Friday, March 23, 2007

Sha'iri Audi Gwandu - Kigon Mawaka

Da yawa basu san wannan bajimin mawakin ba, Audi Gwandu dai jikan Sarkin Gwandu Halilu ne (1833- 58). Amma duk da cewar shi dan sarauta ne, ba'a samu cikakken tarihinsa ba. Amma dai an hakikance shi a zamaninsa mutafannini ne, kuma Arifi. Yayi karatu a hannun Sarkin Tambuwal Umaru Dan Buhari, kuma Sufi ne na kin karawa. Audi yafi sha'awar yawace-yawace, wannan nema yasa ba'a samu mafi yawan ayyukansu da kuma rubuce-rubucensa ba.
Ya fara rubuta wakokinsa tun wajen 1864, kuma ya rayu har zuwa lokacin turawa. Biyu daga cikin wakokinsa da na ci karo dasu, sune wakar da ya rubutawa shahararren jarumin nan wato Garba Jamborodo, sai kuma wata waka da yayi, sai kuma wata waka da yayi a gaban sarki musulmi Ahmadu dan Atiku.

Ance wata rana, sarkin musulmi ya takali Audi da batun waka. Inda ya kalubalance shi da in ya cika sha'iri kuma fasihi, yayi masa waka da baitukanta zasu ringa karewa da "K'O" Ai kuwa nan da nan Audi ya shiga aikinsa. Ga dai kadan daga cikin wakar

Wata safiya gida zaka yita,
Wata ko kayo kana bako.

Wani kai ka bashi, wani ko shi baka
Wani ko tutut, yana roko

Wani ya taho kamat bai taho ba,
Wani na gida ana sako

Wani sai hura ga masakki ya shata
Wani ko yasha ga dan koko

Wani saurayi samaki gare shi
Inya biyo asha Kiko

Wani saurayi kabuli gareshi
Inya biyo ana leko

Wata baibaya ga Bunu ka yo ta
Wata ko ayo da jan Bako.......

Wannan kadanne daga irin gudunmawar Audi Gwandu. Ga mai son yasan wakarsa da ya rubutawa Garba Janborodo, sai ya nemi Kasidar Dr Bello Said, wanda yayi akan tahmisin wakar da Sambo Wali ya rubuta, kuma wacce ya gabatar a Harsunan Nijeriya XIX 2001. CSNL, BUK.

2 comments:

Fatuhu said...

Wannan kawai somin tabi ne

Anonymous said...

very nice.you are a true northerner.