Acikin shekara ta 1906 ne, Turawan mulkin mallaka tare da sojojinsu dauke da muggan, makamai suka yiwa birnin Hadejia tsinke. Inda hakan tayi sanadiyyar gwabza wani mummunan fada tsakanin Turawan mulkin mallaka da kuma Jaruman kasar Hadejia masu gwagwarmayar kwatar yancin kai. Hakan yayi sanadiyyar yiwa mutanen Hadejia kisan kiyashi, inda aka kissima cewa, dubban mutane ne suka rasa rayukansu a sanadiyar hakan. Babban abin lura shine, dukkan wadannan dubban bayin Allah da suka rasa rayukansu, sun rasa ne a rana guda, cikinsu kuwa harda Sarkin na Hadeja a wannan zamani, Wato Sarkin Hadejia Muhammadu. Wannan waka ta tattare dukkan abinda ya faru a ranar, ta kuma yi cikkakken bayani gameda yadda Shahidan Hadeja suka jajircewa abinda suka kira, bautar dasu acikin kasarsu. Koba komai, wannan ya nuna yadda yan Afrika suka dauki yancinsu da muhimmanci. Da fatan Allah ya jikansu, nake cewa ga abinda ya samu;
Allahu sarki Shi kadai yake Wahidun
Sammai da kassai, Jallah bashi da kishiya
Shi ba fari, shi ba Baki ba Ubangiji
Ba ja ba, ba alkashi ba, shi ba rawaya
Ba sake-sake ba, ba kamar yarani ba
Shudi da kore Jalla bashi da mai kama
Zatinsa baya tattara, ba rarraba
Da kawai da motsi babu yayi ko daya
Sarkin da ba na biyunsa, ba na ukunsa
Fahami basira zani begen shahidi
Ranar Talata mun ga tashin duniya
Ranar Muhammdu yai shahada zahira
Yayi jawabi ya cane shi bai gudu
Shi bashi mai kamu a daral duniya
Rago akan kora, a bishi a kam masa
Amma sadauki ba gudu sai faduwa
Sarki Muhammdu yai jawabi ya cika
Shi bashi mai kamu ya ja shi ya tunkiya
Dan Mele Sarkin Yaki shi kuma ya cane
Muna da rai Sarkinmu baya kamuwa
Ma'aji Salihi yai jawabi ya cane
Mun dau shahada zahira bahakikiya
Manya da yara duk shirin yaki su kai
Kowa yana wanka, yana kuma Alwala
Kowa yana sallama cikin ahli nasa
Sun sa gabansu a lahira ba dawaya
Jama'ar Hadejawa dada duk suka hallara
Kowa yana ce "yau ma zama shahidai"
Shi bai kamar tsoro, balle ya razana
Kan ya ije ma babu kingin hamzari
Ajali idan yai babu kwana duniya
Kai dai zamo kullum shiri duk safiya
Shi bai kamar tsoro, balle ya razana
Bai san gudu dan Garba sarki jarumi
Mutuwa tafarki ce kowa zaiyi ta
Kullu nafsin kowanne ya dandana
Aka daura sirdinsa ya hau bisa ya tsaya
Yace "mu dau himmar shahada Zahira"
Sarki Muhammdu bashi tsoro ba gudu
Allah, Ma'aiki su yake tsoro kadai
Hauninsa Linzami mayani ya rike
Damansa tsabihi salatin musdafa
Dan maikaratu, tudun kasa ba dawaya
Dan Garba, jikan Sambo sarkin adali
Duka mai shahada auwalinsu Madacima
Suka barace shi da fari, ya mutu shahidi
Farkon hawan yakin Talata kun jiya
Galadima, Sarki Haruna sune awwali
Alkali, Sarkin Yaki, Kaura Ahmada
Sarkin Arewa sun kaje can tsaye
Suka jeru har da nan kofar gabas
Kafin su zabura mairuwa ta tarda dasu
Kasan Igwa, da fari aka yamutsa
Doki mutum na faduwa ba lasafi
Igwa tana tashi madafa na zuba
Yau sai ta Allah babu Sauran shawari
Sadaukan Muhammadu basu tsoro ko gudu
Sun dakace kofar gida sai faduwa
Sabo, da jikan Tete su harbi suke
A nan a kofar fada duk suka tuntsure
Firyan Hadeja, shi da Bori na Salihu
Kofar Gabas suka fadi duk sun tuntsure
Ai babu mai mutuwa gaban ajali dada
Kan surfa gero, kan daka, wasu kan fita
Hukunci idan Allahu yayi nufinsa
Ba mai tsimi balle dabara ko daya
Tamkar kamar inuwarka baka guje mata
Kan kai gudu ta bika, kai tsai ta tsaya
Attas yana yawo kamar burduduwa
Tamkar zubar wake, acan a masussuka
Ya ratsa soraye, ya rada katanguna
Kamar kabewa, ko kamar tunfafiya
Ya sha zarar Soro, ya ratsa katanguna
Kago da zaure sun fi karfin lasafi
Tsarnu da kurna hakka sa durumi dada
Yansa dabinai, cediya da itatuwa
Rannan musulmi munga kayan al'ajab
Allah ma'aiki su kadai ne magani
AbdulWahabu baka yana hannu nasa
Attas ya samar, nan ya datse tsirkiya.
domin karin bayani, sai a nemi litttafin Dr Haruna Wakili, na Mummbayya House Kano, maisuna Zuwan Turawa Hadejia.
Barka da zuwa Turakar Sha'irai (Hausa Poets Blogspot). An bude wannan Turakar ranar 23 ga Maris 2007 domin yad'a rubutattun wak'ok'in mawak'an Hausa (amma Sha'iran Najeriya, domin ba mu da masaniya game da sha'iran Jamhuriyar Nijar). Muna bukatar ta'aliki da gyara a kan abubuwan da aka gani a wannan Turakar. Allah Ya ba mu sa'a, Amin.
Wednesday, April 4, 2007
Wakar Kuyangin Sakkwato; Daga Sandan Baba1900
Acikin wasu Kundayen adana rubutattun wakoki dake National Archives Kaduna, an tsinci wani File mai No O/AR 2, wanda ke dauke da wata wakar ajami, wadda F Edgar ya samo a shekarun farko na karni na 20. Acikin File na 20 ne wannan waka take, wadda aka hakkake an kattama shi acikin shekara 1911. Bisa ga dukkan alamu Edgar ne ya kwafi wakar da hannunsa, cikin wata takarda falle daya, wanda aka tabbatar da cewa, zai wuya a samu inda ya kwafo wakar. Amma duk da haka ya rubuta sunan wanda ya kwafa, ko kuma ya wallafi wakar wanda ya kira da Sandan Baba. Sai dai kuma bai bayyana kowaye shi wannan Sandan Baba ba, ko kuma mutumin ina ne shi, ko a ina ya ganshi, kwafa yayi daga gurinsa, ko kuma reara masa yayi, shi kuma ya rubuta, Allahu a'alamu? Sai dai a wani File mai no 61, wanda aka sanyawa kwanan wata kamar haka; 1909, an rubuta wata waka maisuna "Wakar Yabo/Bege" , daga Sandan Baba mutumin Sakkwato, inda aka bayyana cewa, Sandan Baba ya rerawa wani malami wai shi Malam Bako wakar, shi kuma ya rubuta ta. Wannan ya dan bada haske na gano cewa, Sandan Baba dai ya reara wakar ne, inda Malam Bako da Frank Edgar suka kwafe ta, ko kuma shi malam Bako ya kwafa, shi kuma Edgar ya samu a wurinsa. Bisa ga dukkan alamu, Edgar bai san Sandan Baba ba, amma yana da masaniya akan Malam Bako.
Wakar dai ta kunshi abubuwa uku, akwai Zambo, Habaici da kuma Yabo. Badai takamaiman kowa akewa wadannan abubuwa, ko duk mutum daya ne, ko kuma mutane da dama. Amma dai kusan sanin kan kowane cewa, abune ba sabo ba ga Yanmatan kasar Hausa, su kirkiri waka don Yabo ko Fallasa, da sigar Gada. Don haka tabbas wakar dai ta Yanmata ce, da suka rera, saboda wasu dalilai da dama.
Ga dai wakar yadda take:
Shiririta ararrata
Kare gadon gida yayyo
Bani bukinka da shara
Sai ranar zuwa aiki in baka taro ka futassan
Farin wake na banza ne
Ko an matsu ba'a gumbatai
Bambeni ka gara gije
Kurche gidansu tag gado
Domin Biri a janye kadarko
Bika da shirin tuma yazzo
Kwa bace ni in rama
Don ba shi ka chi san ba
Anini mai kammarSisi
Da tsakka gashi fudajje
Kwabo kau mai kamar Fataka
Da tsakka gashi fudajje
Mai-Gwanja gaton shigifa
Na mallam-dan-majidadi
Mai kyautar dala da dala
Na malam-dan-majidadi
Diyal laka ta banza ta
Don bata zuwa tayo wanka
Diyal Danko ta banza ta
Don bata fita cikin rana
Zancen daka sai mata da miji
Hanyar bisa dole sai tsuntsu
Garar kasa maganin ajiya
Zago mai fanfatse kaya
Bani zuwa ga yanboko
Gara nazo ga yan madara
Dan boko sai hawan doki
Amma ba kudin sati
Mai rai duk masami ne
Zabarma akwai bidar kuddi
Limamin gidan Joji dogo ketare ka ciro
Har ya manta wando nai
Kuku da Boyi sun rantse
Sai sun dauki yar gwari
Tulu dai ka shan yawo
Randa na nan cikin daki
Mai rai duk shi dau himma
Ayi ta batun bidar kuddi
Dan kawo rinin Allah
Madilla masoyina
Namijin kuti mai kafar kwabi
Har ya raina matatai
Randa na cikin daki
Allah shika bata ruwa ta sha
Tukuruwa mai kaya boye
Gawo da kayarka ka girma
Tataka sai aba doki
Nama sai aba Zaki
Tafarnuwa ta faye yaji
Amma ga maganin sanyi
Dabino farkon ka Baure ne
Acan karshe kake zaki
Anini dan mutan Lokoja
Bana yazo kasar Hausa
Kwa doke ni in rama
Don bashi ka tufasan ba.
Ga mai son jin cikakken bayanin wakar sai ya nemi makalar da Grahm Furniss da Yunusa Ibrahim suka gabatar, mai taken; An Early Twentieth Century Song: "Wakar Kuyangin Sakkwato" A mujallar Harsunan Nijeriya, xvi, 1991/92. CSNL Bayero University Kano. Nigeria.
Wakar dai ta kunshi abubuwa uku, akwai Zambo, Habaici da kuma Yabo. Badai takamaiman kowa akewa wadannan abubuwa, ko duk mutum daya ne, ko kuma mutane da dama. Amma dai kusan sanin kan kowane cewa, abune ba sabo ba ga Yanmatan kasar Hausa, su kirkiri waka don Yabo ko Fallasa, da sigar Gada. Don haka tabbas wakar dai ta Yanmata ce, da suka rera, saboda wasu dalilai da dama.
Ga dai wakar yadda take:
Shiririta ararrata
Kare gadon gida yayyo
Bani bukinka da shara
Sai ranar zuwa aiki in baka taro ka futassan
Farin wake na banza ne
Ko an matsu ba'a gumbatai
Bambeni ka gara gije
Kurche gidansu tag gado
Domin Biri a janye kadarko
Bika da shirin tuma yazzo
Kwa bace ni in rama
Don ba shi ka chi san ba
Anini mai kammarSisi
Da tsakka gashi fudajje
Kwabo kau mai kamar Fataka
Da tsakka gashi fudajje
Mai-Gwanja gaton shigifa
Na mallam-dan-majidadi
Mai kyautar dala da dala
Na malam-dan-majidadi
Diyal laka ta banza ta
Don bata zuwa tayo wanka
Diyal Danko ta banza ta
Don bata fita cikin rana
Zancen daka sai mata da miji
Hanyar bisa dole sai tsuntsu
Garar kasa maganin ajiya
Zago mai fanfatse kaya
Bani zuwa ga yanboko
Gara nazo ga yan madara
Dan boko sai hawan doki
Amma ba kudin sati
Mai rai duk masami ne
Zabarma akwai bidar kuddi
Limamin gidan Joji dogo ketare ka ciro
Har ya manta wando nai
Kuku da Boyi sun rantse
Sai sun dauki yar gwari
Tulu dai ka shan yawo
Randa na nan cikin daki
Mai rai duk shi dau himma
Ayi ta batun bidar kuddi
Dan kawo rinin Allah
Madilla masoyina
Namijin kuti mai kafar kwabi
Har ya raina matatai
Randa na cikin daki
Allah shika bata ruwa ta sha
Tukuruwa mai kaya boye
Gawo da kayarka ka girma
Tataka sai aba doki
Nama sai aba Zaki
Tafarnuwa ta faye yaji
Amma ga maganin sanyi
Dabino farkon ka Baure ne
Acan karshe kake zaki
Anini dan mutan Lokoja
Bana yazo kasar Hausa
Kwa doke ni in rama
Don bashi ka tufasan ba.
Ga mai son jin cikakken bayanin wakar sai ya nemi makalar da Grahm Furniss da Yunusa Ibrahim suka gabatar, mai taken; An Early Twentieth Century Song: "Wakar Kuyangin Sakkwato" A mujallar Harsunan Nijeriya, xvi, 1991/92. CSNL Bayero University Kano. Nigeria.
Sunday, April 1, 2007
Yabon Manzon Allah Daga Dr Aliyu Namangi
Allahu shi bani sani da basira,
In yi yabo bakin ‘karfina.
In yabi Sidi Muhammadu Bawa,
Mai hana sauran bayi ‘kuna.
Yi dad’in tsira Allah da aminci,
Gun manzonka dare har rana.
Da alolinsa da kau sahabbansa,
Da mu mabiyansa dare har rana.
Baicin na cika wannan kalma,
Begen annabi manufana.
Yabon manzon Allah addini,
Shi yafi dace irin sib’ina.
Yabonka Muhammadu nan na fi auki,
Ba ruba bad a d’an damana.
Ba ni da mulki ba ni da aiki,
Begen annabi ne nomana.
Ba ni da guru ba ni da laya,
Sunan annabi ne shingena.
Ba ni da k’arfi ba ni da k’arfe,
In koma Maka ne fatana.
Abin nema a garemu ziyaran,
Wannan d’a mai dad’in suna.
Mai kyau, mai natsuwa, mai kunya,
Sannan ga shi da dad’in suna.
Ina k’aunannka Rasulillahi,
Haske mai dushe zafin rana.
Ina son mai k’aunanka Muhammad,
Ko ya auri d’ayan matana.
Ina kyaman mai k’inka Muhammad,
Ko shi yai mani ragon suna.
Tun da a kai shi yake mashi gandu,
Bai fasaba walau d’ai rana.
Da rana yawan azumi, a darensa,
K’iyamullaili shike duk kwana.
Shirunsa, tunani, kalmominsa,
Gun jama’a wa’azi ko izna.
Allah y a ce ma Ibrahim,
“Na sanya ka maji dadina”.
Ya kuma ce ma Rasulullahi,
“Ka fifita cikin bayi na.
Kai kafi kowane bawa girma,
Don kiwonka da alfarma na
Ba mai daraja tamfalka Muhammad,
Don kiwonka da haddodina”.
Albishirinku masoya Allah,
na ga Amina cikin barcina.
Wadda ta haifi Rasulullahi,
Watan Ramalana a barcin rana.
Na nemi ta sami zama mu yi tad'i.
In cusa shi a wak'ok'i na.
Ban samu ba sabo da lalura,
Don shi na koki irin halina.
Nai fata tahowar fa dalilin,
In koma Maka ne wata rana.
Ko ya zamo shine sanadiyyar
In ga Rasulu cikin barci na.
Ya ce "Bila maza ce ma Aliyu,
Namangi ku zo inuwar sorona".
Mu zo mu ishe yai zaune a zaure,
Ga sahabansa suna kallona.
In gurfana a kan darduma
Hairul Halki yana duba na.
Ya ce mani "Zauna daina sagwangwan,
Kai mani hira kana garkana".
In ce madallah Rasullilahi,
Yau na sami abin nema na.
Tun da na sha inuwar soronka
An warke mani cutocina.
Kuma tun da na zauna cikin sahabbanka,
Yau nai zaune cikin birni na.
Mashigin birnin ya tsarma yak'i,
Ya kuma tsarma hararan arna.
Allah shi ya yabe ka da fari,
Kafin in yi da baubaucina.
Na kuma iske mutanen kirki,
Sun yi da Arbi gaban Hausana.
Kai a ka baiwa Liwa'ul hamdi,
Da tajul izzi da Babban suna.
Wanda ya sa sammai suka zauna,
Taurari da wata har rana.
A kai ma k'asa tuhuwa da yabanya,
Yai ma ruwa a kwari magudana.
Ina k'aunarka Jakadan Allah,
Son, ya zamne cikin bargona.
Don haka in halshe ya yabe ka,
Sai in ji shi cikin kwanya na.
Aka kwab'e halshe na da yabonka,
Har ya zame mani filin gona.
Tuntuni sunayenka Muhammad,
Sun shuka mata baitotina.
Gonar ta yi gamo da yabanya,
Kowa na sha'awar nomana.
Don haka ne fa mutanen kirki,
Kowa ke sha'awar nema na.
In kwana a bene kan darduma,
In sha in ci ana zak'ina.
Ina rok'onka Rasullullahi,
Sa hannunka rik'en dama na.
Ka ce mani "Yadda ka so ka samu,
Yau dai ga shi kana soro na.
Ko yaushe aka tsaida halitta,
Al'amarinka yana hannuna".
Ni na ci albarkanka Muhammad,
Ba ni d'ai ba da 'yan bayana.
Kai tsaye kai yak'i da juhala,
Har muka san darajojin juna.
Ka ci garin yakin kafurrai,
Sorayensu ta komo gona.
Babu ya kai a cikin ta halitta.
Ba za ai shi ba ko wata rana.
Allah shi yi tsira da aminci,
Hal abada a dare har rana.
Kar su gushe ga uban Ibrahim,
Mai zance da wata har rana.
k'asa na alfahari da zamanka,
Tun da ka mai da gumaka gona.
Barzahu na fahari da zamanka,
A tun da ta zammaka soron kwana.
Toya matsafa ratattaka gunki,
Baban Fadima ga hannu na.
Sa hannunka mafi albarkar,
Hannaye, ka rik'e dama na.
Ka ce mani "Yadda ka so ka samu,
Yau banbad'o kana hannuna.
Uwa da ubanka da kakanninka,
Da matayenka kuna hannu na.
Da 'ya'yenka da jikokinka,
Da mai k'aunarka kuna hannuna.
A da Iblis ya cika a yak'i,
Amma yanzu kana hannu na.
Na kwato ka da yardan Allah,
Na jefaka cikin barwana".
Uban Bila baban Salmanul,
Farisa ka ji irin fata na.
Zababbe a halittar Allah,
Kyakkyawa ga sifa har suna.
Mai k'aunar cutarsa ta warke,
Shi ta yabonka dare har rana.
A yabonka Muhammadu ni ne sarki,
Na kau san da mafinfinta na.
Sarauta ta begenka Muhammad,
Ba fahari ba wuni har kwana.
Na gaisheka Rasulullahi,
Amma ka ji irin fata na.
Ran saukar ajali ku halarto,
Har sahabanka wurin gawa na.
Sui mani wanka, kai mani salla,
Har ku had'a ni wurin barci na.
Da albarkanka na Abdullahi,
Da nana Amina nike fata na.
Ka yi min addu'a ga ta'ala Jalla,
Shi gafarta mani aibobi na.
Shi rahama ga musulmi d'urran,
Ba da fari, wuni har kwana.
Ya rufe mu da annuran begenka,
Annabi ka ji irin fata na.
In yi yabo bakin ‘karfina.
In yabi Sidi Muhammadu Bawa,
Mai hana sauran bayi ‘kuna.
Yi dad’in tsira Allah da aminci,
Gun manzonka dare har rana.
Da alolinsa da kau sahabbansa,
Da mu mabiyansa dare har rana.
Baicin na cika wannan kalma,
Begen annabi manufana.
Yabon manzon Allah addini,
Shi yafi dace irin sib’ina.
Yabonka Muhammadu nan na fi auki,
Ba ruba bad a d’an damana.
Ba ni da mulki ba ni da aiki,
Begen annabi ne nomana.
Ba ni da guru ba ni da laya,
Sunan annabi ne shingena.
Ba ni da k’arfi ba ni da k’arfe,
In koma Maka ne fatana.
Abin nema a garemu ziyaran,
Wannan d’a mai dad’in suna.
Mai kyau, mai natsuwa, mai kunya,
Sannan ga shi da dad’in suna.
Ina k’aunannka Rasulillahi,
Haske mai dushe zafin rana.
Ina son mai k’aunanka Muhammad,
Ko ya auri d’ayan matana.
Ina kyaman mai k’inka Muhammad,
Ko shi yai mani ragon suna.
Tun da a kai shi yake mashi gandu,
Bai fasaba walau d’ai rana.
Da rana yawan azumi, a darensa,
K’iyamullaili shike duk kwana.
Shirunsa, tunani, kalmominsa,
Gun jama’a wa’azi ko izna.
Allah y a ce ma Ibrahim,
“Na sanya ka maji dadina”.
Ya kuma ce ma Rasulullahi,
“Ka fifita cikin bayi na.
Kai kafi kowane bawa girma,
Don kiwonka da alfarma na
Ba mai daraja tamfalka Muhammad,
Don kiwonka da haddodina”.
Albishirinku masoya Allah,
na ga Amina cikin barcina.
Wadda ta haifi Rasulullahi,
Watan Ramalana a barcin rana.
Na nemi ta sami zama mu yi tad'i.
In cusa shi a wak'ok'i na.
Ban samu ba sabo da lalura,
Don shi na koki irin halina.
Nai fata tahowar fa dalilin,
In koma Maka ne wata rana.
Ko ya zamo shine sanadiyyar
In ga Rasulu cikin barci na.
Ya ce "Bila maza ce ma Aliyu,
Namangi ku zo inuwar sorona".
Mu zo mu ishe yai zaune a zaure,
Ga sahabansa suna kallona.
In gurfana a kan darduma
Hairul Halki yana duba na.
Ya ce mani "Zauna daina sagwangwan,
Kai mani hira kana garkana".
In ce madallah Rasullilahi,
Yau na sami abin nema na.
Tun da na sha inuwar soronka
An warke mani cutocina.
Kuma tun da na zauna cikin sahabbanka,
Yau nai zaune cikin birni na.
Mashigin birnin ya tsarma yak'i,
Ya kuma tsarma hararan arna.
Allah shi ya yabe ka da fari,
Kafin in yi da baubaucina.
Na kuma iske mutanen kirki,
Sun yi da Arbi gaban Hausana.
Kai a ka baiwa Liwa'ul hamdi,
Da tajul izzi da Babban suna.
Wanda ya sa sammai suka zauna,
Taurari da wata har rana.
A kai ma k'asa tuhuwa da yabanya,
Yai ma ruwa a kwari magudana.
Ina k'aunarka Jakadan Allah,
Son, ya zamne cikin bargona.
Don haka in halshe ya yabe ka,
Sai in ji shi cikin kwanya na.
Aka kwab'e halshe na da yabonka,
Har ya zame mani filin gona.
Tuntuni sunayenka Muhammad,
Sun shuka mata baitotina.
Gonar ta yi gamo da yabanya,
Kowa na sha'awar nomana.
Don haka ne fa mutanen kirki,
Kowa ke sha'awar nema na.
In kwana a bene kan darduma,
In sha in ci ana zak'ina.
Ina rok'onka Rasullullahi,
Sa hannunka rik'en dama na.
Ka ce mani "Yadda ka so ka samu,
Yau dai ga shi kana soro na.
Ko yaushe aka tsaida halitta,
Al'amarinka yana hannuna".
Ni na ci albarkanka Muhammad,
Ba ni d'ai ba da 'yan bayana.
Kai tsaye kai yak'i da juhala,
Har muka san darajojin juna.
Ka ci garin yakin kafurrai,
Sorayensu ta komo gona.
Babu ya kai a cikin ta halitta.
Ba za ai shi ba ko wata rana.
Allah shi yi tsira da aminci,
Hal abada a dare har rana.
Kar su gushe ga uban Ibrahim,
Mai zance da wata har rana.
k'asa na alfahari da zamanka,
Tun da ka mai da gumaka gona.
Barzahu na fahari da zamanka,
A tun da ta zammaka soron kwana.
Toya matsafa ratattaka gunki,
Baban Fadima ga hannu na.
Sa hannunka mafi albarkar,
Hannaye, ka rik'e dama na.
Ka ce mani "Yadda ka so ka samu,
Yau banbad'o kana hannuna.
Uwa da ubanka da kakanninka,
Da matayenka kuna hannu na.
Da 'ya'yenka da jikokinka,
Da mai k'aunarka kuna hannuna.
A da Iblis ya cika a yak'i,
Amma yanzu kana hannu na.
Na kwato ka da yardan Allah,
Na jefaka cikin barwana".
Uban Bila baban Salmanul,
Farisa ka ji irin fata na.
Zababbe a halittar Allah,
Kyakkyawa ga sifa har suna.
Mai k'aunar cutarsa ta warke,
Shi ta yabonka dare har rana.
A yabonka Muhammadu ni ne sarki,
Na kau san da mafinfinta na.
Sarauta ta begenka Muhammad,
Ba fahari ba wuni har kwana.
Na gaisheka Rasulullahi,
Amma ka ji irin fata na.
Ran saukar ajali ku halarto,
Har sahabanka wurin gawa na.
Sui mani wanka, kai mani salla,
Har ku had'a ni wurin barci na.
Da albarkanka na Abdullahi,
Da nana Amina nike fata na.
Ka yi min addu'a ga ta'ala Jalla,
Shi gafarta mani aibobi na.
Shi rahama ga musulmi d'urran,
Ba da fari, wuni har kwana.
Ya rufe mu da annuran begenka,
Annabi ka ji irin fata na.
Wakar Yabon Bawa Jangwarzo (1790)
Bada razana kigon tama
Dan Alasan mai tambari
Bada razana kyauren gari
Bawa kai na magajin gari
Ki gudu sunan sa ne
Sa gudu sunan sa ne
Ni ban ki biya Bawa ba
Ga sirdina aje
Linzami na aje
Kaimi na nan aje
Turkena na nan kafe
Sai rashin doki ag garan
Ba batun yaki munka zo ba
Gaisuwar mutuwa mun ka zo
Da batun yaki mun kazo
Wurno bata yini ko ta kwan
Shiki da dole, tawayen gari
Kankanana nan kajinmu ne
Wadan Galadi, wadan Tubali
Manya-manyan kajinka ne
Kar ka tam musu, sai ran buki
Dan Taka'ida jigon gari
Uban Dawaki Salami
Yai karo da samarin Jitau
sun jisshe shi gaton kaddaji
Hal wayau ma bai tashi ba
Mutan Badarawa ku daina bugun Tanmbari
bawa bai zaka dominku ba
Ku zo mubi jigon gari
Ko mu samu Dawaki mu hau
Da muna tafiya ta gaya mun ka bi
Ko kaya bata soke mu ba
Bawa na Babari, dan Alasan mai shisshinniya
Dan Taka'ida shingen gari
Bawa kai naka bi, babu wargi
ku zo ku bi mai bada kaya
Ko kusan girma nan garai
Ni abinda nike so da kai
Ko ina zaka zo dud da ni
Ni gareka nike taulahi
don in sami farin zuciya
Baiwa kai ka tsiro cin gari
Dan Alasan mai arziki
Yan'uwa ku zo u bi mai arziki
Ko mu sami dawaki mu hau
Dan Alasan mai tambari
Bada razana kyauren gari
Bawa kai na magajin gari
Ki gudu sunan sa ne
Sa gudu sunan sa ne
Ni ban ki biya Bawa ba
Ga sirdina aje
Linzami na aje
Kaimi na nan aje
Turkena na nan kafe
Sai rashin doki ag garan
Ba batun yaki munka zo ba
Gaisuwar mutuwa mun ka zo
Da batun yaki mun kazo
Wurno bata yini ko ta kwan
Shiki da dole, tawayen gari
Kankanana nan kajinmu ne
Wadan Galadi, wadan Tubali
Manya-manyan kajinka ne
Kar ka tam musu, sai ran buki
Dan Taka'ida jigon gari
Uban Dawaki Salami
Yai karo da samarin Jitau
sun jisshe shi gaton kaddaji
Hal wayau ma bai tashi ba
Mutan Badarawa ku daina bugun Tanmbari
bawa bai zaka dominku ba
Ku zo mubi jigon gari
Ko mu samu Dawaki mu hau
Da muna tafiya ta gaya mun ka bi
Ko kaya bata soke mu ba
Bawa na Babari, dan Alasan mai shisshinniya
Dan Taka'ida shingen gari
Bawa kai naka bi, babu wargi
ku zo ku bi mai bada kaya
Ko kusan girma nan garai
Ni abinda nike so da kai
Ko ina zaka zo dud da ni
Ni gareka nike taulahi
don in sami farin zuciya
Baiwa kai ka tsiro cin gari
Dan Alasan mai arziki
Yan'uwa ku zo u bi mai arziki
Ko mu sami dawaki mu hau
Tuesday, March 27, 2007
Wakar Zambon Kazama; Aliyu Namangi Zaria
Ya Allahu Rabbana taimakemu
Mu gargadi yan'uwa ga auren kazama
Auren tsohuwa hasara ga yaro
Gwammaci tsohuwa ga auren kazama
In baka san tane ba kau tambaye ni
In Allah ya yarda kasan kazama
Mummunan halin kazama na fari
Bata fece majina sai da dama
Mai son cin tuwonta sai yaci gashi
Susan hagu na tofi da dama
Hanci majina, idanunta kwantsa
Dattsa ya dadawa bakinta girma
Sai kaga tai gajal da suma da dauda
Ga bauli a kwance, tashinta fama
Bamai son kitso ba, ta kasa aski
Taba ya dafe hakoran kazama
Gude ba kokari ba ga kasa girki
Ga hadama a zuci koshinki fama
Ran girki ba a koshi da jibi
Shi naman miji ki cinye a tsama
In taga ka fito kamar zaka zaure
Sai sababi ya tashi don bata girma
Ka ji "Bar neman fita ina tsame nama
Yau dai kai rabon a zage ka kai ma"
Tunda ka sai kitse ya narke a girki
In aka zo rabo, rabawansa fama.
Wanda ka bashi kankane sai ya raina
Kowa so yake ya karba da dama
Ran nan ma ka sai kashi, na ki zagi
Gun kwarin gidanka mai yada girma
In ta ce dani kazama in rama
Wanda ya san Kumatu yasan kazama
In tace ina da ci ne in rama
"Domin ga Tasallah koshinta fama"
Kwana goma jere, haifanta goma
Ba taran miji ga haifan kazama
Ita ko Bante ta ketara sai ta haifu
In ka san kudi su kare a suna
Ya Allah dadawa matanmu tsabta
Kada Allah ka bamu mata kazama
Tunda mijin kazamiya zai ji kunya
Can Aljanna babu mata kazama.
Mu gargadi yan'uwa ga auren kazama
Auren tsohuwa hasara ga yaro
Gwammaci tsohuwa ga auren kazama
In baka san tane ba kau tambaye ni
In Allah ya yarda kasan kazama
Mummunan halin kazama na fari
Bata fece majina sai da dama
Mai son cin tuwonta sai yaci gashi
Susan hagu na tofi da dama
Hanci majina, idanunta kwantsa
Dattsa ya dadawa bakinta girma
Sai kaga tai gajal da suma da dauda
Ga bauli a kwance, tashinta fama
Bamai son kitso ba, ta kasa aski
Taba ya dafe hakoran kazama
Gude ba kokari ba ga kasa girki
Ga hadama a zuci koshinki fama
Ran girki ba a koshi da jibi
Shi naman miji ki cinye a tsama
In taga ka fito kamar zaka zaure
Sai sababi ya tashi don bata girma
Ka ji "Bar neman fita ina tsame nama
Yau dai kai rabon a zage ka kai ma"
Tunda ka sai kitse ya narke a girki
In aka zo rabo, rabawansa fama.
Wanda ka bashi kankane sai ya raina
Kowa so yake ya karba da dama
Ran nan ma ka sai kashi, na ki zagi
Gun kwarin gidanka mai yada girma
In ta ce dani kazama in rama
Wanda ya san Kumatu yasan kazama
In tace ina da ci ne in rama
"Domin ga Tasallah koshinta fama"
Kwana goma jere, haifanta goma
Ba taran miji ga haifan kazama
Ita ko Bante ta ketara sai ta haifu
In ka san kudi su kare a suna
Ya Allah dadawa matanmu tsabta
Kada Allah ka bamu mata kazama
Tunda mijin kazamiya zai ji kunya
Can Aljanna babu mata kazama.
Wakar Keke; Ta [Dr] Aliyu Namangi
Muna shukura ga Rabbal alamina
Da alherin da yai mana ba kadan ba
Muna murna da mulkin ingilishi
Zuwan da sukai kasarmu ba tai tsiya ba
Zama zamaninsu ne aka zo da Faifa
kudi ba masu nauyaya aljihu ba
Dada zarafinsu ne aka zo da jirgi
Kaje Makka ba da tashin Hankali ba
Sa'annan gasu Babur, ga su Mota
Da farko da can bamu san da su ba
Izan tafiya ta faru ka nemi mota
Izan jirgi ba kui daidai da shi ba
Izan kuwa babu Jirgi babu mota
Ka je da kafarka ba keken tsiya ba
Banni da Basukar Ho! Dan jidali
shakiyyi ba abin Babba ya hau ba
A Dan-Mahawayi nih Hau sai ya barni
Tudun-Yakaji ban kawo gari ba
Ya bar ni da jin jiki da zama a turba
Da dai ko juma'a ba a je dani ba
Kudi tirmis! Na bashi Sule-da-Sisi
keke bai mani rangwame ko dari ba
Na ce masa "Basukur rika sawwakewa"
Yace "Malam hala ba ka sanni ne ba"
"Ina da tsiya biyar farkonsu fanca
Na kau buga bindiga ba mai wuta ba"
In babbake zuciya, in tafi da sawu
Cikin daji kamar ba'a je dani ba
Muna tafiya kuma na fizge kaina
Mu fada kwazazzabo ni ban kula ba
Ina da ciki ana ce mai Kurumbo
Karambanin hawa baka saya ba
Hanjina kaca mai kama riga
In fizgo mai hawa ni ban kula ba
Tsiya na can mu je kan kadarko
Madaidaici in ce ba zamu hau ba
In hau bisa kafadar bari in zauna
Kamar mahayin dadai bai hauni shi ba
Su kai kadda da Sale akan kadarko
Sai yace "Haba Sale bazan yadda kai ba"
Dadai suka wantsala hakan kan ya kwace
Ashe ba Sale ne a cikin ruwa ba?
Ya bishi ya bangaje ya buge yana ce
"Azo a gani idan ban yada kai ba"
Malam Sale saida ya tube riga
Yasa kaga Sale har bai sha ruwa ba
ya tashi ya hau tudu keke ya bi shi
Da rigar Sale keke bai sako ba
Su malam Sanda duk suka tar ma keke
Da ban magana yace ba zai saka ba
Ya ma rantse da jirgi har da mota
Ba zashi sako ba in ba'a sa wuka ba
Malam Sanda wai sun shirya da Keke
Wai yana kaunarsa ba domin tsiya ba
Yace "Haba malami kamarka
Bazan iya yadda babban malami ba"
Izan dai zaka hauni ka tara riga
Da wando ba ka hau ni hawan isa ba
Ya tashi hawa bai tattara ba
Ya fizgo malamin ba a jinjima ba
Ya yasai nan da nan a tsakar gidansa
Cikin matansa tun ba a kai dabe ba
Yace "Bari nai kure yashe ka malam
Dama ban kai ka bakin kasuwa ba
Bana son na yada mutum na kirki
Izan ba inda za ai dariya ba
Da motsa kararrawarka da kama burki
Ba zasu hana ni in jefar da kai ba
Yace masa "Bana kara hawanka keke"
Yace masa "ko adankiya ban kula ba"
Hawan da rashin hawan a gareni dai ne
Ban ga abinda zai cutar dani ba
Kamar tafiya ta sauri ko ta fizge
Baka je inda kaso nan da nan ba
Izan kazo ka hau ni ka bani iska
Na sha, ba inda ba zan je dakai ba
Ashe ba mai hawa keke ya more
Izan ba wanda ya iya zanzaro ba.
Da alherin da yai mana ba kadan ba
Muna murna da mulkin ingilishi
Zuwan da sukai kasarmu ba tai tsiya ba
Zama zamaninsu ne aka zo da Faifa
kudi ba masu nauyaya aljihu ba
Dada zarafinsu ne aka zo da jirgi
Kaje Makka ba da tashin Hankali ba
Sa'annan gasu Babur, ga su Mota
Da farko da can bamu san da su ba
Izan tafiya ta faru ka nemi mota
Izan jirgi ba kui daidai da shi ba
Izan kuwa babu Jirgi babu mota
Ka je da kafarka ba keken tsiya ba
Banni da Basukar Ho! Dan jidali
shakiyyi ba abin Babba ya hau ba
A Dan-Mahawayi nih Hau sai ya barni
Tudun-Yakaji ban kawo gari ba
Ya bar ni da jin jiki da zama a turba
Da dai ko juma'a ba a je dani ba
Kudi tirmis! Na bashi Sule-da-Sisi
keke bai mani rangwame ko dari ba
Na ce masa "Basukur rika sawwakewa"
Yace "Malam hala ba ka sanni ne ba"
"Ina da tsiya biyar farkonsu fanca
Na kau buga bindiga ba mai wuta ba"
In babbake zuciya, in tafi da sawu
Cikin daji kamar ba'a je dani ba
Muna tafiya kuma na fizge kaina
Mu fada kwazazzabo ni ban kula ba
Ina da ciki ana ce mai Kurumbo
Karambanin hawa baka saya ba
Hanjina kaca mai kama riga
In fizgo mai hawa ni ban kula ba
Tsiya na can mu je kan kadarko
Madaidaici in ce ba zamu hau ba
In hau bisa kafadar bari in zauna
Kamar mahayin dadai bai hauni shi ba
Su kai kadda da Sale akan kadarko
Sai yace "Haba Sale bazan yadda kai ba"
Dadai suka wantsala hakan kan ya kwace
Ashe ba Sale ne a cikin ruwa ba?
Ya bishi ya bangaje ya buge yana ce
"Azo a gani idan ban yada kai ba"
Malam Sale saida ya tube riga
Yasa kaga Sale har bai sha ruwa ba
ya tashi ya hau tudu keke ya bi shi
Da rigar Sale keke bai sako ba
Su malam Sanda duk suka tar ma keke
Da ban magana yace ba zai saka ba
Ya ma rantse da jirgi har da mota
Ba zashi sako ba in ba'a sa wuka ba
Malam Sanda wai sun shirya da Keke
Wai yana kaunarsa ba domin tsiya ba
Yace "Haba malami kamarka
Bazan iya yadda babban malami ba"
Izan dai zaka hauni ka tara riga
Da wando ba ka hau ni hawan isa ba
Ya tashi hawa bai tattara ba
Ya fizgo malamin ba a jinjima ba
Ya yasai nan da nan a tsakar gidansa
Cikin matansa tun ba a kai dabe ba
Yace "Bari nai kure yashe ka malam
Dama ban kai ka bakin kasuwa ba
Bana son na yada mutum na kirki
Izan ba inda za ai dariya ba
Da motsa kararrawarka da kama burki
Ba zasu hana ni in jefar da kai ba
Yace masa "Bana kara hawanka keke"
Yace masa "ko adankiya ban kula ba"
Hawan da rashin hawan a gareni dai ne
Ban ga abinda zai cutar dani ba
Kamar tafiya ta sauri ko ta fizge
Baka je inda kaso nan da nan ba
Izan kazo ka hau ni ka bani iska
Na sha, ba inda ba zan je dakai ba
Ashe ba mai hawa keke ya more
Izan ba wanda ya iya zanzaro ba.
Monday, March 26, 2007
Wakar Yabon Aikin Lebura; Lawan Maiturare
Fatara mai sa a lalace
Ta ki yarda ma kasan rance
Yinwa mai kai maza kwance
Ta kashe ba sai da aibi ba
Yau Lebura ne kamar Zakka
Aiki rani zuwa kaka
In gwamnati zata sa doka
Lebura baza su karya ba
Aiki kullum cikin taro
Ana abu sai kace horo
In dai Allah ake tsoro
Da lebura bai talauci ba
Bamu san haka zaku fara ba
Kuyi alkawari ku karya ba
Kaya ba za shi zango ba
Lebura bai bada iko ba
Jirgin sama fankamin wofi
Mota bata zuwa rafi
Ta nutsa ta haya ana tafi
Wannan bamu fara samu ba
A hake titi a sa kwalta
Mai mota yai gare keta
Wani Lebura bai da ko mota
Amma bazai ji ciwo ba
Da mun kare ace sauka
Ayi ma ham don a ruda ka
In ka ki gudu a take ka
Ko yau ba za'a canja ba
A dauki diga a wurgata
Kan tsandauri a sara ta
A tara kasa a kwashe ta
Mota ba zata huta ba
Wannan magana ku duba ta
Aiki kullum kamar bauta
In lebura su ake cuta
Allah sa baza su tabe ba
Kai gidan kwano kana yanga
Ai lebura in yasa targa
Kowa ya fito ya zazzaga
Ya dade bai hangi kwanon ba
Ga katako a jejjera
Shima kwanon a tattara
A bar ka dashi ace dora
Mun san ba zaka dora ba
Dubi tara gyada kamar Dala
Kauye da cikin Kano Jalla
A daura guda kamar hula
Amma ba zata goce ba
Kaji nauyin goro huhun nan
Daya ko daukar guda sannan
Ga wagunu fankamemen nan
Lebura ba za su kasa ba
shin Lebura ko waliyyi ne
Ko jikin da ice da karfe ne
Ko dan lada suke yi ne
Ba don karfen bature ba
Icen tunba a sare shi
Ai katako a tsage shi
Wane ne zasu tsage shi
Kan lebura baiyi aiki ba
Ai lebura sai a gode ma
A tara kudi a mika ma
In ba don kai ba tun da ma
Aiki ba zai yi kirki ba
Jirgi da muke gani babba
Ba za ya zuba ya dauka ba
in lebura baiyi lodi ba
Kaya ba za shi zango ba
Ran nan da na dauki mota ta
Muka je yashi ya kama ta
Da lebura sunki tura ta
Don ni ba zata motsa ba
Jirgin ruwa in yazo kwata
Da lebura za su sa keta
Suki yin aiki su kwankwanta
Shi ba zai je ya sauke ba
Tun sanda muke zuwa kanti
Da lebura dan dako Mati
Wani mummuna gwanin datti
Amma ba'a fishi aiki ba
Ai mai amalanke jigo ne
Babban kura ko gwamna ne
Mutum ko shi minista ne
Bazai iya raina lebo ba
In za'a daka asan gari
Daukar kaya ana zari
Kaga lebura har yana tari
Amma bai fasa aiki ba
Du lebura yan kasa ne ku
Ni banda nufin in raina ku
ku amince min cikin ranku
Da nufin ba zamu saba ba
Nan zamu tsaya mu saurara
In lebura su ake kwara
Zamani zai yi wo kora
kowa ba za ya tsere ba
Kai lebura me ya dame ka
Ga Lawan ya zo ya nuna ka
Da nufin a fahimci aikinka
Amma ba don a raina ba
Kullum aka samu mai sona
Zai wo sako zuwa guna
kulkul acikin Kano tona
Lungu nake ba a titi ba
Kowa ya karanta waka ta
Sha Takwas muka tsara baitinta
Don lebura mun ka tsara ta
Amma ba don minista ba
Ta ki yarda ma kasan rance
Yinwa mai kai maza kwance
Ta kashe ba sai da aibi ba
Yau Lebura ne kamar Zakka
Aiki rani zuwa kaka
In gwamnati zata sa doka
Lebura baza su karya ba
Aiki kullum cikin taro
Ana abu sai kace horo
In dai Allah ake tsoro
Da lebura bai talauci ba
Bamu san haka zaku fara ba
Kuyi alkawari ku karya ba
Kaya ba za shi zango ba
Lebura bai bada iko ba
Jirgin sama fankamin wofi
Mota bata zuwa rafi
Ta nutsa ta haya ana tafi
Wannan bamu fara samu ba
A hake titi a sa kwalta
Mai mota yai gare keta
Wani Lebura bai da ko mota
Amma bazai ji ciwo ba
Da mun kare ace sauka
Ayi ma ham don a ruda ka
In ka ki gudu a take ka
Ko yau ba za'a canja ba
A dauki diga a wurgata
Kan tsandauri a sara ta
A tara kasa a kwashe ta
Mota ba zata huta ba
Wannan magana ku duba ta
Aiki kullum kamar bauta
In lebura su ake cuta
Allah sa baza su tabe ba
Kai gidan kwano kana yanga
Ai lebura in yasa targa
Kowa ya fito ya zazzaga
Ya dade bai hangi kwanon ba
Ga katako a jejjera
Shima kwanon a tattara
A bar ka dashi ace dora
Mun san ba zaka dora ba
Dubi tara gyada kamar Dala
Kauye da cikin Kano Jalla
A daura guda kamar hula
Amma ba zata goce ba
Kaji nauyin goro huhun nan
Daya ko daukar guda sannan
Ga wagunu fankamemen nan
Lebura ba za su kasa ba
shin Lebura ko waliyyi ne
Ko jikin da ice da karfe ne
Ko dan lada suke yi ne
Ba don karfen bature ba
Icen tunba a sare shi
Ai katako a tsage shi
Wane ne zasu tsage shi
Kan lebura baiyi aiki ba
Ai lebura sai a gode ma
A tara kudi a mika ma
In ba don kai ba tun da ma
Aiki ba zai yi kirki ba
Jirgi da muke gani babba
Ba za ya zuba ya dauka ba
in lebura baiyi lodi ba
Kaya ba za shi zango ba
Ran nan da na dauki mota ta
Muka je yashi ya kama ta
Da lebura sunki tura ta
Don ni ba zata motsa ba
Jirgin ruwa in yazo kwata
Da lebura za su sa keta
Suki yin aiki su kwankwanta
Shi ba zai je ya sauke ba
Tun sanda muke zuwa kanti
Da lebura dan dako Mati
Wani mummuna gwanin datti
Amma ba'a fishi aiki ba
Ai mai amalanke jigo ne
Babban kura ko gwamna ne
Mutum ko shi minista ne
Bazai iya raina lebo ba
In za'a daka asan gari
Daukar kaya ana zari
Kaga lebura har yana tari
Amma bai fasa aiki ba
Du lebura yan kasa ne ku
Ni banda nufin in raina ku
ku amince min cikin ranku
Da nufin ba zamu saba ba
Nan zamu tsaya mu saurara
In lebura su ake kwara
Zamani zai yi wo kora
kowa ba za ya tsere ba
Kai lebura me ya dame ka
Ga Lawan ya zo ya nuna ka
Da nufin a fahimci aikinka
Amma ba don a raina ba
Kullum aka samu mai sona
Zai wo sako zuwa guna
kulkul acikin Kano tona
Lungu nake ba a titi ba
Kowa ya karanta waka ta
Sha Takwas muka tsara baitinta
Don lebura mun ka tsara ta
Amma ba don minista ba
Subscribe to:
Posts (Atom)