Tuesday, April 17, 2007

TABARKOKO; Daga Sarkin Zazzau Aliyu Dansidi

Wannan dai itace wakar Tabarkoko, wadda sarkin Zazzau Aliyu Dansidi ya wallafa. Wakar dai gugar zana ce, ko kuma ince shagube da bai nuna wanda yake yiwa ba. Amma ana zaton ko yayi tane domin yiwa fadawansa shagube, game da yadda suke tafiyar da rayuwarsu.

Aboka zo nan mu bata
ka dubi dan dai ga wata
wada daban da batta
Haske na rana da wata
Ba zasu zam daidai ba

He dubi dai tsettsewa
Ya samu kifi a wuya
shina zaton babu kaya
Inta kafe mai ga wuya
ba zasu debe mai ba


He dubi dai irame
Can tai gida a rame
Can dauri kau ta rame
kyaushe mijin Irame
gallonsu ba zaki ba

Abin ga dai gama na
kare shi tono magana
zai iske kura a hana
ba dun akwai wata magana
da bai fito rannan ba

Ai ga fage ga doki
Noman fako ba taki
ai maganan ta sake
da dan kare da na doki
ba zasu zam daidai ba

Mu namu ga ta da taki
babu biri ba zaki
barde dubu mai doki
da zamanin kai taki
da bamu samu nai ba

Saura garin ya waye
duk kokuwan tai kaye
Damu ga yan tawaye
da masu da da maye
zamansu bai zam dai ba

Karya take zabira
bata zama gurara
Iska daban da sarara
matar maza da bera
kudinsu bai zam dai ba

Na ganshi duk ya kwabe
Yayi tabo ya tabe
yayi bago ya rabe
Neman jini ga babe
Ba za'a samu nai ba

Zo ka taba dai ka jiya
Yau muke koko jiya?
Haure ka ciwo ijiya
in yayi sai ayi jinya
ba za'a debewa ba

Ko ka iso, ko ka tsaya
Taunan aya ko ka iya?
Amale cimansa kaya
Jaki, da sa, ko akuya
Ba zasu taunawa ba

Kaya ga Rakumi shike
Takarkari sai taiki
Saimo akanwa taki
Tsaiko akanwa daki
bukka ba ta dauka ba.

Makaryata, mahassada
basu iya komi da guda
na yanzu ba ko da na da
tara su dai duk ka gwada
ba su zamo daidai ba

Babba da jaka ya zaka
Yana bidan kifi tsaka
gulbin da dorina tsaka
Gefen kadanni ya saka
kafansa ba zai kai ba

Yada guda ka dau guda
Duk ka fasa su ba guda
hanya mararraba guda
gaba-gaba akan guda
cikinsu bai ba daya ba

Ga kutu ga Tabarkoko
Ga dole-dole tai hako
ni naga tana ga fako
kai mai bago shiga sako
Wurin ba'a zo mai ba

Kwaddo ina kadangare
Naji kafarsa ta kare
ya bar diyanshi gangare
in yayi nan sai a tare
ni ban gano zai kai ba

Ko kaga mai digirgire
wuya awa gadar zare
Takuna zance hantsare
da zamanin bakin zare
da basu sa riga ba

Ga tsada mai dan tashi
kullum ta dau albashi
ba ta ci bata hana bashi
ran da safiya tai fashi
ba za'a koka mai ba

Ga wani tantalwashi
na biyunsu mai kan bashi
na ukkunsu bashi da nashi
Da dai ana tuna bashi
da basu sa riga ba

Nazundu mai zaka fada
kullum ka gana da rada
roko awa dan makada
a baka bashi a dada
ba zashi fasawa ba

Ga wani wai shi ya iya
yaje ya jawo igiya
ta nannade mai a wuya
yana kira da waiwaya
ba za'a debe mai ba

Shin me ya samu shamuwa
na ga tana ta dimuwa
naga ruwan da kainuwa
ba dun kasan da kaguwa
da bata sauka anan ba

Da kunkuru da bushiyta
halinsu dai noke wuya
ga zamani na waiwaya
da zamanin mazan jiya
ni naga da basu kai ba

Debi yawa, sam ma kadan
yanzu yawa ta zam kadan
a hankali kadan-kadan
Gidan yawa kan yi kadan
Abinga ba banza ba

Nai muku waka ta batu
ku zo ku nemi yan batu
awa su lugegen batu
tara fasihai na batu
ba zasu ganewa ba

Mai wagga waka ta batu
Ali Amiru wan Shatu
Shine abokin Warqatu
Dadai da sirri na batu
Da bashi boyewa ba

Allahu shi yai mu duka
Baki fari yai su duka
Shudi da Korensu duka
Da Ja da Rawaya duka
Shi dai kayi ba wani ba

Zama fa shi dai ya iya
Shi yo mutum shi tafiya
Wadansu ko shi yi su tsaya
Shi yai itace da kaya
Nufinsa ne ba wani ba

Shi yai dawa da karkara
Shi yai dawa da karkara
Shi yai kwai, yai zakara
Yai zabuwa, yai fakara
Shi ad damu ba wani ba

Bautanmu dai hasana'u
Zam haufu, duk dada rija'u
Ku lura ko asma'u
Nisa'u masu gina'u
Sha'aninsu ba karko ba

Asma'u an sanki da dai
Halinki ki ne ko can dadai
Shirinki kullum na kwadai
Maso biyu,bashi da dai
Batun ga ba karyaba

Ywaita rokon Jalla
Ka wakkale ga Allah
Ka zam kula da Salla
A baka ni'ima walla
Anan da can ba waiba

Muyi zikiri da salati
Mu karkare afati
Gobe mu san najjati
Ga shugaban hajati
Muhammadu bawani ba










Monday, April 16, 2007

Wasiyya Sipikiyya; Daga Mudi Spikin

Ta'ala ina rokonka ranar da zan cika
Kasa in cika Allah cikin daki na

Gaban duk iyali na da 'ya'ya da 'yan'uwa
Allah ina rokon ka sai a gidana

Idan na cika yan'uwa na gaya muku
Da kun ji cikawata ku taru gidana

Idan har da rana abin yazo ko cikin dare
Batun jinkiri kar dai ya faru wurina

Idan anyi sallah an gama kar a dakata
A dauka kawai hanyar zuwa kabarina

Idan anka je da zuwa a sani ciki kawai
Cikin hankali domin tuno lamarina

Kasar kabarin kuma kar a ware daban-daban
A turo gaba daya duk ta watsu a kaina

Idan aka kare gini da an tashi an gama
Ku koma wajen harkarku ya jama'ata

Batun sadakar Uku, ko Bakwai, ko ta Arba'in
Kaza shekara wallahi babu ruwana

Irin masu kukan nan da ihu da razana
Don Allah na roke ku kar kuyi kaina

Ina tausayin ku kwarai zuwa gun jana'iza
Kaza wahalar tafiya hakan kabarina

Kaza wahalar wanka da dauko ni don zuwa
Cikin makara tafiya zuwa karshe na

Hakika a rannan da da ikon da zan iya
Ya sa tausayin a wajen dukan jama'ana

Anan zan tsaya domin wasiyarmu ta tsaya
Mudi Spikin ne uba ga Amina

Wakar Shehu malam Nasara Kabara; Daga Mudi Spikin

Bagadada suna ajabi nasa
Don sun ga irin himma tasa
Suka ce kai wannan ya isa
Har yanzu suna Allah yasa
Su ga Alhaji malam Nasiru

Qadiriyya yai zurfi ciki
Darajarta kwarai yai arziki
Jama'a da yawa duk sun saki
Hairi a gare shi daki-daki
Kuma ga takawa gun Nasiru

Shi gwarz ne mai kokari
Mai kamala mai kyawon shiri
Ga mutunci gashi da hankuri
Ko ina an san shi gari-gari
Kwarjini sai Malam Nasiru

RASHA Abokan Fita Kunya; Daga Mudi Spikin

Wannan waka ta jawowa Malam Mudi dauri a gidan yari. Domin a fahimtar Turawan Mulki wannan wani sako ne da kan iya tunzura talakawa suyi bore, kuma kan iya jefa kasa cikin juyin-juya hali irin na Kwaminisanci. Mudi Spikin ya rubuta wannan waka a 1948. Ga dai wakar

Ya yan'uwa ku zo don ku ji ni
Zan wo bayani akan Rusiya

Gama Ingilishi fa sun tashi haikan
Suka suke yi akan Rusiya

Da babbata hanyarsu don kar a so su
Don kar su zo nan mutan Rusiya

Shine nake so in wo dan bayani
Domin ku gane kasar Rusiya

Kasa ce ta kirki da himma garesu
Da kaunar mutane kasar Rusiya

Wakilinsu Malik sunansa ke nan
Sunan musulmi da ba fariya

Ni dai ace yau zan samu iko
Ni sai in koma kasar Rusiya

Kamar na iya tsunts inje can in Zauna
Idan na tuno su mutan Rusiya

Girmama kowa dabi'arsu ce
Ibada kamar Hajji sai Rusiya

Da son musulunci da bayar da zakka
Yawan azumi sai kasar Rusiya

Kwalta na banza damu bamu samu
Da kafur akeyi acan Rusiya

Da banki na rance idan har kana so
Ko fam Dubu Goma baki daya

Musaki acan sai ya zauna da Gwamna
Wajen shawara babu kin gaskiya

Sa'annan da sauran abubba na kirki
Suna da yawa a kasar Rusiya

Gidaje dubu Goma ne don Musakai
A yau su kasar wane ba ko daya

Akwai Talakawa akwai Tajirai
Kamar dai kasarmu ta Nijeriya

Anan gaba na tabbata babu shakka
Nijeriya zamu zam Rusiya

Mu zam mun fice daga gun Ingilishi
Mutanen daba sa rikon gaskiya

Sun barmu babu kudi babu gona
Babu abin yi cikin gaskiya

Sun shekaru yanzu Hamsin kasarmu
Ba taimako babu son gaskiya

Ta'ala Rahimu kadai taimakemu
Ka kawo mutan Rasha Nijeriya

Idan aka ce wa ya tsara ta waka
Ya bayyana halin mutan Rusiya

Ba zan boye suna ba ko za'a nema
Mudi spikin maso Rusiya

Gama bani tsoro na dauri hakika
Akan Rasha ma sai in bar duniya

Karara; daga Malam Mudi Spikin

An haifi Alhaji Mudi Spikin a ran 1 ga watan Oktoba 1930, a unguwar Darma da ke birnin Kano. Yayi karatun qur'ani a hannun Malam Umaru Badamagare. Bai taba zuwa makarantar boko ba, amma duk da haka, ya zauna jarrabawa GCE Ordinary level, ta hanyar yin rijista da wata kwaleji a Ingila, acikin 1960. Ya sami illimin zamani ne a hannun abokansa na gwagwarmayar siyasa irinsu; Malam Sa'adu Zungur, Malam Aminu Kano, da kuma Alhaji Yusuf Maitama Sule. Yana cikin mutanen da suka kafa jam'iyyar kwato yancin talaka wato NEPU a 1950. Ya fara rubuta wakokinsa tun a 1948, ya fara da wakarsa ta "Rasha Abokan Tafiya", da kuma wani raddi da yayiwa malaminsa, wato malam Sa'adu Zungur maitaken "Arewa Jamhuriya Kawai".

A ya jama'a ina tashin
Ku dan ku rage yawan bacci

Ayau na zo gareku da sha
Wara don kara inganci

Mu wo himma mu tashi tsaye
Mu gyara kasa ta san yanci

Mu kawo shawara mai kyau
Mu tashi mu yaki jahilci

Rashin illimi ya sanya yau
Kasar nan ke yawan baci

Fa sai mun tsaya gyara
Na sosai babu jahilci

Sannan zamu san matsayi
Mu tsere wa wulakanci

Idan ba tattali a kasa
Hakika dole ta baci

Idan an zubda hakkin yan
Adam domin wulakanci

Idan masana kwarai an zub
Da su domin rashin yanci

Idan sharia ta zam ciniki
Ana nunnuna bambanci

Idan kuma masu aiki sun
Zamo duk babu inganci

Idan aiki ya zamto ba
Ayi, sai an ciwo hanci

Idan hairi a baki ake
Fada sharri cikin zuci

Idan da akwai yawan hassada
Da bata mutum da iskanci

Idan da akwai yawanta saki
Na aure don wulakanci

Idan ba tanadi wai duk
Wata sai anyi angwanci

Idan aure ya zam a kasa
Ana yi ne da jahilci

Idan kayan biki aka mai
Da su tamkar na dillanci

Idan ga jahilai a kasa
Na kin canji da shashanci

Idan da zama na banza, ba
Sana'a ai ta kakaci

A sa fatala gaban goshi
Da hula wai tsageranci

Ana ta musu ana karta
Ana zance na wawanci

Idan kuma ga yawan zargi
Na banza ga rashin yanci

Idan wani dan'uwa wai yayi
Samu ayi munafunci

Idan sharri ya zo a iza
Nufi dai ayi wulakanci

Idan da akwai yawan camfi
Da bori masu shashanci

Idan da akwai yawan tsegun
Guman banza na jahilci

Idan a kasa ya zam an go
Yi bayan masu lalaci

Idan mai gaskiya ya zamo
A kullum zai ga kaskanci

Idan gata ya sanya wadan
Su yin shirme da shashanci

Idan aka maida wadansu kamar
Ace bayi rashin yanci

Idan yan kasuwa suka zam
Sana'a aita hainici

Idan ga karuwai a kasa
A kullum ai ta fasicci

Idan da giya an ta
Ru kullm nuna iskanci

Idan ba tausayi a kasa
Mutane na ta makirci

Idan kuma har amana tai
Kadan sai nuna ha'inci

Idan har maluma suka bar
Sani i zuwa fagen baci

Idan bidia ta zam an gir
Gina kuma babu sassauci

Idan yaya suna sabon
Mahaifa har da kaskanci

Idan a kasa akwai wannan
Hakika dole ta baci

Fa sai in anyi aiki za
Hiri ba nuna lalaci

Sa'annan zamu san haske
Mu tserewa wulakanci

Abinda na farfadan nanYan
'Uwa da akwai muhimmanci

Fa duk gyaran wadannan na
Garemu cikin batun yanci

Mu daina abinda bashi da kyau
Mu daina biyewa jahilci.






Tuesday, April 10, 2007

Wakar Kidayar Mutanen Nijeriya 1973; Daga Hajiya Yar Shehu

An haifi Hajiya Yar Shehu a shekara 1937, a garin Dambatta. Ta halarci makarantar Yanmata dake lardin Sakkwato, bayan ta kammala karatun addini a gida. Ta fara aiki a ma'aikatar lafiya ta Kano a 1953, bayan ta koyar a makarantun Firamare. Daga bisani ta koma kamfanin jiragen sama na Kano, a matsayin mai bada hanyar Tarho, inda ta zama jami'ar kula da ma'aikata na ma'aikatar. Haka kuma member ce a shahararriyar kungiyar mawakan nan, wato Hikima Kulob. Ta dai wallafi wakoki da dama, domin fadakarwa, zaburarwa, illimantarwa, wa'azantarwa, da sauransu, wakokinta sun hada da "Waka da Bayani", Wakar Kidaya, Wakar Zamani dss. wadanda insha Allahu zamu kawo muku su, da dai-dai. Ta rubuta wannan waka, domin fadakar da mutane akan kidayar jama'a wato Census da akayi a 1973. Ga dai Wakar;

BismilLah na fara da sunan Rabbana
Allah Ta'ala Jallah Sarkin gaskiya

Kai ne Sami'un Basiru, Mai ji, Mai gani
Ka tsare mu sharrin, masu sharrin duniya

Domin Muhammadu shugaban duka duniya
Har lahira ma, in ka bashi gaba daya

Don Annabawa har Sahabbai Mursalai
Har dukka dangogin Rasulu abin biya

Kayi taimako agareni kai min kangiya
Kai ne katanga wadda bata zagaya

To zanyi tsari dan Kidaya ne yankuna
Ta Arewa harma duk kasarmu gaba daya

Allah Hakimu hikimarka da ta isa
Kasa mu gane don mu bayyana gaskiya

Don kada mu fada ayyukan shibcin gizo
Da ya kasa dauka, sai ya karo kungiya

Ga gargadina gun sarakai malamai
Lalle ku dage don ku kange areriya

Komai idanu bakuna har kunnuwa
Komai ya baci wuyanku ne zai rataya

Ko Shehu Fodiye ku yaba tuta tasa
Har ma amanar dogare gaba daya

Domin hakan nan sai ku tashi ku taimaka
Akan kidayar na jihannunmu gaba daya

Don kadda a kwaso kyankyaso da su kwarkwata
a zazzage mana nan Arewa mu sha wuya

Allah jikansu na baya manya sun wuce
Giwa saka kawo ban Arewa gaba daya

Dan kadda mu ji ta kururuwa rashe idon kuma
Har ma da makirci na mai kin gaskiya

Kuma kadda jahilci ya sa sarkacen tasa
Ya ja kafa kuma har wuyanmu gaba daya

In anka zo kirga ya tabbata mun zaka
Mun bayyana musu dangunanmu gaba daya

Maza da mata har da yara kankana
Har jinjirai ma wanda sun kwana daya

Kuma har da tsofaffi da basu fita waje
Don Allah duk a fade su kar a rage daya

Domin barin wani, baya ba wani taimako
An fidda dashi acikin mutan Nijeriya

Shi bai ga tsuntsu bai ga tarko ya bace
Sai yai nadama nan cikin Nijeriya

Allah tsare mu da yin hakan, ya yan'uwa
Kuma maganin wannan a bayyana gaskiya

Kuyi tir da masu batun na banza kun jiyya
Makiya jiharmu, munafukanta Arewaci Nijeriya

Har ma suna cewa haraj za'a sa
Domin su wargazar da shirin ta areriya

Kuma don a danne tattalinmu na arziki
Har ma a danne komi nan arewa mu sha wuya

Ba'a kidaya kan haraji kun sani
Yara da mata ba'a sa musu kun jiya

Haka ma a zozzowa da tsofaffi duka
Suma haraji ba'a sa musu kun jiya

Wannan kidaya dai nufinta daban yake
Nan dai asan jimlar mutan Nijeriya

Kuma don a san adadin mutanen jihhunan
Jihar da tafi yawa cikin Nijeriya

In an rabo ita zata samu mafi yawa
Ninkin ba ninkin za'a bata kunjiya

Kan duk ku da ayyukan gona duka
Kuma asibitoci makarantu kun jiya

To zasu samu rabo mafi girma duka
To kadda mu cuci jiharmu nan ta arewiya

Duk wanda ycce ma haraji za'a sa
Ce mai haraji arziki ne ka jiya

Mara lafiya da mahaukata basa biya
ashe haraji lafiya ne kun jiya

Sauki gareshi gun manomi kun jiya
Zakkar abinda ya aikata shi ke biya

Yan kasuwa ma sau guda ne shekara
Ma'aikata ne ba iyaka kun jiya

Dukkan wata kullum akan diba ake
Sisi ake diba a kowace fam Daya

Kai malami har malama kuyi anniya
Ku bada sunan yan uwanku gaba daya

Yaya da jikoki da dangi ba ragi
Har wanda basu gida suna wata nahiya

Dada wanda yaki shiga cikin kirga kusan
Shi zaya sha kunya cikin Nijeriya

Sannan ya zam mugu sharari jahili
Mai taimakawa don a cuci arewiya

To malaman Sansan inai muku gargadi
Dan Allah don manzo Rasulu abin biya

Kuma banda kosawa ku dau hakuri kwarai
A wajen kidaya kadda ku dinga tsamiya

Ku bi sannu-sannu a hankali ba firgita
Kuma ba tsanantawa a kowace tambaya

In ko akayi muku tambaya ta rashin sani
Ku bada amsa kadda ku kosa kun jiya

Kuyi ayyukanku da gaskiya bisa ka'ida
Acikin birane, kauyuka har tsangaya

Ahaiyye iyyenanaiyaye yurai yurai
Malam abin ga da niyyi kada kai tambaya

Na barwa Jallah wa'azu sarki mai sani
Ubangiji ya sani kafin ya darsu ga zuciya

To shugaban kirga muna ta sa ido
Muga ayyukan komi yana kan gaskiya

Don kadda azo da ka taho ayi ta gunaguni
Harma takai mu fagen a dinga hatsaniya

kuma kar ta kai ga fagen abin da-na-sani
Ita ko alama ce ta bacin zuciya

Da-na-sani keya a baya take tutur
In an fade ta ku tabbata an sha wuya

Gabas da Yamma, Tsakiya da Arewiya
Muga kan shirin komi ya zam mana bai daya

Don kada a sayar da dubu a kasa sayan daya
Har ma akai ga fagen ace ya rasa kiya

Alhamdu LilLahi ina yin godiya
Agurin Ta'ala Jallah Sarki shi daya

Tamat bi HamdilLahi waka ta tsaya
Waka a gargadinku nan mu gaba daya

a wajen bayani kada ku damu da tambaya
Yar shehu tai wanga tsari kun jiya

In an ka ce adires ku duba ba wuya
Don ni a kofar mata sai kui tambaya

Nagode Allah har Rasulu abin biya
Alai Sahabbai Tabi'ina da Auliya

Baitinta Sittin ba Biyar ba kunjiya
Na rufe da sunan wanda baya fariya

Wakar Zuwan An Nasara Kasar Hausa; Daga Sarkin Musulmi Attahiru

Shine dai Sarkin Musulmi na karshe, kafi mulkin Turawa. Ya rasu a Burmi a ran 27 ga watan July 1903, bayan sun kafsa da Turawan mulkin mallaka. Ya ki amincewa da Turawan da kuma tsare-tsaren da suka zo masa da su, a saboda haka nema ya rubuta wannan waka, domin ya fadakar da mutanensa illar zama karkashin mulkin Nasara. Hakan ya jawo bore a kasar Hausa, wanda ya sanya, turawan suka yi fito-na-fito dashi. Ganin hakanne ya sanya ya bar garin Sakkwato, inda yayi niyyar yin Hijira zuwa kasa maitsarki. Ya rasu tare da mutane da dama, kuma an kama jama'u da dama, cikinsu kuwa hadda Sarkin Kano Alu. Ga dai wakar

Gudun mutuwa da son rai aggaremu
Da kau kin kaddara abi Annasara

Ina muka yi da dama da hauni suna
Ku tashi mu sa gabanmu mu tsira tsara

Idan ka ce akwai wahala ga tashi
Lahan duka na ga masu biyan Nasara

Idan iko ka kai kak ko ki tashi
Ina iko shi kai ikon Nasara

Idan sun baka kyauta, kar ka karba
Dafi na sun ka baka guba Nasara

Suna foro garemu mu bar zalama
Mazalunta da kansu diyan Nasara

Bakar fitina garesu da kau makida
Ta bata dinin musulmi Annasara

Halin da mu kai ga yau aka bayyanawa
Dalilin ke ga an ka sako Nasara

Ku bar jin masu cewa ba'a ashi
Ina halin zama ga Annnasara

Mu mai da gabanmu Makka mu zo Madina
Madina da Makka dai ab ba Nasara

Batu na Shehu yai yi shi bashi tashi
Sa'a ta ya fade ta ta Annasara

Muna da nufa idan mun samu iko
Mu ja daga, mu kore Annasara

Idan ko sun kashe mu mu san shahada
Muje aljanna sai mu ishe makara.

Sai dai an samu sabani tsakanin masana, a gameda waye ya rubuta wannan waka. Dandatti Abdukadir ya bayyana hujjar cewa, Sarkin Musulmi Attahiru n ya rubuta ta. Amma A B Yahaya shi yana ganin wani malami ne maisuna Malam Labbo dan Mariya Kwasare ya rubutata, inda yace ya samo wannan hujja ce daga Waziri Junaidu.