Monday, April 16, 2007

Wasiyya Sipikiyya; Daga Mudi Spikin

Ta'ala ina rokonka ranar da zan cika
Kasa in cika Allah cikin daki na

Gaban duk iyali na da 'ya'ya da 'yan'uwa
Allah ina rokon ka sai a gidana

Idan na cika yan'uwa na gaya muku
Da kun ji cikawata ku taru gidana

Idan har da rana abin yazo ko cikin dare
Batun jinkiri kar dai ya faru wurina

Idan anyi sallah an gama kar a dakata
A dauka kawai hanyar zuwa kabarina

Idan anka je da zuwa a sani ciki kawai
Cikin hankali domin tuno lamarina

Kasar kabarin kuma kar a ware daban-daban
A turo gaba daya duk ta watsu a kaina

Idan aka kare gini da an tashi an gama
Ku koma wajen harkarku ya jama'ata

Batun sadakar Uku, ko Bakwai, ko ta Arba'in
Kaza shekara wallahi babu ruwana

Irin masu kukan nan da ihu da razana
Don Allah na roke ku kar kuyi kaina

Ina tausayin ku kwarai zuwa gun jana'iza
Kaza wahalar tafiya hakan kabarina

Kaza wahalar wanka da dauko ni don zuwa
Cikin makara tafiya zuwa karshe na

Hakika a rannan da da ikon da zan iya
Ya sa tausayin a wajen dukan jama'ana

Anan zan tsaya domin wasiyarmu ta tsaya
Mudi Spikin ne uba ga Amina

5 comments:

Sagir abba sumaila said...

Yau Allah ya nufa an cika masa wasiyyarsa, Allah ya jikansa, ameen.

Abubakar Lawan said...

Allah kaji kansa kai masa rahama, ka sanya shi cikin amintattaun bayinka, ka yafe laifukansa, ameen.

Unknown said...

ALLAH Ya jikan Alh. Mudi spikin, Allah Yai masa rahma, Ya yafe masa. Ameen

Thatg wap said...

Allah yai masa rahama

Anonymous said...

Allah yajikansa ya sa Aljanna ce makomarsa. Nasamu abubuwa masu amfani acikin wannan wasiyya tasa.