyunsa, ba na ukunsa
Fahami basira zani begen shahidi

Ranar Talata mun ga tashin duniya
Ranar Muhammdu yai shahada zahira

Yayi jawabi ya cane shi bai gudu
Shi bashi mai kamu a daral duniya

Rago akan kora, a bishi a kam masa
Amma sadauki ba gudu sai faduwa

Sarki Muhammdu yai jawabi ya cika
Shi bashi mai kamu ya ja shi ya tunkiya

Dan Mele Sarkin Yaki shi kuma ya cane
Muna da rai Sarkinmu baya kamuwa

Ma'aji Salihi yai jawabi ya cane
Mun dau shahada zahira bahakikiya

Manya da yara duk shirin yaki su kai
Kowa yana wanka, yana kuma Alwala

Kowa yana sallama cikin ahli nasa
Sun sa gabansu a lahira ba dawaya

Jama'ar Hadejawa dada duk suka hallara
Kowa yana ce "yau ma zama shahidai"

Shi bai kamar tsoro, balle ya razana
Kan ya ije ma babu kingin hamzari

Ajali idan yai babu kwana duniya
Kai dai zamo kullum shiri duk safiya

Shi bai kamar tsoro, balle ya razana
Bai san gudu dan Garba sarki jarumi

Mutuwa tafarki ce kowa zaiyi ta
Kullu nafsin kowanne ya dandana

Aka daura sirdinsa ya hau bisa ya tsaya
Yace "mu dau himmar shahada Zahira"

Sarki Muhammdu bashi tsoro ba gudu
Allah, Ma'aiki su yake tsoro kadai

Hauninsa Linzami mayani ya rike
Damansa tsabihi salatin musdafa

Dan maikaratu, tudun kasa ba dawaya
Dan Garba, jikan Sambo sarkin adali

Duka mai shahada auwalinsu Madacima
Suka barace shi da fari, ya mutu shahidi

Farkon hawan yakin Talata kun jiya
Galadima, Sarki Haruna sune awwali

Alkali, Sarkin Yaki, Kaura Ahmada
Sarkin Arewa sun kaje can tsaye

Suka jeru har da nan kofar gabas
Kafin su zabura mairuwa ta tarda dasu

Kasan Igwa, da fari aka yamutsa
Doki mutum na faduwa ba lasafi

Igwa tana tashi madafa na zuba
Yau sai ta Allah babu Sauran shawari

Sadaukan Muhammadu basu tsoro ko gudu
Sun dakace kofar gida sai faduwa

Sabo, da jikan Tete su harbi suke
A nan a kofar fada duk suka tuntsure

Firyan Hadeja, shi da Bori na Salihu
Kofar Gabas suka fadi duk sun tuntsure

Ai babu mai mutuwa gaban ajali dada
Kan surfa gero, kan daka, wasu kan fita

Hukunci idan Allahu yayi nufinsa
Ba mai tsimi balle dabara ko daya

Tamkar kamar inuwarka baka guje mata
Kan kai gudu ta bika, kai tsai ta tsaya

Attas yana yawo kamar burduduwa
Tamkar zubar wake, acan a masussuka

Ya ratsa soraye, ya rada katanguna
Kamar kabewa, ko kamar tunfafiya

Ya sha zarar Soro, ya ratsa katanguna
Kago da zaure sun fi karfin lasafi

Tsarnu da kurna hakka sa durumi dada
Yansa dabinai, cediya da itatuwa

Rannan musulmi munga kayan al'ajab
Allah ma'aiki su kadai ne magani

AbdulWahabu baka yana hannu nasa
Attas ya samar, nan ya datse tsirkiya.

domin karin bayani, sai a nemi litttafin Dr Haruna Wakili, na Mummbayya House Kano, maisuna Zuwan Turawa Hadejia.

7 comments:

Anonymous said...

ASSALAM NAYI FARINCIKIN GANIN WANNAN KOKARI DA KAYI ALLAH YA SAKA AMMA NI,ABINDA NAKE SON SAMU SHINE TARIN HADEJAWA DA YAKIN DA SUKAYI GABA DAYA,WATAU,YAKIN SU NA GIDA DA KUMA TARAWA.

Unknown said...

assalam gaskiya na jinjina maka da wannan kokari da kayi,amma ni nafi son na samu tarihin hadejawa da yakin da suka yi gaba dayan su.

Anonymous said...

karfarryish
[url=http://healthplusrx.com/migraine]migraine[/url]
KambillianO

maryam Bagel said...

Wannan waka ta raunana zuciyata. Lalai bakaramar wahala akasha ba a kasar hausa lokacin zuwan turwa. Wannan ya can-can ci yazama darasi a azuziwa, domin bai dace ace mutane basu sanbe da irin wayannan dimbin tarihi

Anonymous said...

I've read some excellent stuff here. Definitely worth bookmarking for revisiting. I surprise how so much attempt you put to make such a great informative web site.

Here is my weblog; Bucket truck
My page - used bucket trucks

Anonymous said...

I’m not that muсh οf a online гeader to be honest but уour sites really nicе, keep
it up! I'll go ahead and bookmark your site to come back down the road. Cheers

My blog post: how to make money uying and selling cars

Anonymous said...

I lοve rеading an article that wіll make mеn and wоmеn thіnκ.
Also, many thanκs fοr allowіng for me tο сomment!


Нere is my site search engine optimization dallas