Barka da zuwa Turakar Sha'irai (Hausa Poets Blogspot). An bude wannan Turakar ranar 23 ga Maris 2007 domin yad'a rubutattun wak'ok'in mawak'an Hausa (amma Sha'iran Najeriya, domin ba mu da masaniya game da sha'iran Jamhuriyar Nijar). Muna bukatar ta'aliki da gyara a kan abubuwan da aka gani a wannan Turakar. Allah Ya ba mu sa'a, Amin.
Thursday, October 30, 2008
Wakar Madugu Yahaya; 18th Century
Ita dai wannan wakar wani marokine yayita, shi wannan mawaki da ake kira Yahaya, ba zama yake a gida yana waka ba. A zamanin da ake tafiya fatauci a kasar zuwa, zuwa kasashen ketare, shi sai ya bi ayari, inda duk aka sauka a zango, ya jawo kayan kidansa, yanawa madugai waka. Ba dai takamaiman lokacin da aka yi wannan waka, to amma wanio manazarci da ake kira M. B. Duffill, yayi hasashen cewa, an rubutatane a karshen karni na 18, ko kuma a farkon karni na 19. Ga mai neman cikakken bayani ga wannan waka, sai ya nemi kasidar da M. B. Dufill ya buga a mujallar SOAS, Vol 13, (1986).
Allah ya k aimu Hausa, ba don iya magana ba.
Madugu Yahaya shi bai iya magana ba .
In an tambaya, ya kan ce: Shiga! debi!
Shiga! debi! Borgu, ba zance ne ba.
Yanzu ga Waru zamne, ga washagari.
Ga waga banye, a ce: Shiga! debi!
Madugu Yahaya, shi bai iya tafiya ba.
Zangon azuhur shi kan ce masa hantsi .
Rana faduwa shi kan ce, la'asar ne.
Mai-baki da garatse ' ' kaman bakin gwando.
Kuma baki da garatse namij in yauni.
Ana tashi, ko ana yankan damna?
Miji da kurkunu, ga jak i da alafa .
Ga mata da guragu, '' kuma babu ruwan gora.
Ana yin salla Sayi, ko salon mussar wofi ?
Gurin salla Sayi aka dauke mini wando.
Malam Iyal yana gyaran sage, dada ya ga k irarra .
18 Wanga hannu da gargaza, wancan kuwa ga yauni.
19 Yana ciza gargaza, yana ciza yauni .
20 Yana cewa: Tudun nan muka jida , ko muna kai ga tudun can?
21 Sani dan Muhamman, baban gwani na Jega.
Thursday, May 31, 2007
Ya Ghiyathul Mustagithina; Daga Hayatu bin Sa'id
Hayatu bin Sa'id baya bukatar gabatarwa ga mutane, domin ga wanda yasan tarihin daular Fulani ta Sakkwato, yasan irin gwagwarmayar da aka sha da shi, da kuma yadda yayiwa Daular tawaye. Wanda, bayan hakan yayi mubayi'a ga Muhammad bin Abdullahi al Mahdi,na Sudan. Mahdi ya nada shi a matsayin halifansa a Daular Sakkwato, inda ya nemi Sarkin MUsulmi na wannan lokacin da yayi masa mubayi'a. Rashin samun nasarar hakan ce ta sanya ya koma ya hada kai da Rabih bin Salih (Rabeh). Inda daga baya suka samu sabani, ya dai rasu a wani karo da suka yi da Rabih. Ya rubuta wannan waka ce, a wani shagube da yayiwa yan'uwansa, a saboda irin mummunar fahimtar da suka yi masa.
Ga dai wakar;
1Ya Ghiyathul mustaghithina
2-na wa khairal nasirina
3Agaza ni kadda ka barni
4Ga dibarata ta kaini
5Yi dibara mai dibara
6Rahmanu ka jikaina
6Rabbu dubanni da rahma
7Anta khairil Rahimina
8Rahamakka sabiqata
9Jin kanka wabilina
10Babu mai yi sai da yin ka
11Wanga zance haka nan na
12Kai kayi ba taliki ba
13Taliki kau ajizina
14Rabbu kai ad dai Qadirun
16Jallah Sarki Qadirina
17Babu sarki daga Allah
18Shi fa Sarkin Gaskiyana
19Wanda yai sammai da kassai
20Wanda yayi dare da rana
21Wanda yai duniya da Barzakh
22Bata tsar mai ko ina na
23Wanda yai ran al-Qiyama
24Shi Azizi na gwanina
25Wanda yai wuta yayi al-Jan
26-na hakika Fatirina
27Agaza ni na kiraka
28Don Muhammadu yo i'ana
29Rabbu tsarshen daga kaidin
30Masu kaidi mufsidina
31Masu hasda da Adawa
32Da gamani kha'inina
33Sare kunci duk na makri
34Jallah Khairul makhirina
35Jallah kai ka tsadda Nuhu
36Shi da Hudu ga kafirina
37Jallah kai ka tsadda Ibra
38-him ga kaumun mu'tadina
39Kai fa kacce kana haqqun
40Fika nasarul muminina
41Don Muhammadu ya ilahil
42Arshi tsarshen makiyana
43Bani ikon shafe bid'a
44Bani ikon raya sunna
45Yo ijaba nai salati
46Ga Muhammadu dan Amina
47Hakaza Allai Sahabbai
48Duk jama'a tabi'ina
Ga dai wakar;
1Ya Ghiyathul mustaghithina
2-na wa khairal nasirina
3Agaza ni kadda ka barni
4Ga dibarata ta kaini
5Yi dibara mai dibara
6Rahmanu ka jikaina
6Rabbu dubanni da rahma
7Anta khairil Rahimina
8Rahamakka sabiqata
9Jin kanka wabilina
10Babu mai yi sai da yin ka
11Wanga zance haka nan na
12Kai kayi ba taliki ba
13Taliki kau ajizina
14Rabbu kai ad dai Qadirun
16Jallah Sarki Qadirina
17Babu sarki daga Allah
18Shi fa Sarkin Gaskiyana
19Wanda yai sammai da kassai
20Wanda yayi dare da rana
21Wanda yai duniya da Barzakh
22Bata tsar mai ko ina na
23Wanda yai ran al-Qiyama
24Shi Azizi na gwanina
25Wanda yai wuta yayi al-Jan
26-na hakika Fatirina
27Agaza ni na kiraka
28Don Muhammadu yo i'ana
29Rabbu tsarshen daga kaidin
30Masu kaidi mufsidina
31Masu hasda da Adawa
32Da gamani kha'inina
33Sare kunci duk na makri
34Jallah Khairul makhirina
35Jallah kai ka tsadda Nuhu
36Shi da Hudu ga kafirina
37Jallah kai ka tsadda Ibra
38-him ga kaumun mu'tadina
39Kai fa kacce kana haqqun
40Fika nasarul muminina
41Don Muhammadu ya ilahil
42Arshi tsarshen makiyana
43Bani ikon shafe bid'a
44Bani ikon raya sunna
45Yo ijaba nai salati
46Ga Muhammadu dan Amina
47Hakaza Allai Sahabbai
48Duk jama'a tabi'ina
Sunday, May 13, 2007
Wakar Gyaran Kano; Daga Dr Aliyu Aqilu 1975
Wannan waka an rubuta ta ne a 1975, ya kuma yi tane domin wani hangen nesa da yaga Kantomman Kano na weannan lokaci yayi, wato Dr Uba Adamu. A hirar da nayi da Dr Uba Adamu, a gidansa cikin watan April, ya bayyana mini cewa " Cikin 1974 ne suka yi tunanin, kawo gyara a tsarin zamantakewar birnin Kano. A saboda haka suka kawo wani tsari, wanda hakan ya haifar da gina manyan tituna a Birnin Kano, da yin Kwalbatoci, da kuma wajejen zuba shara. A wannan lokacin ne akayi Manyan titunan da ake amfani dasu har yanzu a birnin Kano. Aka kuma yi musu Kwalbatoci a gefunansu, da kuma wajejen zuba shara". A saboda jin dadin wannan aiki ne, ya sanya Dr Aliyu Aqilu ya yi wannan waka. Ga dai wakar
Zan je ziyarar shugaba
Dattijo Kantoma Uba.
Bazan shiru na kawai ta ba
In ba da na ce Rabbu ba.
Sarki guda daya wahidi
Bazan takaita kiransa ba.
Bayan fadar Allah da gai da
Manzo Muhammadu Mujtaba.
Me zai biyo bayan su ne
Na abin nufi da yake gaba.
Haka ne akwai wani dan batu
Da ba zan ki tunkarar sa ba.
Ga dai bayani dan kadan
A takaice ba dungunsa ba.
Niyar ziyara ce dani
Zancenta yau zan bayyana.
Mai tambaya ya so yaji
Domin ya amfana gaba.
Manufar ziyarar wacce nai
Maganarta tun farko gaba.
Ya zuwa ina wai zani kai
Mai tambaya bai aibu ba.
Zan bayyana masa ne ya ji
Bazan yi kwauro gun sa ba.
Zan dau ziyara ne ni kai
Ta kano gari ba kauye ba.
Wajen masoyina abin
kamna sahihin Shugaba.
Shine Muhammadu Adamu
Kantoma mai lakabi Uba.
Dattijo din nan adali
Mai tausayin jama'a Uba.
Bangon tama ki faduwa
Sha kabra garnakaki Uba.
Matsayinka din nan kai can
Canta da shi malam Uba.
Illimi zalaka ke gare
ka da kwarjini na kwarai Uba.
Ga hattara ga hankali
Kantoma ga hangen gaba.
Illimin makamar zamani
Da sanin sharia tun gaba.
Ka san su ka kuma dandake
Ba yau kawai ka tsire suba.
Birnin Kano da wajenta duk
Ta samu babban cigaba.
A wajen nizafa in ka du
Ba kauyuka ba a bar suba.
Balle cikin birnin fa
Ba wai bane ba inke ba.
Kwatami cakal yau babu shi
Shara butsa bamu ganta ba.
Sarari a hanya ya dadu
Albarkacin himmar Uba.
Duk tarkace an kauda su
Daga ko ina ba a bar shi ba.
Sababi da wane mun ka sami
wannan gimgimemen cigaba.
Mun samu kakkaifan mutum
Mai kokari ba kasa ba.
Gwarzon maza namijin tsaye
Inuwa ba a bisne ki ba.
Kantoma Muhammadu Adamu
Dattijo mai lakabi Uba.
Bompai da Rimin Dada sun
Maka godiya malam Uba.
Sabon gari da Tudun wada
Sun gode mai daraja Uba.
Tarauni su da Giginyu sun
Yi yabo ga mai daraja Uba.
Gandu Sharada da Dorayi
Da Salanta., Calawa gaba.
Jama’ar da ke Fanshekara
Duk sun yi san barka Uba.
Waika da Jajira, Gobira
Wa, sun yi godiya malam Uba.
Kurna, Fagged da Gwagwarwa
sun maka godiya malam Uba.
Na sauka Fanisau mutan
Gama sun game da yabon Uba.
Ungogo, Kunya suna fadar
Madalla-madalla Uba.
Wannan Sadauki adali
Dattijo bai yashe mu ba.
Kub! Dai yawa kuwa lara bugu
Daya ta mace bata tashi ba.
Ya watsa rundunar
Sauro a yau bamu ji shi ba.
Bana nufin guda da dai
Ban daura niyyar yinta ba.
Amma dalili ya saka, ni
Na yi ta ban shiryeta ba.
Domin saboda farin ciki
Dadin zamanmu da kai Uba.
Zai sa ni Kwalla yar kadan
Watakil bakwa zarge niba.
Sirri na kokon zuciya
Fuska bata rasa jin sa ba.
Yururui! A yau na randama
Kodai da ban sabeta.
Amma akwai Magana daban
Da ba zan iya ban yi taba.
Domin ta nai mini kaikayi
Na zo ka sosa wajen Uba.
Najasa da ke yi barkatai
Haka nan butsa! An zuzzuba.
Ba kariya ko yar kadan
Daga baya har ya zuwa gaba.
Ka ga sangamemen saurayi
Bama su yara kanana ba.
Ya yaye al’aura a fi
Li bada jin kunyarsa ba.
Wannan abin bisa gaskiya
Ban samu jin dadinsa ba.
Domin akwai ill agama
Baki ba za su yabe mu ba
Harma sukan zarge mu ne
Ba wai bane, ba inke ba.
Ni naji sanda suke fade
Kuma na gwada na jarraba.
Kasan ni kan fita ne waje
Zancenga ban kage shi ba.
Wannan ta ja mini damuwa
Na tafo ka maganta Uba.
Ai ya kamata ka tsawata
Kuma kar a kara nan gaba.
Nasan ka baka rurumi
Kuma baka lalaci Uba.
Me maida kai kake mai kula
Ga abinda duk ka saka gaba.
Tsuguna da tashi ba’a yin ta
A ofishin malam Uba.
Baka shiri da munafuki
Cece-kuce baka ji shi ba.
Kowa shigo da maganganu
Mara sa shiri a gaban Uba.
Kudarsa zai kuwa dandana
Dadin karon bai ji shi ba.
Su kwaramniya da rigingimu
Da hayaniya an zuzzuba.
Duk dai a karata dole ne
Ayi gaskiya a gaban Uba.
Domin kurum shi kayi shi ji
Kowa abinda ya rattaba.
Suna daban yau zan fada
A gareka yau malam Uba.
Kere kana fasa kan maki
Bin gaskiya baka san shi ba.
In kun tuna nace da ku
Guda bana rika yin ta ba.
Amma fa har haka dan ku ji
Dadi bazai inganta ba.
In banda an ware shi an
Yafa shi an more shi ba.
Kash! Nan wajen zan dakata
In sa alama sai gaba.
Ni ne Aqilu Aliyu na
Gaisheka mai daraja Uba.
Kantoma huta lafiya
Sai lokaci wani nan gaba.
In Rabbana ya kaddara
Mana saduwa ban mata ba.
Bana yawaita maganganu
Sai addu’a zan kattaba.
Ya Rabbi ya Sarki Gwani
Allah ka ja zamanin Uba.
Amin saboda abin biya
Da yabo Muhammadu Mujtaba.
Tamat bi AunilLahi mun
Bidi taimako nasa tun gaba.>
Zan je ziyarar shugaba
Dattijo Kantoma Uba.
Bazan shiru na kawai ta ba
In ba da na ce Rabbu ba.
Sarki guda daya wahidi
Bazan takaita kiransa ba.
Bayan fadar Allah da gai da
Manzo Muhammadu Mujtaba.
Me zai biyo bayan su ne
Na abin nufi da yake gaba.
Haka ne akwai wani dan batu
Da ba zan ki tunkarar sa ba.
Ga dai bayani dan kadan
A takaice ba dungunsa ba.
Niyar ziyara ce dani
Zancenta yau zan bayyana.
Mai tambaya ya so yaji
Domin ya amfana gaba.
Manufar ziyarar wacce nai
Maganarta tun farko gaba.
Ya zuwa ina wai zani kai
Mai tambaya bai aibu ba.
Zan bayyana masa ne ya ji
Bazan yi kwauro gun sa ba.
Zan dau ziyara ne ni kai
Ta kano gari ba kauye ba.
Wajen masoyina abin
kamna sahihin Shugaba.
Shine Muhammadu Adamu
Kantoma mai lakabi Uba.
Dattijo din nan adali
Mai tausayin jama'a Uba.
Bangon tama ki faduwa
Sha kabra garnakaki Uba.
Matsayinka din nan kai can
Canta da shi malam Uba.
Illimi zalaka ke gare
ka da kwarjini na kwarai Uba.
Ga hattara ga hankali
Kantoma ga hangen gaba.
Illimin makamar zamani
Da sanin sharia tun gaba.
Ka san su ka kuma dandake
Ba yau kawai ka tsire suba.
Birnin Kano da wajenta duk
Ta samu babban cigaba.
A wajen nizafa in ka du
Ba kauyuka ba a bar suba.
Balle cikin birnin fa
Ba wai bane ba inke ba.
Kwatami cakal yau babu shi
Shara butsa bamu ganta ba.
Sarari a hanya ya dadu
Albarkacin himmar Uba.
Duk tarkace an kauda su
Daga ko ina ba a bar shi ba.
Sababi da wane mun ka sami
wannan gimgimemen cigaba.
Mun samu kakkaifan mutum
Mai kokari ba kasa ba.
Gwarzon maza namijin tsaye
Inuwa ba a bisne ki ba.
Kantoma Muhammadu Adamu
Dattijo mai lakabi Uba.
Bompai da Rimin Dada sun
Maka godiya malam Uba.
Sabon gari da Tudun wada
Sun gode mai daraja Uba.
Tarauni su da Giginyu sun
Yi yabo ga mai daraja Uba.
Gandu Sharada da Dorayi
Da Salanta., Calawa gaba.
Jama’ar da ke Fanshekara
Duk sun yi san barka Uba.
Waika da Jajira, Gobira
Wa, sun yi godiya malam Uba.
Kurna, Fagged da Gwagwarwa
sun maka godiya malam Uba.
Na sauka Fanisau mutan
Gama sun game da yabon Uba.
Ungogo, Kunya suna fadar
Madalla-madalla Uba.
Wannan Sadauki adali
Dattijo bai yashe mu ba.
Kub! Dai yawa kuwa lara bugu
Daya ta mace bata tashi ba.
Ya watsa rundunar
Sauro a yau bamu ji shi ba.
Bana nufin guda da dai
Ban daura niyyar yinta ba.
Amma dalili ya saka, ni
Na yi ta ban shiryeta ba.
Domin saboda farin ciki
Dadin zamanmu da kai Uba.
Zai sa ni Kwalla yar kadan
Watakil bakwa zarge niba.
Sirri na kokon zuciya
Fuska bata rasa jin sa ba.
Yururui! A yau na randama
Kodai da ban sabeta.
Amma akwai Magana daban
Da ba zan iya ban yi taba.
Domin ta nai mini kaikayi
Na zo ka sosa wajen Uba.
Najasa da ke yi barkatai
Haka nan butsa! An zuzzuba.
Ba kariya ko yar kadan
Daga baya har ya zuwa gaba.
Ka ga sangamemen saurayi
Bama su yara kanana ba.
Ya yaye al’aura a fi
Li bada jin kunyarsa ba.
Wannan abin bisa gaskiya
Ban samu jin dadinsa ba.
Domin akwai ill agama
Baki ba za su yabe mu ba
Harma sukan zarge mu ne
Ba wai bane, ba inke ba.
Ni naji sanda suke fade
Kuma na gwada na jarraba.
Kasan ni kan fita ne waje
Zancenga ban kage shi ba.
Wannan ta ja mini damuwa
Na tafo ka maganta Uba.
Ai ya kamata ka tsawata
Kuma kar a kara nan gaba.
Nasan ka baka rurumi
Kuma baka lalaci Uba.
Me maida kai kake mai kula
Ga abinda duk ka saka gaba.
Tsuguna da tashi ba’a yin ta
A ofishin malam Uba.
Baka shiri da munafuki
Cece-kuce baka ji shi ba.
Kowa shigo da maganganu
Mara sa shiri a gaban Uba.
Kudarsa zai kuwa dandana
Dadin karon bai ji shi ba.
Su kwaramniya da rigingimu
Da hayaniya an zuzzuba.
Duk dai a karata dole ne
Ayi gaskiya a gaban Uba.
Domin kurum shi kayi shi ji
Kowa abinda ya rattaba.
Suna daban yau zan fada
A gareka yau malam Uba.
Kere kana fasa kan maki
Bin gaskiya baka san shi ba.
In kun tuna nace da ku
Guda bana rika yin ta ba.
Amma fa har haka dan ku ji
Dadi bazai inganta ba.
In banda an ware shi an
Yafa shi an more shi ba.
Kash! Nan wajen zan dakata
In sa alama sai gaba.
Ni ne Aqilu Aliyu na
Gaisheka mai daraja Uba.
Kantoma huta lafiya
Sai lokaci wani nan gaba.
In Rabbana ya kaddara
Mana saduwa ban mata ba.
Bana yawaita maganganu
Sai addu’a zan kattaba.
Ya Rabbi ya Sarki Gwani
Allah ka ja zamanin Uba.
Amin saboda abin biya
Da yabo Muhammadu Mujtaba.
Tamat bi AunilLahi mun
Bidi taimako nasa tun gaba.>
Saturday, May 12, 2007
Wakar da ake Sanin Halin mata da ita; Muhammad Dangani Katsina
Wannan waka dai ta shahara a kafafen watsa labarai na Kano da Kaduna,domin akan watsa ta a shirye-shirye da dama.Ga dai wakar.
Bismillahir Rahmanir Rahim
Wasallallahu ala Nabiyul Karim
To bismiLlah Allah Sarki
Mai abu mai komai mai kyauta
Bani zalaka, bani fasaha
Inyi bayani na, a fahimta
Zanyi bayani halin mata
Zani rubuta, don a karanta
Kasan mata sun kasu ukku
Zo kusa in na fada ka rubuta
Akwai mata mai tsoron Allah
Bata nufin kowa da mugunta
Akwai wata ga barna ga gyara
Gata da saukin kai ga cuta
Sai ta ukunsu gadangama kenan
Bata nufin gyara sai cuta
Bata nufin hairi ga mijinta
Baga kiyoshi,ba ga makwabta
Bata nufin gyara sai barna
Sai duk safe ta cuci mijinta
Ya tafi office kokuma kanti
Bata kara zama dakinta
In mai noma ne ko zage
Ya tafi gona, zaure za ta
Tana nema taga masu wucewa
Wai ita dai suga kyan fuskarta
In taga sunki shiga harkarta
Sai kaji tace zata makwabta
Kaji irin halayen mata
Munana,manyan, makwadaita
In mace bata da kunya barta
Kama da miya,in ba gishirinta
In mace bata raga maka barta
Daina nufinta kabar sha'awarta
In mace ta zama bata ragama
Ko ka sota, kana kuma kinta
In mace, shashanci ya gameta
Ba mai kara ganin kirkinta
Bata nufin Allah da Ma'aiki
Sai bidi'a ita ke ka gunta
Taji ana Biko tai mika
Sai kaji tace Biko zata
Ba dangin iya babu na Baba
Ko kace ta bari, can zata
Wannan mace,ba mace ce ba
Dai na nufinta kabar sha'awarta
Natsuwa itace mace,ko yar wace
In kaga ba natsuwa,ka bajeta
Kasan mata sun iya karya
Sun iya yadda suke shirgata
Ba duk mace ke son addini ba
Nufinsu a basu kudi, su bukata
Matar da ta zam bata san Allah ba
Ba ta kara zama dakinta
Sai ta fito a tashar Takatale
Sai tai batsa gaban kanwarta
In kace mata, wance ki lura
Baka hana ni bugun cinyata
Babu ruwanta da kunya faufau
Ga Ashar, ko ciwake yana kunyarta
Sanarwata itace ga mazaje
Kar a yawaita kwadai, a takaita
Aure ba abu ne ba na wasa
Bar neman kyau, nemi nagarta
Ni nasan mace, komi kyaunta
Indai babu hali da nagarta
Kana sha'awarta, kana kuma sonta
Badan Allah ba kana kyale ta
Don haka, tun farko ka tsaya tsaf!
Kai nazari da irin halinta
In mace ta zama, shagiri girbau
Ko ka aureta, baka iyata.
Kun ji mazaje, kar ku kiya man
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai mata na nan su shidda
Zo kusa inna fada ka jimilta
Akwai dibgau! Mai dibge mijinta
Ba ta jira ga fada shi taya ta
Danbago, mai zurfin tumbi
Ba ta takowa sai ta cikinta
Sai shirwa ita dai tayi fige
Kan ta shigo daki sai ta sata
Ratata, sarkin magana ce
Tun daga nesa, kana jin kanta
In maganar mace tayi yawa, kaji
Tun daga nesa, kana jin kanta
Wannan mata, tayi hasara
Sai a nada mata sarki wauta
Sai Malali, ita dai tayi kwance
Ta ki ta tashi, ta nemi na kanta
Ba ta kadi, kuma bata sanaá
Sai na mijinta, ya bata, ta sata
Sai ta cikon shida, mai mulkin kai
Ba mai sa ta, bare shi hana ta
Aure ne, ni nis sa kaina
In ka matsa mani, in tafiyata
To shida ta cika ban kara ba
Akwai saura, amma na takaita
Akwai saura, amma na kaita
Ka shaida akwai mata masu kazanta
In mace ta zam bata da tsafta
wannan kam, ta cuci mijinta
Yin tsafta, ta jiki da tufafi
Shine ke hana yadon cuta
Wadda ta zam, bata wanke tufa ba
Shike shaida, anga kazanta
Zani tuna muku in kun manta
Kashedi, da mata masu kazanta
Sun gaza wanke tufa da tukwane
Sun ki kula da abinci su kyauta
Ta gaza share cikin dakinta
Balle na mijinta, bale fuskatta
Kun ji isharata ku kiyaye
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai barna ga mazaje
Zamu fada musu, don su raga ta
Wadansu maza dauka da ajewa
Sun dauko mace, sai su aje ta
Ba laifin tsaye, babu na zaune
Sai kaga basu zuwa dakinta
Ran aikinta ba zai fara'a ba
Ko magana tai, bashi kulawa
Duk namijin da ya dau kwanan wata
In ya hana mata, don bai son ta
Yaki bsatun Allah da maáiki
ya kashe kansa, saboda mugunta
Mata gunku amanar Allah ce
Don Allah maza ku rike ta
In mace tai maka laifi daure
Sai ka tuna, ai kai ka aje ta
Su mata halinsu mugunta
Sai dai-dai ke, basu da keta
Macce, mijinta ko sarki ne
bata yaba masa, sai in bata
Macce mijinta ko malam ne
Bata yabonsa tace da nagarta
Tana iya cewa miji mataulaci
Koda yayi kudin Dantata
Su ka bugu su riga kai kara
Ba ai magana ba su je su tsirata
In mace ta shirya maka karya
Ko boka kam, bashi iyata
Macce tana shiryawa mijinta
Karya, don ya bari tayi cuta
Tâce mashi zata gidan kanwarta
Ko kuma zata ta gaida uwaye
Ta fita, ta samu ta sulale
Ta shiga yawo santa-santa
Ba ta gidan iya, bata na Baba
Kaji nufinta ta sheke ayarta
Don haka mata, ba'a iya musu
In kaji sun magana ka aje ta
Kowace mata na da halinta
Wadansu da kyau, wasu ko da mugunta
Wata in suka fara fada da mijinta
Sai ta rike shi, tace ya kasheta
In kuma yaki ta kama tufarsa
Ace ta sake shi, tace ya kasheta
Ko kuma yanzu ka bani takarda
In kuma ka ban in ketata
In kuma kace anshi takardar
Sai kaji tace, bani riketa
Ita dai sababi ta ka so ta aza mai
Indai yace bashi sakinta
In ka hada ta da Allah sannan
Tafi matsa maka don tsiwarta
Kai kuma gaka kana jin kunya
Ga shari'a ka zage ka kasheta
Don haka sai kowa yayi sannu
Ya nemi hali mai kyau da nagarta
Ba'a sayan mota don kyanta
Sai kaya, da gudu, da nagarta
To haka ne mace, komi kyaunta.
Indai babu hali da nagarta
Kamar mota take komi kyaunta
Indai ba tafiya, bari sonta
Kyan ladabin mace tai wa mijinta
In taki ya mishi, ta kashe kanta
Kui ladabi mata ku kiyaye
aure ba'a gama shi da bauta
In mace tai ladabi ta kiyaye
Allah sarki, shi ka biyanta
Ku mata ku jiya, ku kiyaye
In kuma kun ki, kui mahukunta
Ran mutuwa, da gamo, da kasawa
Sai a tuna maka, in ka mance
In mace tabi mijinta da gaske
Tayi hakuri ta tsaya dakinta
Bata ganin wani banda mijinta
Allah zai mata, babbar kyauta
Miji babban abune bi mjinki
Dai na ganin waccan da mijinta
Bishi, ki so shi, ki bar raina shi
Ko shine sarkin matalauta
Don ki sani Allah ya aza mai
Shi aza masi, shi zai kyauta
Shi abu duk aikin Allah ne
Allah shike bada wadata
Ya kasa bayi fanni-fanni
Shi yai ma'azurta, yai matalauta
In niyyarki gudun matalauta
Sai ya so sannan ki wadata
Shi Allah ba ai masa wayo
Yanda yaso, haka za shi hukunta
Ki hakuri ki tsaya ga mijinki
In ya wadatu, sai ki wadata
Ya Allahu muna rokonka,
ya Allah ka bamu wadata
Ka bamu abinci ckin suturarmú
Allah kadda ka nufe mu da sata
Duk makiyanmu aza mu akansu
Duk sharrin da su kai da mugunta
Ka daukaka addini bisa komai
Ya Allahu bidia ka kashe ta
Kai tsira ga Muhammadu Ahmadu
Don dakin makka, don siffatai
Sahabi nabiyu, da ahlil baiti
Ahlil abaí kaza makusanta
Bismillahir Rahmanir Rahim
Wasallallahu ala Nabiyul Karim
To bismiLlah Allah Sarki
Mai abu mai komai mai kyauta
Bani zalaka, bani fasaha
Inyi bayani na, a fahimta
Zanyi bayani halin mata
Zani rubuta, don a karanta
Kasan mata sun kasu ukku
Zo kusa in na fada ka rubuta
Akwai mata mai tsoron Allah
Bata nufin kowa da mugunta
Akwai wata ga barna ga gyara
Gata da saukin kai ga cuta
Sai ta ukunsu gadangama kenan
Bata nufin gyara sai cuta
Bata nufin hairi ga mijinta
Baga kiyoshi,ba ga makwabta
Bata nufin gyara sai barna
Sai duk safe ta cuci mijinta
Ya tafi office kokuma kanti
Bata kara zama dakinta
In mai noma ne ko zage
Ya tafi gona, zaure za ta
Tana nema taga masu wucewa
Wai ita dai suga kyan fuskarta
In taga sunki shiga harkarta
Sai kaji tace zata makwabta
Kaji irin halayen mata
Munana,manyan, makwadaita
In mace bata da kunya barta
Kama da miya,in ba gishirinta
In mace bata raga maka barta
Daina nufinta kabar sha'awarta
In mace ta zama bata ragama
Ko ka sota, kana kuma kinta
In mace, shashanci ya gameta
Ba mai kara ganin kirkinta
Bata nufin Allah da Ma'aiki
Sai bidi'a ita ke ka gunta
Taji ana Biko tai mika
Sai kaji tace Biko zata
Ba dangin iya babu na Baba
Ko kace ta bari, can zata
Wannan mace,ba mace ce ba
Dai na nufinta kabar sha'awarta
Natsuwa itace mace,ko yar wace
In kaga ba natsuwa,ka bajeta
Kasan mata sun iya karya
Sun iya yadda suke shirgata
Ba duk mace ke son addini ba
Nufinsu a basu kudi, su bukata
Matar da ta zam bata san Allah ba
Ba ta kara zama dakinta
Sai ta fito a tashar Takatale
Sai tai batsa gaban kanwarta
In kace mata, wance ki lura
Baka hana ni bugun cinyata
Babu ruwanta da kunya faufau
Ga Ashar, ko ciwake yana kunyarta
Sanarwata itace ga mazaje
Kar a yawaita kwadai, a takaita
Aure ba abu ne ba na wasa
Bar neman kyau, nemi nagarta
Ni nasan mace, komi kyaunta
Indai babu hali da nagarta
Kana sha'awarta, kana kuma sonta
Badan Allah ba kana kyale ta
Don haka, tun farko ka tsaya tsaf!
Kai nazari da irin halinta
In mace ta zama, shagiri girbau
Ko ka aureta, baka iyata.
Kun ji mazaje, kar ku kiya man
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai mata na nan su shidda
Zo kusa inna fada ka jimilta
Akwai dibgau! Mai dibge mijinta
Ba ta jira ga fada shi taya ta
Danbago, mai zurfin tumbi
Ba ta takowa sai ta cikinta
Sai shirwa ita dai tayi fige
Kan ta shigo daki sai ta sata
Ratata, sarkin magana ce
Tun daga nesa, kana jin kanta
In maganar mace tayi yawa, kaji
Tun daga nesa, kana jin kanta
Wannan mata, tayi hasara
Sai a nada mata sarki wauta
Sai Malali, ita dai tayi kwance
Ta ki ta tashi, ta nemi na kanta
Ba ta kadi, kuma bata sanaá
Sai na mijinta, ya bata, ta sata
Sai ta cikon shida, mai mulkin kai
Ba mai sa ta, bare shi hana ta
Aure ne, ni nis sa kaina
In ka matsa mani, in tafiyata
To shida ta cika ban kara ba
Akwai saura, amma na takaita
Akwai saura, amma na kaita
Ka shaida akwai mata masu kazanta
In mace ta zam bata da tsafta
wannan kam, ta cuci mijinta
Yin tsafta, ta jiki da tufafi
Shine ke hana yadon cuta
Wadda ta zam, bata wanke tufa ba
Shike shaida, anga kazanta
Zani tuna muku in kun manta
Kashedi, da mata masu kazanta
Sun gaza wanke tufa da tukwane
Sun ki kula da abinci su kyauta
Ta gaza share cikin dakinta
Balle na mijinta, bale fuskatta
Kun ji isharata ku kiyaye
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai barna ga mazaje
Zamu fada musu, don su raga ta
Wadansu maza dauka da ajewa
Sun dauko mace, sai su aje ta
Ba laifin tsaye, babu na zaune
Sai kaga basu zuwa dakinta
Ran aikinta ba zai fara'a ba
Ko magana tai, bashi kulawa
Duk namijin da ya dau kwanan wata
In ya hana mata, don bai son ta
Yaki bsatun Allah da maáiki
ya kashe kansa, saboda mugunta
Mata gunku amanar Allah ce
Don Allah maza ku rike ta
In mace tai maka laifi daure
Sai ka tuna, ai kai ka aje ta
Su mata halinsu mugunta
Sai dai-dai ke, basu da keta
Macce, mijinta ko sarki ne
bata yaba masa, sai in bata
Macce mijinta ko malam ne
Bata yabonsa tace da nagarta
Tana iya cewa miji mataulaci
Koda yayi kudin Dantata
Su ka bugu su riga kai kara
Ba ai magana ba su je su tsirata
In mace ta shirya maka karya
Ko boka kam, bashi iyata
Macce tana shiryawa mijinta
Karya, don ya bari tayi cuta
Tâce mashi zata gidan kanwarta
Ko kuma zata ta gaida uwaye
Ta fita, ta samu ta sulale
Ta shiga yawo santa-santa
Ba ta gidan iya, bata na Baba
Kaji nufinta ta sheke ayarta
Don haka mata, ba'a iya musu
In kaji sun magana ka aje ta
Kowace mata na da halinta
Wadansu da kyau, wasu ko da mugunta
Wata in suka fara fada da mijinta
Sai ta rike shi, tace ya kasheta
In kuma yaki ta kama tufarsa
Ace ta sake shi, tace ya kasheta
Ko kuma yanzu ka bani takarda
In kuma ka ban in ketata
In kuma kace anshi takardar
Sai kaji tace, bani riketa
Ita dai sababi ta ka so ta aza mai
Indai yace bashi sakinta
In ka hada ta da Allah sannan
Tafi matsa maka don tsiwarta
Kai kuma gaka kana jin kunya
Ga shari'a ka zage ka kasheta
Don haka sai kowa yayi sannu
Ya nemi hali mai kyau da nagarta
Ba'a sayan mota don kyanta
Sai kaya, da gudu, da nagarta
To haka ne mace, komi kyaunta.
Indai babu hali da nagarta
Kamar mota take komi kyaunta
Indai ba tafiya, bari sonta
Kyan ladabin mace tai wa mijinta
In taki ya mishi, ta kashe kanta
Kui ladabi mata ku kiyaye
aure ba'a gama shi da bauta
In mace tai ladabi ta kiyaye
Allah sarki, shi ka biyanta
Ku mata ku jiya, ku kiyaye
In kuma kun ki, kui mahukunta
Ran mutuwa, da gamo, da kasawa
Sai a tuna maka, in ka mance
In mace tabi mijinta da gaske
Tayi hakuri ta tsaya dakinta
Bata ganin wani banda mijinta
Allah zai mata, babbar kyauta
Miji babban abune bi mjinki
Dai na ganin waccan da mijinta
Bishi, ki so shi, ki bar raina shi
Ko shine sarkin matalauta
Don ki sani Allah ya aza mai
Shi aza masi, shi zai kyauta
Shi abu duk aikin Allah ne
Allah shike bada wadata
Ya kasa bayi fanni-fanni
Shi yai ma'azurta, yai matalauta
In niyyarki gudun matalauta
Sai ya so sannan ki wadata
Shi Allah ba ai masa wayo
Yanda yaso, haka za shi hukunta
Ki hakuri ki tsaya ga mijinki
In ya wadatu, sai ki wadata
Ya Allahu muna rokonka,
ya Allah ka bamu wadata
Ka bamu abinci ckin suturarmú
Allah kadda ka nufe mu da sata
Duk makiyanmu aza mu akansu
Duk sharrin da su kai da mugunta
Ka daukaka addini bisa komai
Ya Allahu bidia ka kashe ta
Kai tsira ga Muhammadu Ahmadu
Don dakin makka, don siffatai
Sahabi nabiyu, da ahlil baiti
Ahlil abaí kaza makusanta
Wednesday, April 18, 2007
MAIGANJI; Daga Malam Muhammadu Namaiganji
Ba dai wani takamaimiyar magana, akan kowanene Malam Muhammadu Na Maiganji, ba kuma tabbacin lokacin da ya rubutata. Amma insha Allah, zan kawo cikakken bayani a gameda wakar ta Maiganji. A yanzu dai ga wakar Maiganji
Bi Bismillah ni bawa, na far yabo ga mai baiwa
Arrahmani baiwarsa, gamamma ce ga dan kowa
Rahmani ya kebe baiwarsa, baya yiwa majusawa
Allahu yai dadin tsira, ga Ahmadu shugaban kowa
Baicin ambaton Allah, nufina gargadin kowa
2]Wanda ya yada addini, baya tambayar kowa
Girman kai ya debe shi, ya sashi ya fandare wawa
Yaku yan uwa dangi, Allah ya halicce mu
Domin tsaida addini, Tawhidi kaza Sallah
Musan Azumi da Zakkarmu, kaza Hajji wajibin kowa
3]Mu sansu, mu sanda yayanmu, kaza matanmu bayinmu
Kanko mun ki sanasshe su, ranar lahira ka sani
Acan aka tambayar kowa, akan doran siradinsa
Ga kaifi, ga makonansa, Kama nan za'a tsaishe ka
Idan yazo dasu ya shige, idan bai zo da kome ba
Wa'ila sai su turo shi, cikin zurfin wuta wawa
4]Bayi na ciki su cane, ya kaitonka kai bawa
Ina halinku ma'aikinku, ya kance 'sun isar da sani'
Iyaye sun ka bashe mu, suna aikin majusawa
Kan ance da su su bari, su kance 'mu iyayenmu
Mun same su sun aika, abinda su kanyi shi zamu bi, bama jin fadar kowa
5]Ka duba can ga kakanku, , Adamu, Nuhu, Idrisu
Da Ibrahim uban kowa, Manyan Annabawa ne
Sun bi fada ta Allahu, tazo har kan ma'aikinmu
Kowak ki ta ya ratse, yabi fadar Yahudawa
6]Yahudu, Nasara sun ratse, shaidani ya rude su
Yace ku tsaya a nushe ku, ga aikin iyayenkuAbin bautarsu su gunki, gama shine mashasharku
Kar ku bi annabin kowaYa jama'a ta addini, bin Allah farillansa
Bin manzo cikin sunna, wanda ya yada bin sunna
Kamar bai aika komai ba, kamar dai wanda yai sallah
Bai zakka ba ya tabe, cikin bin Jallah mai baiwa
7]Wanda ya bauta Allahu, yana sabon iyayensa
Bai karba ba sarkinmu, ka tuba ka bisu kai wawa
Ya mai bauta Allahu, nemi halas abar cinka
Kan ko tabe, haramun wanda ya cita
Misalin gwargwadon lauma
Kwana Arba'in za ai, yana bauta ga sarkinmu
Bai karba Allahu, Jallah ubangijin kowa
8]Ina Malam, Ina Malam Malam tsorci Allahu
Kabar tsoron mutanenka, fada musu gaskiya hakkan
Kan sun bita ka huta, kan sun ki ta ka kubuta
Wurin Sarkinmu Allahu, Jallah Karimu mai baiwa
9]Zan muku gargadi dangi
Ku kai yayanku gun malam
Karatu wajibin kowa
10]Wanda ya samu da nasa, Yaki ya kai shi gun malam
Ya dau alhakin dan sa, Yahudu, Nasara sun samu
Kaza suma majusawa, Kowanne da
Ka haifeshi, duk jama'ar Ma'aikine
Sai babansa yaki shi, yakan koma Nasarawa
11]Malam nemi sarkinka, kace masa yai fadan bidi'a
Bidi'a kishiyar Sunna, kowab bita y rates
Yabi fada ta shaidani, yaki fadar ma'aikinmu
Muhammadu Annabin kowa, wanda yabar fadar MammanYana nushe shi kan turba, Yana kimso cikin jeji, yana yawo kamar giwa
12]Mai yawo cikin jeji, kan yaje cikin jama'a
Mazaje masu bin Allah, suna taro gidan malam
Ko jam'a ta yin sallah, baka ga shi baya sheka yana cigiyar, bata wawa
Koda nace, da ko daji, ba daji na kura ba
13]Ko acikin gidnsa yake, yaki yaje gidan malam
Shi san Allah, bazai Sallah, kace masa
Mai shiga jeji, zaya bace cikin njeji, Babu gudunmawar kowa
Maza mata ku nemi, fada tasa shugaban kowa
14]Wanda ya bar fadar Mamman, yaki fada ta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, Wanda yabar fadar Allahu
Ya kafirta ya watse, yabi safun
Abu Jahalin, Abu Lahabin da wansunsu
Yana koyi da su wawa
15] Ya jama'ar musulminmu, mai kaunar yasan Rahma
Yabar aure cikin idda, Allah bai hallata ba
Ma'aiki bai halatta ba, Malam ya cane ka bari
Kana yi kaito kai wawa
Mutum uku munji sun rates, limamin da ya daura
16]Waliyin wanda ya aiko, da mai nema cikin idda
Sun ko sun ki bin turba, Ta annabi shugaban kowa
Su duka mun ji sun ratse, da wadda ta karkace idda
Har jama'ar da tai shaidar, asasu wuta
Cikin karfe, su kuna ba ruwan kowa
17]Inai muku gargadi dani, maso jinkai
Ya same shi, Yai auren halaliya
Ya dauki ruwa da gammonsa, ko ya saya
Da kurdinsa, Ruwan wankanta ko sallah
Hadisin shugaban kowa.
18]Wajibne ga da namiji, yai bauta ga matansa
Kadan yalwa ta same shi, kadda su durkusa
Dutse, Ni fan day a bare mai yawa
Fadar nan duk da nayita, nib a shisshigi
Nai ba, ka bi ta kabar batun kowa
19]Wanda ya kama matansa, da cinsu da shansu ya dauka
Yana yi gwargwadon iko
Tamkar wanda yai sadaka, har ma yafi mai sadaka
Wurin sarkinmu Allahu
Jalla karimu mai baiwa
20]Ka nemi halas ka cishe su, Allah zai biya kowa
Kadda ka nan haraminya, kowac cita ya kuna
Sai ya tuba ya barta, Rahimu ya maida jinkansa
Allah Rahimin kowa
Yaku masu bin bidi'a, da kun tuba kun barta
21]Kun bi fadar ma'aikinmu, bin farali da bin sunna
Kowa mai hana ku barin, Yalwa sai ta same ku
Dabbobi sa wadaceku, Kishirwa babu
Ko yunwa, bare yafi ya daukeka
Bare bautar Nasarawa
22]Ku shirya zasu bashe ku, kui damara ta bin
Mamman, ku tserewa Nasarawa
Ku bar waka ta shaidani, kui zikiri na bin Allah
Halshe an halitta shi, dan zikiri
Da yin kalma, ku bar zagin ubankowa
23]Ku bar zambon iyayenku, Gwarabjawa
Da Maiganji, ku tuba ku bar gamin kowa
Mai zagin iyayensa, mu mun sami labari
Can a wutar Yahudawa
24]Mu mun sami labariAcan a can a wutar Yahudawa
Macizai har kunaminta, suna dako su cije shi
Kan sun sami bakinsa
Sukan kama suna yago,
Su kan taye kamar yawa.
25]Kunaminta na harbi dubu saba'in,
Karin nasu gaba daya zsu soke shi
Su zarta jikin maki Allah, masabin dan Kuraishawa
Muhammadu wanda yaki ka, shi darajarsa ta tauy
Anan duniya gidan Darbashan, inda Dayyanu mai sakawa dan kowa
26]Ina makadi maki Allah, da shi da ubansa shaidani
Da mai murnar abinda su kai, Allah ya la'ance su
Ma'aiki ya la'ance su, Mala'iku na Allah suma
Sun la'ance su, mutane masu bin sunna
Suma sun la'ance su
27]Kifi maigida a ruwa, shima ya la'ance su
Tsuntsu maigida a sama, shima ya la'ance su
Duk bayio na Allahu, basu san su
Domin kinsu bin Allah
Ta'ala wanda yai kowa
28]Mai ganga maki Allah, kan ya dauki Gangarsa,
Ya kanje dandali nasa
Shaidani yakan tashi, yana gayya gidan kowa
Kowa amsa gayyarsa, can zai kaishi gun gayyu
Shiko Gayyu Zaza ne, cikin zurfin wuta wawa
29]Kowa tuba ya huta, Allah rahimin kowa
Ku tuba ku daina yin bidi'a, Allah ya jikan kowa
Ina makadi uban bidi'a, mai sababinka kin Allah
Yai maka hannu da kafa, ya baka idanu da kafa
Da baki duk da kunnenka, wa zai kirga baiwarsa da yai maka ja'iri wawa
30]Kaki ka gode baiwarsa, menene tsakaninku
Kana bijirar da bayinsa, kana ta kidi suna waka
Kana bauta ga shaidani, kun ki ku bauta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, ku bar bauta ga shaidani
Nufinsa yaje ya yashe ku, ya kai ku cikin wuta wawa
31]Ina makadi uban bidi'a, da kun tuba kun bit
Allah sai ya yafe ku, Rahimu Ubangijin kowa
Kan ance su bar Bidi'a, su kan ce tun iyayensu
Da kakanni ake yinta, shi sabonsa
Tun nan, basa jin fadar kowa
32]Ku duba tun iyayenku, da kakannin iyayenku
Sha sabon karatun nan, suka tarda shi wawa
Ina jin tausayin dangi, basa tausayin kansu
Sun ki su kama bin turbar
Muhammdu shugaban kowa
33]Fitar mata zuwa jeji
Suna nema da dan gyaftoSuna cin kasuwar lahadi...........
34]Yaya ne ka auro su, ba bayi ka auro ba
Kabar su suke fita yawo, tsorci
Ubangiji Allah, Ta'ala wanda yai kow
Ko bayi ka same su, kanka bukace su
Auransu kadda ka bar su su yawo, fada ta ubangijin kowa
35]Kuna cewa iyayenku, basu bada su da ka-
Kanninku, Addini na Ibrahim, yai tsari ga matansa
Sahhabai dukka sunyi tsari, dan kakanku yaki tsari
Ba sauki akai masa ba
Shi ne yaki bin turbar Annabin kowa
36]Fadar Allah Ta'ala ce, zaman mata cikin daki
Kun ki fada ta Allahu, kuke fusshesu gun narko
Bar kallon fadar Allah, ko sarkin kasa ya fadi
Kan ka ki ta ka tashi, gidanka
Da shi da gonarka, don ka barshi bayanka
37]Ka sheka kana yawo, cikin ZazzauKaza
Katsina, ko birnin Kazaurawa
Kamarka mutum kakewa gudu
Ka rasa zamna gidanka
In ka ki fadar Allah, ina magudarka kai wawa?
38]Mala'iku su kamo ka su saka
A sasarin karfe, a sundukin bakin karfe
Sai ka tuba ka barsu, kai hakuri
Da noman so, Allah sai ya yafe ka
Domin bin uban Kasim, jikin Hashimiyawa
39]Ina mai annamimanci, da mai hassada
Da mai ruwa, da mai zina ja'iri bawa
Da mai suka ga addini, da mai gaba
Da malumma, da mai karya cikin jama'a
Da mai zuku yana tazidu............
40]Mai zina ya shiga ya shiga uku, radda ka tada yan adam
Da aljannai da wansunsu, du da mala'ikun Allah
Ana kallonsa duk jama'a, yayi baki bakin zunubi
Kai kace bakin wawa
Da shi da abokiyar la'ana, gabanta kamar ruwan miki
41]Tana yoyo cikin jama'a, kamar randa data burme
Ga doyi kamar kuna
Kaman nan zai kusance ta
Yana lasa da bakinsa
Kamar lasar kare wawa
42]Jahannama can tana dako
Akai mata jairin bawa, maki sarkinmu Allahu
Maki jin gargadin kowa
Mai riya zamu zancansa, maki zancen
Ma'aikinmu, maki jin gargadin kowa
43]Manzo ya cane ya bari, Shirka ce wurin Allah
Shiko yaki mai shirka
Wanda ya bada kayansa, don a fada a cane
Wane, jikan wane, dan wane
Shaidani ya rude shi, don ya batar da shi Wawa
44]Shi bai nemi lada ba, wurin sarkinmu Allahu
Shi dai duniya ta fadi, suit a yabonsa yan
Adam, sun ace ba kamar wane, domin
Sunga wawa ne, shi bai san da karya ba
A’a ya sani it ace, yake bautar kwanikawa.
45]Ina wawa maki turba, fahimci abinda za
Ni fadi, Allah ya halitto ka, dan bautarsa
Ka ki sani, kana neman taro da kwabo
Kaki ka nan shinan Sallah, bar kallon taro da Kwabo
Ko kasan Sule da Dala, ko rumbu guda ka cika, sai wata ran mala’ika, ya dauke ran yabar gawa.
46]Su kai ka su sa cikin rami rami, su lullube
Yar kasa su rufe, su juya can wurin karfe
Suna ta raba sub a naka, Anini guda
Basa baka, Kwabo ma yafi karfinka
Kanan shinan Sallah sai itace, wurin bawa cikin kabarinsa kai wawa
47]Ku san neman taro da kwabo, halaline wurin Allah
Kan ka san shinan Sallah, kadan ko ba shinan
Sallah, haramunce gad an kowa
Allah yayi wo bawa, dan bautarsa kai wawa
Kai ko ka ki bautarsa, dan neman taro da kwabo, ka duba arzikin bawa
47]Rababbe ne wurin Allah, abinda ya bashi ya bashi
Da zai hau samaniya yana neman dadi
Babu yace ya gode mai baiwa
Godewa ga sarkinmu, bin sa da
Bin ma’aikinmu, da bin ulama’u kai wawa
48]Lura fadar da nai bawa, kan ka kita ka tabe
Ba azumi bare sallah, duk aikin addininka
Ba lada wurin Allah, sai ka tambayo malam
Allah yaki addinin
Da ba’a tambayar kowa
48]Azaba can tana dako, ga bawa wanda yaki sani
Kamanan wanda yayi sani, baya aiki da shi
Wawa ku bar wasa ku nemi sani
Said a sani ake samun gidan Rahma
Wurin Sarkinmu Allahu, Ta’alas wanda yai kowa
49]Ana wa’azin bakin bawa, dillalin bakin bawa
Wanda yaje cikin kurmi, yana yawo da ka-
Yansa, kan ace da shi ya cira, yakan ce
Yafi karfinka abinda akan tayi goma, yakan ce Sha Biyar ka taya,
Ba tsoro bare kunya, yaki fadar ma’aikinmu, bare maganar ubankowa.
50]Kiyayi riba haramunce, wanda ya cita zai kone
Ka tsoraci ubangiji Allkah, Tabaraka wanda yai kowa
Karya ma haramunce, kabar san yenta kai wawa
Mai karya cikin jama’a, shi kan keta bakinsa
Yakan je har zuwa keya, kadan karyarsa ta shahara
51]Allah ya la’ance shi, a sa la’ana a goshinsa
Kowag ganshi ya san shi
Duk dabbar gida da dawa, kan tag an shi ta san shi
Ta ce Alhamdu lilLahi ni nagode sarkinmu
Tunda yayi ni ni dabba, naïf makaryacin bawa, mugu fajiri wawa
52]Ina bawan dake hassada, ya tuba ya daina yin hassada
Kan ko yaki ya kone, yana haushin
Rabon Allah, zato nasa ja’iri wawa
Zani yabon ma’aikinmu, tsattsarka uban Kasim
Baban Fadima Zahra, mai hakuri uban dayyabu, Sidi Balaraben kowa
53]Mai haske da kyau Mamman, Mai saje da kyawun
Fuska, gashi da kyan bakin gashi, bashi da furfura
Da yawa, cikin sajensa har gemu
Kan ka san guda goma, kana neman biyar ka dada
Baka samu ba sai ka tsaya, kana kallon wushiryarsa
54]Ga haske yana tashi, turare ma yana tashi
Kamshi ya buche kowa
Ana ajabi da sawunsa, Kan ya taka kan dutse
Wurin takun yakan gurbi, kan ya taka
Rairansa, baka gurin ba yai gurbi, hukumcin Jalla mai baiwa
55]Dadai ka gani bawa, yadda ka tsaida yan adam
Wurin ikonsa Sarkinmu, ranar kaga jayayya
Iyayensu da yayansu, mazaje su da matansu
Sarki shi da fadawa, dogarrai da sauransu
Har da yace da babansa, kai ka batar dani Turba
56]Kana ji na ina ihu, nakan zallko ina juya
Kai ko ka ki yin tsawa
Kowa ya kira dansa, yana nusheshi
Bin turba, kai ko ka ki nushe ni
Bare nabi annabin kowa
57]Ina Magana ga dattijo, tunda ya bar fadar Mamman
Ya ki fada ta Allahu, jallah ubangijin kowa
Yara su da manyansu, kan suka dubi kankanci
Su kance Rabbu sarkinmu, mun bi ta
Shugabanninmu, su suka bi damu turba
58]Rabbu ka fara bashes u, sui nisa da jinkanka
Jallah ubangijin kowa
Wadanga da su da manyansu, jayayya takan
Rude, sukan ce mu musulmi ne
Bad an ku ba manyanmu, su suka ce da su a’a, …………
59]Sukan ce ba Kaman nan ba, ko kace mu bar turba
Mui bautar wanin Allah, ace fa su daina jayayya
Akai su wutar Nasarawa, fadar wa’azi da nai dangi
Don mai hankali na fadi, koda nace daku waka
Tunda ya sa dani acikin, musulmi masu san baiwa
60]Acikin mutane masu yin Sallah
Suna karbar fadar Mamman, Sidi balaraben kowa
Salatin Lahi Sarkinmu, ya tabbata
Ya tabbata nan ga manzonmu
Muhammdu mai dubun baiwa
61]Da aloli da as’habu, damu mabiya umarninsa
Ana ranar dab a bawa, mai debe kewa
Kan ance daku waka, wanene matsarinta
Ku ce masu kankanin bawa, malacin gayyi
Aikin karatu ya buwaye shi, na Qur’ani kaza ilimu, sai sururi abin wawa
62]Cikakken hankalin bawa, yai sauki da surutu
Sakankance da wautarsa,
kan ya yawaita surutu
cikin taro, wajen jama’a
Ku taru gidan zaka wawa.
Bi Bismillah ni bawa, na far yabo ga mai baiwa
Arrahmani baiwarsa, gamamma ce ga dan kowa
Rahmani ya kebe baiwarsa, baya yiwa majusawa
Allahu yai dadin tsira, ga Ahmadu shugaban kowa
Baicin ambaton Allah, nufina gargadin kowa
2]Wanda ya yada addini, baya tambayar kowa
Girman kai ya debe shi, ya sashi ya fandare wawa
Yaku yan uwa dangi, Allah ya halicce mu
Domin tsaida addini, Tawhidi kaza Sallah
Musan Azumi da Zakkarmu, kaza Hajji wajibin kowa
3]Mu sansu, mu sanda yayanmu, kaza matanmu bayinmu
Kanko mun ki sanasshe su, ranar lahira ka sani
Acan aka tambayar kowa, akan doran siradinsa
Ga kaifi, ga makonansa, Kama nan za'a tsaishe ka
Idan yazo dasu ya shige, idan bai zo da kome ba
Wa'ila sai su turo shi, cikin zurfin wuta wawa
4]Bayi na ciki su cane, ya kaitonka kai bawa
Ina halinku ma'aikinku, ya kance 'sun isar da sani'
Iyaye sun ka bashe mu, suna aikin majusawa
Kan ance da su su bari, su kance 'mu iyayenmu
Mun same su sun aika, abinda su kanyi shi zamu bi, bama jin fadar kowa
5]Ka duba can ga kakanku, , Adamu, Nuhu, Idrisu
Da Ibrahim uban kowa, Manyan Annabawa ne
Sun bi fada ta Allahu, tazo har kan ma'aikinmu
Kowak ki ta ya ratse, yabi fadar Yahudawa
6]Yahudu, Nasara sun ratse, shaidani ya rude su
Yace ku tsaya a nushe ku, ga aikin iyayenkuAbin bautarsu su gunki, gama shine mashasharku
Kar ku bi annabin kowaYa jama'a ta addini, bin Allah farillansa
Bin manzo cikin sunna, wanda ya yada bin sunna
Kamar bai aika komai ba, kamar dai wanda yai sallah
Bai zakka ba ya tabe, cikin bin Jallah mai baiwa
7]Wanda ya bauta Allahu, yana sabon iyayensa
Bai karba ba sarkinmu, ka tuba ka bisu kai wawa
Ya mai bauta Allahu, nemi halas abar cinka
Kan ko tabe, haramun wanda ya cita
Misalin gwargwadon lauma
Kwana Arba'in za ai, yana bauta ga sarkinmu
Bai karba Allahu, Jallah ubangijin kowa
8]Ina Malam, Ina Malam Malam tsorci Allahu
Kabar tsoron mutanenka, fada musu gaskiya hakkan
Kan sun bita ka huta, kan sun ki ta ka kubuta
Wurin Sarkinmu Allahu, Jallah Karimu mai baiwa
9]Zan muku gargadi dangi
Ku kai yayanku gun malam
Karatu wajibin kowa
10]Wanda ya samu da nasa, Yaki ya kai shi gun malam
Ya dau alhakin dan sa, Yahudu, Nasara sun samu
Kaza suma majusawa, Kowanne da
Ka haifeshi, duk jama'ar Ma'aikine
Sai babansa yaki shi, yakan koma Nasarawa
11]Malam nemi sarkinka, kace masa yai fadan bidi'a
Bidi'a kishiyar Sunna, kowab bita y rates
Yabi fada ta shaidani, yaki fadar ma'aikinmu
Muhammadu Annabin kowa, wanda yabar fadar MammanYana nushe shi kan turba, Yana kimso cikin jeji, yana yawo kamar giwa
12]Mai yawo cikin jeji, kan yaje cikin jama'a
Mazaje masu bin Allah, suna taro gidan malam
Ko jam'a ta yin sallah, baka ga shi baya sheka yana cigiyar, bata wawa
Koda nace, da ko daji, ba daji na kura ba
13]Ko acikin gidnsa yake, yaki yaje gidan malam
Shi san Allah, bazai Sallah, kace masa
Mai shiga jeji, zaya bace cikin njeji, Babu gudunmawar kowa
Maza mata ku nemi, fada tasa shugaban kowa
14]Wanda ya bar fadar Mamman, yaki fada ta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, Wanda yabar fadar Allahu
Ya kafirta ya watse, yabi safun
Abu Jahalin, Abu Lahabin da wansunsu
Yana koyi da su wawa
15] Ya jama'ar musulminmu, mai kaunar yasan Rahma
Yabar aure cikin idda, Allah bai hallata ba
Ma'aiki bai halatta ba, Malam ya cane ka bari
Kana yi kaito kai wawa
Mutum uku munji sun rates, limamin da ya daura
16]Waliyin wanda ya aiko, da mai nema cikin idda
Sun ko sun ki bin turba, Ta annabi shugaban kowa
Su duka mun ji sun ratse, da wadda ta karkace idda
Har jama'ar da tai shaidar, asasu wuta
Cikin karfe, su kuna ba ruwan kowa
17]Inai muku gargadi dani, maso jinkai
Ya same shi, Yai auren halaliya
Ya dauki ruwa da gammonsa, ko ya saya
Da kurdinsa, Ruwan wankanta ko sallah
Hadisin shugaban kowa.
18]Wajibne ga da namiji, yai bauta ga matansa
Kadan yalwa ta same shi, kadda su durkusa
Dutse, Ni fan day a bare mai yawa
Fadar nan duk da nayita, nib a shisshigi
Nai ba, ka bi ta kabar batun kowa
19]Wanda ya kama matansa, da cinsu da shansu ya dauka
Yana yi gwargwadon iko
Tamkar wanda yai sadaka, har ma yafi mai sadaka
Wurin sarkinmu Allahu
Jalla karimu mai baiwa
20]Ka nemi halas ka cishe su, Allah zai biya kowa
Kadda ka nan haraminya, kowac cita ya kuna
Sai ya tuba ya barta, Rahimu ya maida jinkansa
Allah Rahimin kowa
Yaku masu bin bidi'a, da kun tuba kun barta
21]Kun bi fadar ma'aikinmu, bin farali da bin sunna
Kowa mai hana ku barin, Yalwa sai ta same ku
Dabbobi sa wadaceku, Kishirwa babu
Ko yunwa, bare yafi ya daukeka
Bare bautar Nasarawa
22]Ku shirya zasu bashe ku, kui damara ta bin
Mamman, ku tserewa Nasarawa
Ku bar waka ta shaidani, kui zikiri na bin Allah
Halshe an halitta shi, dan zikiri
Da yin kalma, ku bar zagin ubankowa
23]Ku bar zambon iyayenku, Gwarabjawa
Da Maiganji, ku tuba ku bar gamin kowa
Mai zagin iyayensa, mu mun sami labari
Can a wutar Yahudawa
24]Mu mun sami labariAcan a can a wutar Yahudawa
Macizai har kunaminta, suna dako su cije shi
Kan sun sami bakinsa
Sukan kama suna yago,
Su kan taye kamar yawa.
25]Kunaminta na harbi dubu saba'in,
Karin nasu gaba daya zsu soke shi
Su zarta jikin maki Allah, masabin dan Kuraishawa
Muhammadu wanda yaki ka, shi darajarsa ta tauy
Anan duniya gidan Darbashan, inda Dayyanu mai sakawa dan kowa
26]Ina makadi maki Allah, da shi da ubansa shaidani
Da mai murnar abinda su kai, Allah ya la'ance su
Ma'aiki ya la'ance su, Mala'iku na Allah suma
Sun la'ance su, mutane masu bin sunna
Suma sun la'ance su
27]Kifi maigida a ruwa, shima ya la'ance su
Tsuntsu maigida a sama, shima ya la'ance su
Duk bayio na Allahu, basu san su
Domin kinsu bin Allah
Ta'ala wanda yai kowa
28]Mai ganga maki Allah, kan ya dauki Gangarsa,
Ya kanje dandali nasa
Shaidani yakan tashi, yana gayya gidan kowa
Kowa amsa gayyarsa, can zai kaishi gun gayyu
Shiko Gayyu Zaza ne, cikin zurfin wuta wawa
29]Kowa tuba ya huta, Allah rahimin kowa
Ku tuba ku daina yin bidi'a, Allah ya jikan kowa
Ina makadi uban bidi'a, mai sababinka kin Allah
Yai maka hannu da kafa, ya baka idanu da kafa
Da baki duk da kunnenka, wa zai kirga baiwarsa da yai maka ja'iri wawa
30]Kaki ka gode baiwarsa, menene tsakaninku
Kana bijirar da bayinsa, kana ta kidi suna waka
Kana bauta ga shaidani, kun ki ku bauta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, ku bar bauta ga shaidani
Nufinsa yaje ya yashe ku, ya kai ku cikin wuta wawa
31]Ina makadi uban bidi'a, da kun tuba kun bit
Allah sai ya yafe ku, Rahimu Ubangijin kowa
Kan ance su bar Bidi'a, su kan ce tun iyayensu
Da kakanni ake yinta, shi sabonsa
Tun nan, basa jin fadar kowa
32]Ku duba tun iyayenku, da kakannin iyayenku
Sha sabon karatun nan, suka tarda shi wawa
Ina jin tausayin dangi, basa tausayin kansu
Sun ki su kama bin turbar
Muhammdu shugaban kowa
33]Fitar mata zuwa jeji
Suna nema da dan gyaftoSuna cin kasuwar lahadi...........
34]Yaya ne ka auro su, ba bayi ka auro ba
Kabar su suke fita yawo, tsorci
Ubangiji Allah, Ta'ala wanda yai kow
Ko bayi ka same su, kanka bukace su
Auransu kadda ka bar su su yawo, fada ta ubangijin kowa
35]Kuna cewa iyayenku, basu bada su da ka-
Kanninku, Addini na Ibrahim, yai tsari ga matansa
Sahhabai dukka sunyi tsari, dan kakanku yaki tsari
Ba sauki akai masa ba
Shi ne yaki bin turbar Annabin kowa
36]Fadar Allah Ta'ala ce, zaman mata cikin daki
Kun ki fada ta Allahu, kuke fusshesu gun narko
Bar kallon fadar Allah, ko sarkin kasa ya fadi
Kan ka ki ta ka tashi, gidanka
Da shi da gonarka, don ka barshi bayanka
37]Ka sheka kana yawo, cikin ZazzauKaza
Katsina, ko birnin Kazaurawa
Kamarka mutum kakewa gudu
Ka rasa zamna gidanka
In ka ki fadar Allah, ina magudarka kai wawa?
38]Mala'iku su kamo ka su saka
A sasarin karfe, a sundukin bakin karfe
Sai ka tuba ka barsu, kai hakuri
Da noman so, Allah sai ya yafe ka
Domin bin uban Kasim, jikin Hashimiyawa
39]Ina mai annamimanci, da mai hassada
Da mai ruwa, da mai zina ja'iri bawa
Da mai suka ga addini, da mai gaba
Da malumma, da mai karya cikin jama'a
Da mai zuku yana tazidu............
40]Mai zina ya shiga ya shiga uku, radda ka tada yan adam
Da aljannai da wansunsu, du da mala'ikun Allah
Ana kallonsa duk jama'a, yayi baki bakin zunubi
Kai kace bakin wawa
Da shi da abokiyar la'ana, gabanta kamar ruwan miki
41]Tana yoyo cikin jama'a, kamar randa data burme
Ga doyi kamar kuna
Kaman nan zai kusance ta
Yana lasa da bakinsa
Kamar lasar kare wawa
42]Jahannama can tana dako
Akai mata jairin bawa, maki sarkinmu Allahu
Maki jin gargadin kowa
Mai riya zamu zancansa, maki zancen
Ma'aikinmu, maki jin gargadin kowa
43]Manzo ya cane ya bari, Shirka ce wurin Allah
Shiko yaki mai shirka
Wanda ya bada kayansa, don a fada a cane
Wane, jikan wane, dan wane
Shaidani ya rude shi, don ya batar da shi Wawa
44]Shi bai nemi lada ba, wurin sarkinmu Allahu
Shi dai duniya ta fadi, suit a yabonsa yan
Adam, sun ace ba kamar wane, domin
Sunga wawa ne, shi bai san da karya ba
A’a ya sani it ace, yake bautar kwanikawa.
45]Ina wawa maki turba, fahimci abinda za
Ni fadi, Allah ya halitto ka, dan bautarsa
Ka ki sani, kana neman taro da kwabo
Kaki ka nan shinan Sallah, bar kallon taro da Kwabo
Ko kasan Sule da Dala, ko rumbu guda ka cika, sai wata ran mala’ika, ya dauke ran yabar gawa.
46]Su kai ka su sa cikin rami rami, su lullube
Yar kasa su rufe, su juya can wurin karfe
Suna ta raba sub a naka, Anini guda
Basa baka, Kwabo ma yafi karfinka
Kanan shinan Sallah sai itace, wurin bawa cikin kabarinsa kai wawa
47]Ku san neman taro da kwabo, halaline wurin Allah
Kan ka san shinan Sallah, kadan ko ba shinan
Sallah, haramunce gad an kowa
Allah yayi wo bawa, dan bautarsa kai wawa
Kai ko ka ki bautarsa, dan neman taro da kwabo, ka duba arzikin bawa
47]Rababbe ne wurin Allah, abinda ya bashi ya bashi
Da zai hau samaniya yana neman dadi
Babu yace ya gode mai baiwa
Godewa ga sarkinmu, bin sa da
Bin ma’aikinmu, da bin ulama’u kai wawa
48]Lura fadar da nai bawa, kan ka kita ka tabe
Ba azumi bare sallah, duk aikin addininka
Ba lada wurin Allah, sai ka tambayo malam
Allah yaki addinin
Da ba’a tambayar kowa
48]Azaba can tana dako, ga bawa wanda yaki sani
Kamanan wanda yayi sani, baya aiki da shi
Wawa ku bar wasa ku nemi sani
Said a sani ake samun gidan Rahma
Wurin Sarkinmu Allahu, Ta’alas wanda yai kowa
49]Ana wa’azin bakin bawa, dillalin bakin bawa
Wanda yaje cikin kurmi, yana yawo da ka-
Yansa, kan ace da shi ya cira, yakan ce
Yafi karfinka abinda akan tayi goma, yakan ce Sha Biyar ka taya,
Ba tsoro bare kunya, yaki fadar ma’aikinmu, bare maganar ubankowa.
50]Kiyayi riba haramunce, wanda ya cita zai kone
Ka tsoraci ubangiji Allkah, Tabaraka wanda yai kowa
Karya ma haramunce, kabar san yenta kai wawa
Mai karya cikin jama’a, shi kan keta bakinsa
Yakan je har zuwa keya, kadan karyarsa ta shahara
51]Allah ya la’ance shi, a sa la’ana a goshinsa
Kowag ganshi ya san shi
Duk dabbar gida da dawa, kan tag an shi ta san shi
Ta ce Alhamdu lilLahi ni nagode sarkinmu
Tunda yayi ni ni dabba, naïf makaryacin bawa, mugu fajiri wawa
52]Ina bawan dake hassada, ya tuba ya daina yin hassada
Kan ko yaki ya kone, yana haushin
Rabon Allah, zato nasa ja’iri wawa
Zani yabon ma’aikinmu, tsattsarka uban Kasim
Baban Fadima Zahra, mai hakuri uban dayyabu, Sidi Balaraben kowa
53]Mai haske da kyau Mamman, Mai saje da kyawun
Fuska, gashi da kyan bakin gashi, bashi da furfura
Da yawa, cikin sajensa har gemu
Kan ka san guda goma, kana neman biyar ka dada
Baka samu ba sai ka tsaya, kana kallon wushiryarsa
54]Ga haske yana tashi, turare ma yana tashi
Kamshi ya buche kowa
Ana ajabi da sawunsa, Kan ya taka kan dutse
Wurin takun yakan gurbi, kan ya taka
Rairansa, baka gurin ba yai gurbi, hukumcin Jalla mai baiwa
55]Dadai ka gani bawa, yadda ka tsaida yan adam
Wurin ikonsa Sarkinmu, ranar kaga jayayya
Iyayensu da yayansu, mazaje su da matansu
Sarki shi da fadawa, dogarrai da sauransu
Har da yace da babansa, kai ka batar dani Turba
56]Kana ji na ina ihu, nakan zallko ina juya
Kai ko ka ki yin tsawa
Kowa ya kira dansa, yana nusheshi
Bin turba, kai ko ka ki nushe ni
Bare nabi annabin kowa
57]Ina Magana ga dattijo, tunda ya bar fadar Mamman
Ya ki fada ta Allahu, jallah ubangijin kowa
Yara su da manyansu, kan suka dubi kankanci
Su kance Rabbu sarkinmu, mun bi ta
Shugabanninmu, su suka bi damu turba
58]Rabbu ka fara bashes u, sui nisa da jinkanka
Jallah ubangijin kowa
Wadanga da su da manyansu, jayayya takan
Rude, sukan ce mu musulmi ne
Bad an ku ba manyanmu, su suka ce da su a’a, …………
59]Sukan ce ba Kaman nan ba, ko kace mu bar turba
Mui bautar wanin Allah, ace fa su daina jayayya
Akai su wutar Nasarawa, fadar wa’azi da nai dangi
Don mai hankali na fadi, koda nace daku waka
Tunda ya sa dani acikin, musulmi masu san baiwa
60]Acikin mutane masu yin Sallah
Suna karbar fadar Mamman, Sidi balaraben kowa
Salatin Lahi Sarkinmu, ya tabbata
Ya tabbata nan ga manzonmu
Muhammdu mai dubun baiwa
61]Da aloli da as’habu, damu mabiya umarninsa
Ana ranar dab a bawa, mai debe kewa
Kan ance daku waka, wanene matsarinta
Ku ce masu kankanin bawa, malacin gayyi
Aikin karatu ya buwaye shi, na Qur’ani kaza ilimu, sai sururi abin wawa
62]Cikakken hankalin bawa, yai sauki da surutu
Sakankance da wautarsa,
kan ya yawaita surutu
cikin taro, wajen jama’a
Ku taru gidan zaka wawa.
Tuesday, April 17, 2007
TABARKOKO; Daga Sarkin Zazzau Aliyu Dansidi
Wannan dai itace wakar Tabarkoko, wadda sarkin Zazzau Aliyu Dansidi ya wallafa. Wakar dai gugar zana ce, ko kuma ince shagube da bai nuna wanda yake yiwa ba. Amma ana zaton ko yayi tane domin yiwa fadawansa shagube, game da yadda suke tafiyar da rayuwarsu.
Aboka zo nan mu bata
ka dubi dan dai ga wata
wada daban da batta
Haske na rana da wata
Ba zasu zam daidai ba
He dubi dai tsettsewa
Ya samu kifi a wuya
shina zaton babu kaya
Inta kafe mai ga wuya
ba zasu debe mai ba
He dubi dai irame
Can tai gida a rame
Can dauri kau ta rame
kyaushe mijin Irame
gallonsu ba zaki ba
Abin ga dai gama na
kare shi tono magana
zai iske kura a hana
ba dun akwai wata magana
da bai fito rannan ba
Ai ga fage ga doki
Noman fako ba taki
ai maganan ta sake
da dan kare da na doki
ba zasu zam daidai ba
Mu namu ga ta da taki
babu biri ba zaki
barde dubu mai doki
da zamanin kai taki
da bamu samu nai ba
Saura garin ya waye
duk kokuwan tai kaye
Damu ga yan tawaye
da masu da da maye
zamansu bai zam dai ba
Karya take zabira
bata zama gurara
Iska daban da sarara
matar maza da bera
kudinsu bai zam dai ba
Na ganshi duk ya kwabe
Yayi tabo ya tabe
yayi bago ya rabe
Neman jini ga babe
Ba za'a samu nai ba
Zo ka taba dai ka jiya
Yau muke koko jiya?
Haure ka ciwo ijiya
in yayi sai ayi jinya
ba za'a debewa ba
Ko ka iso, ko ka tsaya
Taunan aya ko ka iya?
Amale cimansa kaya
Jaki, da sa, ko akuya
Ba zasu taunawa ba
Kaya ga Rakumi shike
Takarkari sai taiki
Saimo akanwa taki
Tsaiko akanwa daki
bukka ba ta dauka ba.
Makaryata, mahassada
basu iya komi da guda
na yanzu ba ko da na da
tara su dai duk ka gwada
ba su zamo daidai ba
Babba da jaka ya zaka
Yana bidan kifi tsaka
gulbin da dorina tsaka
Gefen kadanni ya saka
kafansa ba zai kai ba
Yada guda ka dau guda
Duk ka fasa su ba guda
hanya mararraba guda
gaba-gaba akan guda
cikinsu bai ba daya ba
Ga kutu ga Tabarkoko
Ga dole-dole tai hako
ni naga tana ga fako
kai mai bago shiga sako
Wurin ba'a zo mai ba
Kwaddo ina kadangare
Naji kafarsa ta kare
ya bar diyanshi gangare
in yayi nan sai a tare
ni ban gano zai kai ba
Ko kaga mai digirgire
wuya awa gadar zare
Takuna zance hantsare
da zamanin bakin zare
da basu sa riga ba
Ga tsada mai dan tashi
kullum ta dau albashi
ba ta ci bata hana bashi
ran da safiya tai fashi
ba za'a koka mai ba
Ga wani tantalwashi
na biyunsu mai kan bashi
na ukkunsu bashi da nashi
Da dai ana tuna bashi
da basu sa riga ba
Nazundu mai zaka fada
kullum ka gana da rada
roko awa dan makada
a baka bashi a dada
ba zashi fasawa ba
Ga wani wai shi ya iya
yaje ya jawo igiya
ta nannade mai a wuya
yana kira da waiwaya
ba za'a debe mai ba
Shin me ya samu shamuwa
na ga tana ta dimuwa
naga ruwan da kainuwa
ba dun kasan da kaguwa
da bata sauka anan ba
Da kunkuru da bushiyta
halinsu dai noke wuya
ga zamani na waiwaya
da zamanin mazan jiya
ni naga da basu kai ba
Debi yawa, sam ma kadan
yanzu yawa ta zam kadan
a hankali kadan-kadan
Gidan yawa kan yi kadan
Abinga ba banza ba
Nai muku waka ta batu
ku zo ku nemi yan batu
awa su lugegen batu
tara fasihai na batu
ba zasu ganewa ba
Mai wagga waka ta batu
Ali Amiru wan Shatu
Shine abokin Warqatu
Dadai da sirri na batu
Da bashi boyewa ba
Allahu shi yai mu duka
Baki fari yai su duka
Shudi da Korensu duka
Da Ja da Rawaya duka
Shi dai kayi ba wani ba
Zama fa shi dai ya iya
Shi yo mutum shi tafiya
Wadansu ko shi yi su tsaya
Shi yai itace da kaya
Nufinsa ne ba wani ba
Shi yai dawa da karkara
Shi yai dawa da karkara
Shi yai kwai, yai zakara
Yai zabuwa, yai fakara
Shi ad damu ba wani ba
Bautanmu dai hasana'u
Zam haufu, duk dada rija'u
Ku lura ko asma'u
Nisa'u masu gina'u
Sha'aninsu ba karko ba
Asma'u an sanki da dai
Halinki ki ne ko can dadai
Shirinki kullum na kwadai
Maso biyu,bashi da dai
Batun ga ba karyaba
Ywaita rokon Jalla
Ka wakkale ga Allah
Ka zam kula da Salla
A baka ni'ima walla
Anan da can ba waiba
Muyi zikiri da salati
Mu karkare afati
Gobe mu san najjati
Ga shugaban hajati
Muhammadu bawani ba
Aboka zo nan mu bata
ka dubi dan dai ga wata
wada daban da batta
Haske na rana da wata
Ba zasu zam daidai ba
He dubi dai tsettsewa
Ya samu kifi a wuya
shina zaton babu kaya
Inta kafe mai ga wuya
ba zasu debe mai ba
He dubi dai irame
Can tai gida a rame
Can dauri kau ta rame
kyaushe mijin Irame
gallonsu ba zaki ba
Abin ga dai gama na
kare shi tono magana
zai iske kura a hana
ba dun akwai wata magana
da bai fito rannan ba
Ai ga fage ga doki
Noman fako ba taki
ai maganan ta sake
da dan kare da na doki
ba zasu zam daidai ba
Mu namu ga ta da taki
babu biri ba zaki
barde dubu mai doki
da zamanin kai taki
da bamu samu nai ba
Saura garin ya waye
duk kokuwan tai kaye
Damu ga yan tawaye
da masu da da maye
zamansu bai zam dai ba
Karya take zabira
bata zama gurara
Iska daban da sarara
matar maza da bera
kudinsu bai zam dai ba
Na ganshi duk ya kwabe
Yayi tabo ya tabe
yayi bago ya rabe
Neman jini ga babe
Ba za'a samu nai ba
Zo ka taba dai ka jiya
Yau muke koko jiya?
Haure ka ciwo ijiya
in yayi sai ayi jinya
ba za'a debewa ba
Ko ka iso, ko ka tsaya
Taunan aya ko ka iya?
Amale cimansa kaya
Jaki, da sa, ko akuya
Ba zasu taunawa ba
Kaya ga Rakumi shike
Takarkari sai taiki
Saimo akanwa taki
Tsaiko akanwa daki
bukka ba ta dauka ba.
Makaryata, mahassada
basu iya komi da guda
na yanzu ba ko da na da
tara su dai duk ka gwada
ba su zamo daidai ba
Babba da jaka ya zaka
Yana bidan kifi tsaka
gulbin da dorina tsaka
Gefen kadanni ya saka
kafansa ba zai kai ba
Yada guda ka dau guda
Duk ka fasa su ba guda
hanya mararraba guda
gaba-gaba akan guda
cikinsu bai ba daya ba
Ga kutu ga Tabarkoko
Ga dole-dole tai hako
ni naga tana ga fako
kai mai bago shiga sako
Wurin ba'a zo mai ba
Kwaddo ina kadangare
Naji kafarsa ta kare
ya bar diyanshi gangare
in yayi nan sai a tare
ni ban gano zai kai ba
Ko kaga mai digirgire
wuya awa gadar zare
Takuna zance hantsare
da zamanin bakin zare
da basu sa riga ba
Ga tsada mai dan tashi
kullum ta dau albashi
ba ta ci bata hana bashi
ran da safiya tai fashi
ba za'a koka mai ba
Ga wani tantalwashi
na biyunsu mai kan bashi
na ukkunsu bashi da nashi
Da dai ana tuna bashi
da basu sa riga ba
Nazundu mai zaka fada
kullum ka gana da rada
roko awa dan makada
a baka bashi a dada
ba zashi fasawa ba
Ga wani wai shi ya iya
yaje ya jawo igiya
ta nannade mai a wuya
yana kira da waiwaya
ba za'a debe mai ba
Shin me ya samu shamuwa
na ga tana ta dimuwa
naga ruwan da kainuwa
ba dun kasan da kaguwa
da bata sauka anan ba
Da kunkuru da bushiyta
halinsu dai noke wuya
ga zamani na waiwaya
da zamanin mazan jiya
ni naga da basu kai ba
Debi yawa, sam ma kadan
yanzu yawa ta zam kadan
a hankali kadan-kadan
Gidan yawa kan yi kadan
Abinga ba banza ba
Nai muku waka ta batu
ku zo ku nemi yan batu
awa su lugegen batu
tara fasihai na batu
ba zasu ganewa ba
Mai wagga waka ta batu
Ali Amiru wan Shatu
Shine abokin Warqatu
Dadai da sirri na batu
Da bashi boyewa ba
Allahu shi yai mu duka
Baki fari yai su duka
Shudi da Korensu duka
Da Ja da Rawaya duka
Shi dai kayi ba wani ba
Zama fa shi dai ya iya
Shi yo mutum shi tafiya
Wadansu ko shi yi su tsaya
Shi yai itace da kaya
Nufinsa ne ba wani ba
Shi yai dawa da karkara
Shi yai dawa da karkara
Shi yai kwai, yai zakara
Yai zabuwa, yai fakara
Shi ad damu ba wani ba
Bautanmu dai hasana'u
Zam haufu, duk dada rija'u
Ku lura ko asma'u
Nisa'u masu gina'u
Sha'aninsu ba karko ba
Asma'u an sanki da dai
Halinki ki ne ko can dadai
Shirinki kullum na kwadai
Maso biyu,bashi da dai
Batun ga ba karyaba
Ywaita rokon Jalla
Ka wakkale ga Allah
Ka zam kula da Salla
A baka ni'ima walla
Anan da can ba waiba
Muyi zikiri da salati
Mu karkare afati
Gobe mu san najjati
Ga shugaban hajati
Muhammadu bawani ba
Monday, April 16, 2007
Wasiyya Sipikiyya; Daga Mudi Spikin
Ta'ala ina rokonka ranar da zan cika
Kasa in cika Allah cikin daki na
Gaban duk iyali na da 'ya'ya da 'yan'uwa
Allah ina rokon ka sai a gidana
Idan na cika yan'uwa na gaya muku
Da kun ji cikawata ku taru gidana
Idan har da rana abin yazo ko cikin dare
Batun jinkiri kar dai ya faru wurina
Idan anyi sallah an gama kar a dakata
A dauka kawai hanyar zuwa kabarina
Idan anka je da zuwa a sani ciki kawai
Cikin hankali domin tuno lamarina
Kasar kabarin kuma kar a ware daban-daban
A turo gaba daya duk ta watsu a kaina
Idan aka kare gini da an tashi an gama
Ku koma wajen harkarku ya jama'ata
Batun sadakar Uku, ko Bakwai, ko ta Arba'in
Kaza shekara wallahi babu ruwana
Irin masu kukan nan da ihu da razana
Don Allah na roke ku kar kuyi kaina
Ina tausayin ku kwarai zuwa gun jana'iza
Kaza wahalar tafiya hakan kabarina
Kaza wahalar wanka da dauko ni don zuwa
Cikin makara tafiya zuwa karshe na
Hakika a rannan da da ikon da zan iya
Ya sa tausayin a wajen dukan jama'ana
Anan zan tsaya domin wasiyarmu ta tsaya
Mudi Spikin ne uba ga Amina
Kasa in cika Allah cikin daki na
Gaban duk iyali na da 'ya'ya da 'yan'uwa
Allah ina rokon ka sai a gidana
Idan na cika yan'uwa na gaya muku
Da kun ji cikawata ku taru gidana
Idan har da rana abin yazo ko cikin dare
Batun jinkiri kar dai ya faru wurina
Idan anyi sallah an gama kar a dakata
A dauka kawai hanyar zuwa kabarina
Idan anka je da zuwa a sani ciki kawai
Cikin hankali domin tuno lamarina
Kasar kabarin kuma kar a ware daban-daban
A turo gaba daya duk ta watsu a kaina
Idan aka kare gini da an tashi an gama
Ku koma wajen harkarku ya jama'ata
Batun sadakar Uku, ko Bakwai, ko ta Arba'in
Kaza shekara wallahi babu ruwana
Irin masu kukan nan da ihu da razana
Don Allah na roke ku kar kuyi kaina
Ina tausayin ku kwarai zuwa gun jana'iza
Kaza wahalar tafiya hakan kabarina
Kaza wahalar wanka da dauko ni don zuwa
Cikin makara tafiya zuwa karshe na
Hakika a rannan da da ikon da zan iya
Ya sa tausayin a wajen dukan jama'ana
Anan zan tsaya domin wasiyarmu ta tsaya
Mudi Spikin ne uba ga Amina
Subscribe to:
Posts (Atom)