Thursday, October 30, 2008

Wakar Abinda

Ita dai wannan wakar, malam Umaru Salga ne ya baiwa Mischlich, wani baturen mulki na kasar Jamus, a yayin da yake kokarin tattara bayanai akan tarihin kasar Hausa, domin manazarta dake can kasar Jamus. A cewarsa, "wani almajiri ne ya auri wata mata maisuna Abinda, amma kuma ita Abinda kazama ce ta kin karawa, to a saboda haka sai ya shirya mata wannan waka. Ka nemi kasidar M. B. Dufill domin samun karin bayani.


1 Abinda kazama ce kwarai, ba kadan na ba.

2 Ina son k i bar halin da duk, bai kamata ba.

3 K i zam yin fa shara, kuma kina dumke farkuwa.

4 Iya t a mutane, duk ba ta bar abin ga ba.

5 Tuwonki k i zam gyara, kisa 'yan ruwa kadan.

6 Tuwon j iya kin bata , shi mu ba mu c i shi ba.

7 Idan kin y i min damun fura , saita yamutse.

8 Fa ko na ji yunwa, ba ni iya shan furalkiba.

9 Abin ga da kumya kuma da haushi ga zuciya.

10 Abinda k i bar halin ga, duka bai kamata ba.