Wednesday, April 18, 2007

MAIGANJI; Daga Malam Muhammadu Namaiganji

Ba dai wani takamaimiyar magana, akan kowanene Malam Muhammadu Na Maiganji, ba kuma tabbacin lokacin da ya rubutata. Amma insha Allah, zan kawo cikakken bayani a gameda wakar ta Maiganji. A yanzu dai ga wakar Maiganji

Bi Bismillah ni bawa, na far yabo ga mai baiwa
Arrahmani baiwarsa, gamamma ce ga dan kowa
Rahmani ya kebe baiwarsa, baya yiwa majusawa
Allahu yai dadin tsira, ga Ahmadu shugaban kowa
Baicin ambaton Allah, nufina gargadin kowa

2]Wanda ya yada addini, baya tambayar kowa
Girman kai ya debe shi, ya sashi ya fandare wawa
Yaku yan uwa dangi, Allah ya halicce mu
Domin tsaida addini, Tawhidi kaza Sallah
Musan Azumi da Zakkarmu, kaza Hajji wajibin kowa

3]Mu sansu, mu sanda yayanmu, kaza matanmu bayinmu
Kanko mun ki sanasshe su, ranar lahira ka sani
Acan aka tambayar kowa, akan doran siradinsa
Ga kaifi, ga makonansa, Kama nan za'a tsaishe ka
Idan yazo dasu ya shige, idan bai zo da kome ba
Wa'ila sai su turo shi, cikin zurfin wuta wawa

4]Bayi na ciki su cane, ya kaitonka kai bawa
Ina halinku ma'aikinku, ya kance 'sun isar da sani'
Iyaye sun ka bashe mu, suna aikin majusawa
Kan ance da su su bari, su kance 'mu iyayenmu
Mun same su sun aika, abinda su kanyi shi zamu bi, bama jin fadar kowa

5]Ka duba can ga kakanku, , Adamu, Nuhu, Idrisu
Da Ibrahim uban kowa, Manyan Annabawa ne
Sun bi fada ta Allahu, tazo har kan ma'aikinmu
Kowak ki ta ya ratse, yabi fadar Yahudawa

6]Yahudu, Nasara sun ratse, shaidani ya rude su
Yace ku tsaya a nushe ku, ga aikin iyayenkuAbin bautarsu su gunki, gama shine mashasharku
Kar ku bi annabin kowaYa jama'a ta addini, bin Allah farillansa
Bin manzo cikin sunna, wanda ya yada bin sunna
Kamar bai aika komai ba, kamar dai wanda yai sallah
Bai zakka ba ya tabe, cikin bin Jallah mai baiwa

7]Wanda ya bauta Allahu, yana sabon iyayensa
Bai karba ba sarkinmu, ka tuba ka bisu kai wawa
Ya mai bauta Allahu, nemi halas abar cinka
Kan ko tabe, haramun wanda ya cita
Misalin gwargwadon lauma
Kwana Arba'in za ai, yana bauta ga sarkinmu
Bai karba Allahu, Jallah ubangijin kowa

8]Ina Malam, Ina Malam Malam tsorci Allahu
Kabar tsoron mutanenka, fada musu gaskiya hakkan
Kan sun bita ka huta, kan sun ki ta ka kubuta
Wurin Sarkinmu Allahu, Jallah Karimu mai baiwa

9]Zan muku gargadi dangi
Ku kai yayanku gun malam
Karatu wajibin kowa

10]Wanda ya samu da nasa, Yaki ya kai shi gun malam
Ya dau alhakin dan sa, Yahudu, Nasara sun samu
Kaza suma majusawa, Kowanne da
Ka haifeshi, duk jama'ar Ma'aikine
Sai babansa yaki shi, yakan koma Nasarawa

11]Malam nemi sarkinka, kace masa yai fadan bidi'a
Bidi'a kishiyar Sunna, kowab bita y rates
Yabi fada ta shaidani, yaki fadar ma'aikinmu
Muhammadu Annabin kowa, wanda yabar fadar MammanYana nushe shi kan turba, Yana kimso cikin jeji, yana yawo kamar giwa

12]Mai yawo cikin jeji, kan yaje cikin jama'a
Mazaje masu bin Allah, suna taro gidan malam
Ko jam'a ta yin sallah, baka ga shi baya sheka yana cigiyar, bata wawa
Koda nace, da ko daji, ba daji na kura ba

13]Ko acikin gidnsa yake, yaki yaje gidan malam
Shi san Allah, bazai Sallah, kace masa
Mai shiga jeji, zaya bace cikin njeji, Babu gudunmawar kowa
Maza mata ku nemi, fada tasa shugaban kowa

14]Wanda ya bar fadar Mamman, yaki fada ta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, Wanda yabar fadar Allahu
Ya kafirta ya watse, yabi safun
Abu Jahalin, Abu Lahabin da wansunsu
Yana koyi da su wawa

15] Ya jama'ar musulminmu, mai kaunar yasan Rahma
Yabar aure cikin idda, Allah bai hallata ba
Ma'aiki bai halatta ba, Malam ya cane ka bari
Kana yi kaito kai wawa
Mutum uku munji sun rates, limamin da ya daura

16]Waliyin wanda ya aiko, da mai nema cikin idda
Sun ko sun ki bin turba, Ta annabi shugaban kowa
Su duka mun ji sun ratse, da wadda ta karkace idda
Har jama'ar da tai shaidar, asasu wuta
Cikin karfe, su kuna ba ruwan kowa

17]Inai muku gargadi dani, maso jinkai
Ya same shi, Yai auren halaliya
Ya dauki ruwa da gammonsa, ko ya saya
Da kurdinsa, Ruwan wankanta ko sallah
Hadisin shugaban kowa.

18]Wajibne ga da namiji, yai bauta ga matansa
Kadan yalwa ta same shi, kadda su durkusa
Dutse, Ni fan day a bare mai yawa
Fadar nan duk da nayita, nib a shisshigi
Nai ba, ka bi ta kabar batun kowa


19]Wanda ya kama matansa, da cinsu da shansu ya dauka
Yana yi gwargwadon iko
Tamkar wanda yai sadaka, har ma yafi mai sadaka
Wurin sarkinmu Allahu
Jalla karimu mai baiwa

20]Ka nemi halas ka cishe su, Allah zai biya kowa
Kadda ka nan haraminya, kowac cita ya kuna
Sai ya tuba ya barta, Rahimu ya maida jinkansa
Allah Rahimin kowa
Yaku masu bin bidi'a, da kun tuba kun barta

21]Kun bi fadar ma'aikinmu, bin farali da bin sunna
Kowa mai hana ku barin, Yalwa sai ta same ku
Dabbobi sa wadaceku, Kishirwa babu
Ko yunwa, bare yafi ya daukeka
Bare bautar Nasarawa

22]Ku shirya zasu bashe ku, kui damara ta bin
Mamman, ku tserewa Nasarawa
Ku bar waka ta shaidani, kui zikiri na bin Allah
Halshe an halitta shi, dan zikiri
Da yin kalma, ku bar zagin ubankowa

23]Ku bar zambon iyayenku, Gwarabjawa
Da Maiganji, ku tuba ku bar gamin kowa
Mai zagin iyayensa, mu mun sami labari
Can a wutar Yahudawa

24]Mu mun sami labariAcan a can a wutar Yahudawa
Macizai har kunaminta, suna dako su cije shi
Kan sun sami bakinsa
Sukan kama suna yago,
Su kan taye kamar yawa.

25]Kunaminta na harbi dubu saba'in,
Karin nasu gaba daya zsu soke shi
Su zarta jikin maki Allah, masabin dan Kuraishawa
Muhammadu wanda yaki ka, shi darajarsa ta tauy
Anan duniya gidan Darbashan, inda Dayyanu mai sakawa dan kowa

26]Ina makadi maki Allah, da shi da ubansa shaidani
Da mai murnar abinda su kai, Allah ya la'ance su
Ma'aiki ya la'ance su, Mala'iku na Allah suma
Sun la'ance su, mutane masu bin sunna
Suma sun la'ance su

27]Kifi maigida a ruwa, shima ya la'ance su
Tsuntsu maigida a sama, shima ya la'ance su
Duk bayio na Allahu, basu san su
Domin kinsu bin Allah
Ta'ala wanda yai kowa

28]Mai ganga maki Allah, kan ya dauki Gangarsa,
Ya kanje dandali nasa
Shaidani yakan tashi, yana gayya gidan kowa
Kowa amsa gayyarsa, can zai kaishi gun gayyu
Shiko Gayyu Zaza ne, cikin zurfin wuta wawa

29]Kowa tuba ya huta, Allah rahimin kowa
Ku tuba ku daina yin bidi'a, Allah ya jikan kowa
Ina makadi uban bidi'a, mai sababinka kin Allah
Yai maka hannu da kafa, ya baka idanu da kafa
Da baki duk da kunnenka, wa zai kirga baiwarsa da yai maka ja'iri wawa

30]Kaki ka gode baiwarsa, menene tsakaninku
Kana bijirar da bayinsa, kana ta kidi suna waka
Kana bauta ga shaidani, kun ki ku bauta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, ku bar bauta ga shaidani
Nufinsa yaje ya yashe ku, ya kai ku cikin wuta wawa

31]Ina makadi uban bidi'a, da kun tuba kun bit
Allah sai ya yafe ku, Rahimu Ubangijin kowa
Kan ance su bar Bidi'a, su kan ce tun iyayensu
Da kakanni ake yinta, shi sabonsa
Tun nan, basa jin fadar kowa


32]Ku duba tun iyayenku, da kakannin iyayenku
Sha sabon karatun nan, suka tarda shi wawa
Ina jin tausayin dangi, basa tausayin kansu
Sun ki su kama bin turbar
Muhammdu shugaban kowa

33]Fitar mata zuwa jeji
Suna nema da dan gyaftoSuna cin kasuwar lahadi...........

34]Yaya ne ka auro su, ba bayi ka auro ba
Kabar su suke fita yawo, tsorci
Ubangiji Allah, Ta'ala wanda yai kow
Ko bayi ka same su, kanka bukace su
Auransu kadda ka bar su su yawo, fada ta ubangijin kowa

35]Kuna cewa iyayenku, basu bada su da ka-
Kanninku, Addini na Ibrahim, yai tsari ga matansa
Sahhabai dukka sunyi tsari, dan kakanku yaki tsari
Ba sauki akai masa ba
Shi ne yaki bin turbar Annabin kowa

36]Fadar Allah Ta'ala ce, zaman mata cikin daki
Kun ki fada ta Allahu, kuke fusshesu gun narko
Bar kallon fadar Allah, ko sarkin kasa ya fadi
Kan ka ki ta ka tashi, gidanka
Da shi da gonarka, don ka barshi bayanka

37]Ka sheka kana yawo, cikin ZazzauKaza
Katsina, ko birnin Kazaurawa
Kamarka mutum kakewa gudu
Ka rasa zamna gidanka
In ka ki fadar Allah, ina magudarka kai wawa?

38]Mala'iku su kamo ka su saka
A sasarin karfe, a sundukin bakin karfe
Sai ka tuba ka barsu, kai hakuri
Da noman so, Allah sai ya yafe ka
Domin bin uban Kasim, jikin Hashimiyawa

39]Ina mai annamimanci, da mai hassada
Da mai ruwa, da mai zina ja'iri bawa
Da mai suka ga addini, da mai gaba
Da malumma, da mai karya cikin jama'a
Da mai zuku yana tazidu............

40]Mai zina ya shiga ya shiga uku, radda ka tada yan adam
Da aljannai da wansunsu, du da mala'ikun Allah
Ana kallonsa duk jama'a, yayi baki bakin zunubi
Kai kace bakin wawa
Da shi da abokiyar la'ana, gabanta kamar ruwan miki

41]Tana yoyo cikin jama'a, kamar randa data burme
Ga doyi kamar kuna
Kaman nan zai kusance ta
Yana lasa da bakinsa
Kamar lasar kare wawa

42]Jahannama can tana dako
Akai mata jairin bawa, maki sarkinmu Allahu
Maki jin gargadin kowa
Mai riya zamu zancansa, maki zancen
Ma'aikinmu, maki jin gargadin kowa

43]Manzo ya cane ya bari, Shirka ce wurin Allah
Shiko yaki mai shirka
Wanda ya bada kayansa, don a fada a cane
Wane, jikan wane, dan wane
Shaidani ya rude shi, don ya batar da shi Wawa

44]Shi bai nemi lada ba, wurin sarkinmu Allahu
Shi dai duniya ta fadi, suit a yabonsa yan
Adam, sun ace ba kamar wane, domin
Sunga wawa ne, shi bai san da karya ba
A’a ya sani it ace, yake bautar kwanikawa.

45]Ina wawa maki turba, fahimci abinda za
Ni fadi, Allah ya halitto ka, dan bautarsa
Ka ki sani, kana neman taro da kwabo
Kaki ka nan shinan Sallah, bar kallon taro da Kwabo
Ko kasan Sule da Dala, ko rumbu guda ka cika, sai wata ran mala’ika, ya dauke ran yabar gawa.

46]Su kai ka su sa cikin rami rami, su lullube
Yar kasa su rufe, su juya can wurin karfe
Suna ta raba sub a naka, Anini guda
Basa baka, Kwabo ma yafi karfinka
Kanan shinan Sallah sai itace, wurin bawa cikin kabarinsa kai wawa

47]Ku san neman taro da kwabo, halaline wurin Allah
Kan ka san shinan Sallah, kadan ko ba shinan
Sallah, haramunce gad an kowa
Allah yayi wo bawa, dan bautarsa kai wawa
Kai ko ka ki bautarsa, dan neman taro da kwabo, ka duba arzikin bawa
47]Rababbe ne wurin Allah, abinda ya bashi ya bashi
Da zai hau samaniya yana neman dadi
Babu yace ya gode mai baiwa
Godewa ga sarkinmu, bin sa da
Bin ma’aikinmu, da bin ulama’u kai wawa

48]Lura fadar da nai bawa, kan ka kita ka tabe
Ba azumi bare sallah, duk aikin addininka
Ba lada wurin Allah, sai ka tambayo malam
Allah yaki addinin
Da ba’a tambayar kowa

48]Azaba can tana dako, ga bawa wanda yaki sani
Kamanan wanda yayi sani, baya aiki da shi
Wawa ku bar wasa ku nemi sani
Said a sani ake samun gidan Rahma
Wurin Sarkinmu Allahu, Ta’alas wanda yai kowa

49]Ana wa’azin bakin bawa, dillalin bakin bawa
Wanda yaje cikin kurmi, yana yawo da ka-
Yansa, kan ace da shi ya cira, yakan ce
Yafi karfinka abinda akan tayi goma, yakan ce Sha Biyar ka taya,
Ba tsoro bare kunya, yaki fadar ma’aikinmu, bare maganar ubankowa.

50]Kiyayi riba haramunce, wanda ya cita zai kone
Ka tsoraci ubangiji Allkah, Tabaraka wanda yai kowa
Karya ma haramunce, kabar san yenta kai wawa
Mai karya cikin jama’a, shi kan keta bakinsa
Yakan je har zuwa keya, kadan karyarsa ta shahara

51]Allah ya la’ance shi, a sa la’ana a goshinsa
Kowag ganshi ya san shi
Duk dabbar gida da dawa, kan tag an shi ta san shi
Ta ce Alhamdu lilLahi ni nagode sarkinmu
Tunda yayi ni ni dabba, naïf makaryacin bawa, mugu fajiri wawa

52]Ina bawan dake hassada, ya tuba ya daina yin hassada
Kan ko yaki ya kone, yana haushin
Rabon Allah, zato nasa ja’iri wawa
Zani yabon ma’aikinmu, tsattsarka uban Kasim
Baban Fadima Zahra, mai hakuri uban dayyabu, Sidi Balaraben kowa

53]Mai haske da kyau Mamman, Mai saje da kyawun
Fuska, gashi da kyan bakin gashi, bashi da furfura
Da yawa, cikin sajensa har gemu
Kan ka san guda goma, kana neman biyar ka dada
Baka samu ba sai ka tsaya, kana kallon wushiryarsa

54]Ga haske yana tashi, turare ma yana tashi
Kamshi ya buche kowa
Ana ajabi da sawunsa, Kan ya taka kan dutse
Wurin takun yakan gurbi, kan ya taka
Rairansa, baka gurin ba yai gurbi, hukumcin Jalla mai baiwa

55]Dadai ka gani bawa, yadda ka tsaida yan adam
Wurin ikonsa Sarkinmu, ranar kaga jayayya
Iyayensu da yayansu, mazaje su da matansu
Sarki shi da fadawa, dogarrai da sauransu
Har da yace da babansa, kai ka batar dani Turba

56]Kana ji na ina ihu, nakan zallko ina juya
Kai ko ka ki yin tsawa
Kowa ya kira dansa, yana nusheshi
Bin turba, kai ko ka ki nushe ni
Bare nabi annabin kowa

57]Ina Magana ga dattijo, tunda ya bar fadar Mamman
Ya ki fada ta Allahu, jallah ubangijin kowa
Yara su da manyansu, kan suka dubi kankanci
Su kance Rabbu sarkinmu, mun bi ta
Shugabanninmu, su suka bi damu turba

58]Rabbu ka fara bashes u, sui nisa da jinkanka
Jallah ubangijin kowa
Wadanga da su da manyansu, jayayya takan
Rude, sukan ce mu musulmi ne
Bad an ku ba manyanmu, su suka ce da su a’a, …………

59]Sukan ce ba Kaman nan ba, ko kace mu bar turba
Mui bautar wanin Allah, ace fa su daina jayayya
Akai su wutar Nasarawa, fadar wa’azi da nai dangi
Don mai hankali na fadi, koda nace daku waka
Tunda ya sa dani acikin, musulmi masu san baiwa

60]Acikin mutane masu yin Sallah
Suna karbar fadar Mamman, Sidi balaraben kowa
Salatin Lahi Sarkinmu, ya tabbata
Ya tabbata nan ga manzonmu
Muhammdu mai dubun baiwa

61]Da aloli da as’habu, damu mabiya umarninsa
Ana ranar dab a bawa, mai debe kewa
Kan ance daku waka, wanene matsarinta
Ku ce masu kankanin bawa, malacin gayyi
Aikin karatu ya buwaye shi, na Qur’ani kaza ilimu, sai sururi abin wawa

62]Cikakken hankalin bawa, yai sauki da surutu
Sakankance da wautarsa,
kan ya yawaita surutu
cikin taro, wajen jama’a
Ku taru gidan zaka wawa.





9 comments:

Anonymous said...

Asslam alaikum

sannu da aikifa,

gaisheka da babban aiki ina fatan uban giji ya taimakeka kaima katai maki mutanenka da al'ummarka,

a gaskiya , na dade ina bakin ciki da damuwa bisa rashin samin ingantaccen tarihin arewan nigeria, wanda mutanenmu suka rubuta da hannunsu, duk kittifan dana samu naga cewa ,ba yan kasarmune suka rubuta suba,

akwai wata tambaya danakeso nasan jawabinta,
ina fatan kana dashi kuma

yaya yanayin islama yake a garin hausawa , kafin zuwan dan fodio , idan akwai shi kenan?

akwai wnai littafi aka rubuta akan wannan maudu'i?

kuma inaso nasan indan ka rubuta littafi akan tarihin malamanmu , wanda suka rigamu gidan gaskiya da wanda ke raye,
abin bakin cikine cewa , ni nakasa samin wani takaimaiman llittafi da mutanenmu suka rubuta akan tarihinmu da addinimu da adabinmu,

kafin muslunci da kuma bayan shigowar addini garuruwanmu,

ina godiya tareda fatan alkhairi

wasslam alaikum

yyyu said...

Mallam Fatihu. Na gaisheka nima.
Amma ina so ka saka wakokin Akilu Aliyu da yawa. A gaskiya ina son nazartar su.
Yakubu

Anonymous said...

I would like to exchange links with your site shairai.blogspot.com
Is this possible?

Anonymous said...

Hi, I think your website might be having browser compatibility issues.
When I look at your blog in Firefox, it looks fine
but when opening in Internet Explorer, it has some overlapping.
I just wanted to give you a quick heads up!

Other then that, amazing blog!

Also visit my web page; pirater un Compte Facebook

Anonymous said...

I'm extremely inspired together with your writing skills and also with the structure to your weblog. Is that this a paid subject matter or did you customize it yourself? Either way keep up the nice quality writing, it's
rare to see a great blog like this one nowadays.
.

Also visit my homepage - Dragon City Cheat Engine

Anonymous said...

Why viewers still use to read news papers when in this
technological world everything is accessible on web?


My web-site Generateur de Code PSN

pak muliadi said...

KAMI SEKELUARGA MENGUCAPKAN BANYAK TERIMA KASIH ATAS BANTUANNYA MBAH , NOMOR YANG MBAH BERIKAN/ 4D SGP& HK SAYA DAPAT (350) JUTA ALHAMDULILLAH TEMBUS, SELURUH HUTANG2 SAYA SUDAH SAYA LUNAS DAN KAMI BISAH USAHA LAGI. JIKA ANDA INGIN SEPERTI SAYA HUB MBAH_PURO _085_342_734_904_ terima kasih.

KAMI SEKELUARGA MENGUCAPKAN BANYAK TERIMA KASIH ATAS BANTUANNYA MBAH , NOMOR YANG MBAH BERIKAN/ 4D SGP& HK SAYA DAPAT (350) JUTA ALHAMDULILLAH TEMBUS, SELURUH HUTANG2 SAYA SUDAH SAYA LUNAS DAN KAMI BISAH USAHA LAGI. JIKA ANDA INGIN SEPERTI SAYA HUB MBAH_PURO _085_342_734_904_ terima kasih.

KAMI SEKELUARGA MENGUCAPKAN BANYAK TERIMA KASIH ATAS BANTUANNYA MBAH , NOMOR YANG MBAH BERIKAN/ 4D SGP& HK SAYA DAPAT (350) JUTA ALHAMDULILLAH TEMBUS, SELURUH HUTANG2 SAYA SUDAH SAYA LUNAS DAN KAMI BISAH USAHA LAGI. JIKA ANDA INGIN SEPERTI SAYA HUB MBAH_PURO _085_342_734_904_ terima kasih.



Anonymous said...

Malam Muhammadu Na Maiganji mutumin Maiganji ne . Maiganji kuma tana gabas da Danbatta a kasar Kano. Babban malani ne.ya shahara. Gardawa sun lakanci wannan wake nasa. Ya fito daga babban gida a Maiganji . Kuma kabarin yana nan kudu da Maiganji.
Har yanzu zuriyarsa na nan a wannan babban gida kuma zaka samu bayanai daga manyan da sukai saura, inshaAllah.

Anonymous said...

Allah ya jikan shi da rahama