Monday, April 16, 2007

Wakar Shehu malam Nasara Kabara; Daga Mudi Spikin

Bagadada suna ajabi nasa
Don sun ga irin himma tasa
Suka ce kai wannan ya isa
Har yanzu suna Allah yasa
Su ga Alhaji malam Nasiru

Qadiriyya yai zurfi ciki
Darajarta kwarai yai arziki
Jama'a da yawa duk sun saki
Hairi a gare shi daki-daki
Kuma ga takawa gun Nasiru

Shi gwarz ne mai kokari
Mai kamala mai kyawon shiri
Ga mutunci gashi da hankuri
Ko ina an san shi gari-gari
Kwarjini sai Malam Nasiru

12 comments:

Anonymous said...

Salamu alaikum,
M. Fatihu,

Godiya ta tabbata ga Allah madaukaki, tsira da amincin sa ya sadu da halarar maikin sa.

Gaskiya na ji matukar dadi da na ga wannan qasida ta malam domin dama haka ya kamata a rika fitar da irin wannan abubuwa musamman irin su malam kabara wadanda suka yiwa musulunci da musulmin africa ayyuka wanda tarihi bai kamata ya manta da su ba, kuma ina fata idan akwai kari dan allah a saka don wadanda basu kai darajarsu ba suna sakawa.
Allah ya saka maka da alhairi kuma gafara ba sai ka rasuba Allah ya yi maka ita ameen.

Naka: Alphateh assammany
Umdurman-Sudan

Anonymous said...

Da fatan a gyara sunan Malamin Nasir(U)

Na gode

Anonymous said...

salam,

malam fatihu Allah yasaka maka da al hairi Amin, dafan za'a zakulo mana ragowar wakokin sheikh Nasiru kabara na hausa.
kuma don Allah kamar yadda naga wani yaroke ka a gyara sunan malam din daga Nasara zuwa Nasiru duk da dai daya ne domin kuwa yasami Nasarar, to amma anfi sanin sa da Nasirun.
Allah yasa mudace Amin.

Maifatan Alhairi gareka
Muhammad Almaghili
Kano.

MUNIR ABUBAKAR TANIMU said...

salamu alaykum.
wallahi abin yayi min dadi da naga irin wannan kokari naka malam fatihu,babu abin da zance ni dai sadai nmayi fatan Allah yasa ka da alkairi kuma Allah yayi albarka.
kuma nima MUNIR na bude irin wannan waje amma na USSAQUN NABIYI sai dai ban gama kammalashiba amma da zarar na kammala abin zanyi shela ga kowa wanda shi kuma wannan ya shafi kungiyar nan ne ta usshaqun na biyi wanda malam ibrahim kaulahi yake jagora.
DAGA MUNIR ABUBAKAR SANI MAI NAGGE KANO

Anonymous said...

Sorry for my bad english. Thank you so much for your good post. Your post helped me in my college assignment, If you can provide me more details please email me.

Anonymous said...

Peut connecter un autre ordinateur sur mon réseau influencer les connexions des autres ordinateurs?

Saratu musa gwammaja said...

Maulana amiril jeshi ana kiransa dana kabara ko muce malam dan in akace malam to ni nasan ko wa ake nufi

Anonymous said...

What's up Dear, are you truly visiting this web site on a regular
basis, if so afterward you will without doubt obtain nice experience.



My blog :: referencer site

Gombe said...

Salamun alaykum, lallai irin wannan namijin yunkuri ya cancanci jinjina. Allah ya saka da alheri domin muna barin turasin mu yana tafiya hadaran
Ina bada shawari da a raya turasin sheikh Dan Fudiyo domin ba'a kyautawa na baya ba idan aka bari ya wuce haka. More grease to your elbow. May God help us.

Hasani kabara said...

Allah yasaka

Unknown said...

Allah ya saka' da fatan za a kara kokartawa a kara jefo mana wasu

Anonymous said...

Dan Allah ina neman rubutacciyar"Wakar jalla Sarki sonka nake..." T maulana Nasiru Kabara.