Monday, April 16, 2007

Wakar Shehu malam Nasara Kabara; Daga Mudi Spikin

Bagadada suna ajabi nasa
Don sun ga irin himma tasa
Suka ce kai wannan ya isa
Har yanzu suna Allah yasa
Su ga Alhaji malam Nasiru

Qadiriyya yai zurfi ciki
Darajarta kwarai yai arziki
Jama'a da yawa duk sun saki
Hairi a gare shi daki-daki
Kuma ga takawa gun Nasiru

Shi gwarz ne mai kokari
Mai kamala mai kyawon shiri
Ga mutunci gashi da hankuri
Ko ina an san shi gari-gari
Kwarjini sai Malam Nasiru

RASHA Abokan Fita Kunya; Daga Mudi Spikin

Wannan waka ta jawowa Malam Mudi dauri a gidan yari. Domin a fahimtar Turawan Mulki wannan wani sako ne da kan iya tunzura talakawa suyi bore, kuma kan iya jefa kasa cikin juyin-juya hali irin na Kwaminisanci. Mudi Spikin ya rubuta wannan waka a 1948. Ga dai wakar

Ya yan'uwa ku zo don ku ji ni
Zan wo bayani akan Rusiya

Gama Ingilishi fa sun tashi haikan
Suka suke yi akan Rusiya

Da babbata hanyarsu don kar a so su
Don kar su zo nan mutan Rusiya

Shine nake so in wo dan bayani
Domin ku gane kasar Rusiya

Kasa ce ta kirki da himma garesu
Da kaunar mutane kasar Rusiya

Wakilinsu Malik sunansa ke nan
Sunan musulmi da ba fariya

Ni dai ace yau zan samu iko
Ni sai in koma kasar Rusiya

Kamar na iya tsunts inje can in Zauna
Idan na tuno su mutan Rusiya

Girmama kowa dabi'arsu ce
Ibada kamar Hajji sai Rusiya

Da son musulunci da bayar da zakka
Yawan azumi sai kasar Rusiya

Kwalta na banza damu bamu samu
Da kafur akeyi acan Rusiya

Da banki na rance idan har kana so
Ko fam Dubu Goma baki daya

Musaki acan sai ya zauna da Gwamna
Wajen shawara babu kin gaskiya

Sa'annan da sauran abubba na kirki
Suna da yawa a kasar Rusiya

Gidaje dubu Goma ne don Musakai
A yau su kasar wane ba ko daya

Akwai Talakawa akwai Tajirai
Kamar dai kasarmu ta Nijeriya

Anan gaba na tabbata babu shakka
Nijeriya zamu zam Rusiya

Mu zam mun fice daga gun Ingilishi
Mutanen daba sa rikon gaskiya

Sun barmu babu kudi babu gona
Babu abin yi cikin gaskiya

Sun shekaru yanzu Hamsin kasarmu
Ba taimako babu son gaskiya

Ta'ala Rahimu kadai taimakemu
Ka kawo mutan Rasha Nijeriya

Idan aka ce wa ya tsara ta waka
Ya bayyana halin mutan Rusiya

Ba zan boye suna ba ko za'a nema
Mudi spikin maso Rusiya

Gama bani tsoro na dauri hakika
Akan Rasha ma sai in bar duniya

Karara; daga Malam Mudi Spikin

An haifi Alhaji Mudi Spikin a ran 1 ga watan Oktoba 1930, a unguwar Darma da ke birnin Kano. Yayi karatun qur'ani a hannun Malam Umaru Badamagare. Bai taba zuwa makarantar boko ba, amma duk da haka, ya zauna jarrabawa GCE Ordinary level, ta hanyar yin rijista da wata kwaleji a Ingila, acikin 1960. Ya sami illimin zamani ne a hannun abokansa na gwagwarmayar siyasa irinsu; Malam Sa'adu Zungur, Malam Aminu Kano, da kuma Alhaji Yusuf Maitama Sule. Yana cikin mutanen da suka kafa jam'iyyar kwato yancin talaka wato NEPU a 1950. Ya fara rubuta wakokinsa tun a 1948, ya fara da wakarsa ta "Rasha Abokan Tafiya", da kuma wani raddi da yayiwa malaminsa, wato malam Sa'adu Zungur maitaken "Arewa Jamhuriya Kawai".

A ya jama'a ina tashin
Ku dan ku rage yawan bacci

Ayau na zo gareku da sha
Wara don kara inganci

Mu wo himma mu tashi tsaye
Mu gyara kasa ta san yanci

Mu kawo shawara mai kyau
Mu tashi mu yaki jahilci

Rashin illimi ya sanya yau
Kasar nan ke yawan baci

Fa sai mun tsaya gyara
Na sosai babu jahilci

Sannan zamu san matsayi
Mu tsere wa wulakanci

Idan ba tattali a kasa
Hakika dole ta baci

Idan an zubda hakkin yan
Adam domin wulakanci

Idan masana kwarai an zub
Da su domin rashin yanci

Idan sharia ta zam ciniki
Ana nunnuna bambanci

Idan kuma masu aiki sun
Zamo duk babu inganci

Idan aiki ya zamto ba
Ayi, sai an ciwo hanci

Idan hairi a baki ake
Fada sharri cikin zuci

Idan da akwai yawan hassada
Da bata mutum da iskanci

Idan da akwai yawanta saki
Na aure don wulakanci

Idan ba tanadi wai duk
Wata sai anyi angwanci

Idan aure ya zam a kasa
Ana yi ne da jahilci

Idan kayan biki aka mai
Da su tamkar na dillanci

Idan ga jahilai a kasa
Na kin canji da shashanci

Idan da zama na banza, ba
Sana'a ai ta kakaci

A sa fatala gaban goshi
Da hula wai tsageranci

Ana ta musu ana karta
Ana zance na wawanci

Idan kuma ga yawan zargi
Na banza ga rashin yanci

Idan wani dan'uwa wai yayi
Samu ayi munafunci

Idan sharri ya zo a iza
Nufi dai ayi wulakanci

Idan da akwai yawan camfi
Da bori masu shashanci

Idan da akwai yawan tsegun
Guman banza na jahilci

Idan a kasa ya zam an go
Yi bayan masu lalaci

Idan mai gaskiya ya zamo
A kullum zai ga kaskanci

Idan gata ya sanya wadan
Su yin shirme da shashanci

Idan aka maida wadansu kamar
Ace bayi rashin yanci

Idan yan kasuwa suka zam
Sana'a aita hainici

Idan ga karuwai a kasa
A kullum ai ta fasicci

Idan da giya an ta
Ru kullm nuna iskanci

Idan ba tausayi a kasa
Mutane na ta makirci

Idan kuma har amana tai
Kadan sai nuna ha'inci

Idan har maluma suka bar
Sani i zuwa fagen baci

Idan bidia ta zam an gir
Gina kuma babu sassauci

Idan yaya suna sabon
Mahaifa har da kaskanci

Idan a kasa akwai wannan
Hakika dole ta baci

Fa sai in anyi aiki za
Hiri ba nuna lalaci

Sa'annan zamu san haske
Mu tserewa wulakanci

Abinda na farfadan nanYan
'Uwa da akwai muhimmanci

Fa duk gyaran wadannan na
Garemu cikin batun yanci

Mu daina abinda bashi da kyau
Mu daina biyewa jahilci.






Tuesday, April 10, 2007

Wakar Kidayar Mutanen Nijeriya 1973; Daga Hajiya Yar Shehu

An haifi Hajiya Yar Shehu a shekara 1937, a garin Dambatta. Ta halarci makarantar Yanmata dake lardin Sakkwato, bayan ta kammala karatun addini a gida. Ta fara aiki a ma'aikatar lafiya ta Kano a 1953, bayan ta koyar a makarantun Firamare. Daga bisani ta koma kamfanin jiragen sama na Kano, a matsayin mai bada hanyar Tarho, inda ta zama jami'ar kula da ma'aikata na ma'aikatar. Haka kuma member ce a shahararriyar kungiyar mawakan nan, wato Hikima Kulob. Ta dai wallafi wakoki da dama, domin fadakarwa, zaburarwa, illimantarwa, wa'azantarwa, da sauransu, wakokinta sun hada da "Waka da Bayani", Wakar Kidaya, Wakar Zamani dss. wadanda insha Allahu zamu kawo muku su, da dai-dai. Ta rubuta wannan waka, domin fadakar da mutane akan kidayar jama'a wato Census da akayi a 1973. Ga dai Wakar;

BismilLah na fara da sunan Rabbana
Allah Ta'ala Jallah Sarkin gaskiya

Kai ne Sami'un Basiru, Mai ji, Mai gani
Ka tsare mu sharrin, masu sharrin duniya

Domin Muhammadu shugaban duka duniya
Har lahira ma, in ka bashi gaba daya

Don Annabawa har Sahabbai Mursalai
Har dukka dangogin Rasulu abin biya

Kayi taimako agareni kai min kangiya
Kai ne katanga wadda bata zagaya

To zanyi tsari dan Kidaya ne yankuna
Ta Arewa harma duk kasarmu gaba daya

Allah Hakimu hikimarka da ta isa
Kasa mu gane don mu bayyana gaskiya

Don kada mu fada ayyukan shibcin gizo
Da ya kasa dauka, sai ya karo kungiya

Ga gargadina gun sarakai malamai
Lalle ku dage don ku kange areriya

Komai idanu bakuna har kunnuwa
Komai ya baci wuyanku ne zai rataya

Ko Shehu Fodiye ku yaba tuta tasa
Har ma amanar dogare gaba daya

Domin hakan nan sai ku tashi ku taimaka
Akan kidayar na jihannunmu gaba daya

Don kadda a kwaso kyankyaso da su kwarkwata
a zazzage mana nan Arewa mu sha wuya

Allah jikansu na baya manya sun wuce
Giwa saka kawo ban Arewa gaba daya

Dan kadda mu ji ta kururuwa rashe idon kuma
Har ma da makirci na mai kin gaskiya

Kuma kadda jahilci ya sa sarkacen tasa
Ya ja kafa kuma har wuyanmu gaba daya

In anka zo kirga ya tabbata mun zaka
Mun bayyana musu dangunanmu gaba daya

Maza da mata har da yara kankana
Har jinjirai ma wanda sun kwana daya

Kuma har da tsofaffi da basu fita waje
Don Allah duk a fade su kar a rage daya

Domin barin wani, baya ba wani taimako
An fidda dashi acikin mutan Nijeriya

Shi bai ga tsuntsu bai ga tarko ya bace
Sai yai nadama nan cikin Nijeriya

Allah tsare mu da yin hakan, ya yan'uwa
Kuma maganin wannan a bayyana gaskiya

Kuyi tir da masu batun na banza kun jiyya
Makiya jiharmu, munafukanta Arewaci Nijeriya

Har ma suna cewa haraj za'a sa
Domin su wargazar da shirin ta areriya

Kuma don a danne tattalinmu na arziki
Har ma a danne komi nan arewa mu sha wuya

Ba'a kidaya kan haraji kun sani
Yara da mata ba'a sa musu kun jiya

Haka ma a zozzowa da tsofaffi duka
Suma haraji ba'a sa musu kun jiya

Wannan kidaya dai nufinta daban yake
Nan dai asan jimlar mutan Nijeriya

Kuma don a san adadin mutanen jihhunan
Jihar da tafi yawa cikin Nijeriya

In an rabo ita zata samu mafi yawa
Ninkin ba ninkin za'a bata kunjiya

Kan duk ku da ayyukan gona duka
Kuma asibitoci makarantu kun jiya

To zasu samu rabo mafi girma duka
To kadda mu cuci jiharmu nan ta arewiya

Duk wanda ycce ma haraji za'a sa
Ce mai haraji arziki ne ka jiya

Mara lafiya da mahaukata basa biya
ashe haraji lafiya ne kun jiya

Sauki gareshi gun manomi kun jiya
Zakkar abinda ya aikata shi ke biya

Yan kasuwa ma sau guda ne shekara
Ma'aikata ne ba iyaka kun jiya

Dukkan wata kullum akan diba ake
Sisi ake diba a kowace fam Daya

Kai malami har malama kuyi anniya
Ku bada sunan yan uwanku gaba daya

Yaya da jikoki da dangi ba ragi
Har wanda basu gida suna wata nahiya

Dada wanda yaki shiga cikin kirga kusan
Shi zaya sha kunya cikin Nijeriya

Sannan ya zam mugu sharari jahili
Mai taimakawa don a cuci arewiya

To malaman Sansan inai muku gargadi
Dan Allah don manzo Rasulu abin biya

Kuma banda kosawa ku dau hakuri kwarai
A wajen kidaya kadda ku dinga tsamiya

Ku bi sannu-sannu a hankali ba firgita
Kuma ba tsanantawa a kowace tambaya

In ko akayi muku tambaya ta rashin sani
Ku bada amsa kadda ku kosa kun jiya

Kuyi ayyukanku da gaskiya bisa ka'ida
Acikin birane, kauyuka har tsangaya

Ahaiyye iyyenanaiyaye yurai yurai
Malam abin ga da niyyi kada kai tambaya

Na barwa Jallah wa'azu sarki mai sani
Ubangiji ya sani kafin ya darsu ga zuciya

To shugaban kirga muna ta sa ido
Muga ayyukan komi yana kan gaskiya

Don kadda azo da ka taho ayi ta gunaguni
Harma takai mu fagen a dinga hatsaniya

kuma kar ta kai ga fagen abin da-na-sani
Ita ko alama ce ta bacin zuciya

Da-na-sani keya a baya take tutur
In an fade ta ku tabbata an sha wuya

Gabas da Yamma, Tsakiya da Arewiya
Muga kan shirin komi ya zam mana bai daya

Don kada a sayar da dubu a kasa sayan daya
Har ma akai ga fagen ace ya rasa kiya

Alhamdu LilLahi ina yin godiya
Agurin Ta'ala Jallah Sarki shi daya

Tamat bi HamdilLahi waka ta tsaya
Waka a gargadinku nan mu gaba daya

a wajen bayani kada ku damu da tambaya
Yar shehu tai wanga tsari kun jiya

In an ka ce adires ku duba ba wuya
Don ni a kofar mata sai kui tambaya

Nagode Allah har Rasulu abin biya
Alai Sahabbai Tabi'ina da Auliya

Baitinta Sittin ba Biyar ba kunjiya
Na rufe da sunan wanda baya fariya

Wakar Zuwan An Nasara Kasar Hausa; Daga Sarkin Musulmi Attahiru

Shine dai Sarkin Musulmi na karshe, kafi mulkin Turawa. Ya rasu a Burmi a ran 27 ga watan July 1903, bayan sun kafsa da Turawan mulkin mallaka. Ya ki amincewa da Turawan da kuma tsare-tsaren da suka zo masa da su, a saboda haka nema ya rubuta wannan waka, domin ya fadakar da mutanensa illar zama karkashin mulkin Nasara. Hakan ya jawo bore a kasar Hausa, wanda ya sanya, turawan suka yi fito-na-fito dashi. Ganin hakanne ya sanya ya bar garin Sakkwato, inda yayi niyyar yin Hijira zuwa kasa maitsarki. Ya rasu tare da mutane da dama, kuma an kama jama'u da dama, cikinsu kuwa hadda Sarkin Kano Alu. Ga dai wakar

Gudun mutuwa da son rai aggaremu
Da kau kin kaddara abi Annasara

Ina muka yi da dama da hauni suna
Ku tashi mu sa gabanmu mu tsira tsara

Idan ka ce akwai wahala ga tashi
Lahan duka na ga masu biyan Nasara

Idan iko ka kai kak ko ki tashi
Ina iko shi kai ikon Nasara

Idan sun baka kyauta, kar ka karba
Dafi na sun ka baka guba Nasara

Suna foro garemu mu bar zalama
Mazalunta da kansu diyan Nasara

Bakar fitina garesu da kau makida
Ta bata dinin musulmi Annasara

Halin da mu kai ga yau aka bayyanawa
Dalilin ke ga an ka sako Nasara

Ku bar jin masu cewa ba'a ashi
Ina halin zama ga Annnasara

Mu mai da gabanmu Makka mu zo Madina
Madina da Makka dai ab ba Nasara

Batu na Shehu yai yi shi bashi tashi
Sa'a ta ya fade ta ta Annasara

Muna da nufa idan mun samu iko
Mu ja daga, mu kore Annasara

Idan ko sun kashe mu mu san shahada
Muje aljanna sai mu ishe makara.

Sai dai an samu sabani tsakanin masana, a gameda waye ya rubuta wannan waka. Dandatti Abdukadir ya bayyana hujjar cewa, Sarkin Musulmi Attahiru n ya rubuta ta. Amma A B Yahaya shi yana ganin wani malami ne maisuna Malam Labbo dan Mariya Kwasare ya rubutata, inda yace ya samo wannan hujja ce daga Waziri Junaidu.

Saturday, April 7, 2007

Wakar Buhari; Daga Wazirin Sakkwato Buhari 1903

Wannan wakar an rubutata ne a lokacin da Daular Usmaniya ta Sakkwato ta shiga cikin wani halin kaka-ni-kayi. A lokacin da Turawan mulki suka tasarwa Daular haikan! Daga kudancin Daular, ga kuma Rabih daga bangaren Gabas, sa'annan ga kuma yake yake acikin daular, tsakanin Tukurawa da Yusufawa a Kano, da kuma wasu sassa na daular. Marubucin dai shine shahararran Wazirin nan na Sakkwato, wato Waziri Buhari dan Gidado, wanda jika ne ga Sarkin Musulmi Muhammadu Bello. Ya nuna takaicinsa game da yadda abubuwa suka tarwatsewa Daular ta fulani, da kuma yadda ya gaza wajen sulhuntawa tsakanin Sarkin Kano Tukur da Yan'uwansa, wanda hakan yayi sanadiyyar Yakin Basasar Kano. Hakan nema ya jawo ya rasa idonsa. Ya dai rayu, har zamanin da turawa suka ci Sakkwato, ya rasu a farkon karni na 20.
Ga dai wakar tasa;

Jama'a da ku ni ke kun ji aqrani
Tsoho da sabubba, dud da yan sabyani
Ku zan fadama na nesa hal jirani
Na tsorata, tsoro mai yawa ikhwani
Ga abubuwanga da niggani ashjani

In kun bideni ku tambaya mi ag garan
Halin da ajjiya yau dabam ya firgitan
Shagala zaman ashraru ya shiga sai kadan
Kowa da kowa yau ya rage sai kadan
Wannan abin ya tsoratani

Ga abinda nijji da nig gani bisa kowane
Abu na cikinmu ku dubi iko ya dune
Ban san shi da wuri waliyya tab bayyane
Tsoronga Maryamu taggani har tat tuni
ajban li dhalika minka aw ajbani

Kaitonmu ya jama'a ku tashi mu fifika
Ga abinda sun kayi ko kadanne mu taimaka
Bisa gwargwadanmu ku dubi sa'a ta cika
umara'una, ulama'una sun sam tuqa
Sulaha'una, shuhada'una naji bayani

Amma in da zato raina nai tuni
Shibka abinda ka turbuda shi kan gani
Bari firgita don juge-jugen zamani
Baka gadi tsoro gunmu hakkan ka sani
Ko mumini mai quwwatu lil imani

Tunda randa kas san wanda yaika mai sama
Samo rashi, khairan da Sharran ya gama
Bamai ije maka dai cikinsu, tsaya ruma
Komi taho maka hankuri zaka yi zama
Ka wakkalawa ubangiji Rahmani

Kai dan'uwa na so ka lura ka rarrabe
Ga abinda yaffi gareka don ka fice kure
Rike gaskiya ka santa me kake lalube
Inda kasan tuba kakan rike gwadabe
Daba kaji tsoro ba don hidhyani

Kullum ina jin wa'azi inda shuyukina
Nazo karatu naji gun ulama'una
Subhana, kin ji yai yawa don son ghina
Madalla Maryamu kin tuna min na tuna
Can da wuri na zauna cin nasyani

Na kasa farga yau da gobe suna zuwa
Ga mutum shi kasa abinda yayi cikin fa wa
Karfi shi kau da gani, shi kau sha mantuwa
Na kasa tuba ga zunubbai sun yawa
Kuma ga shuyukhi ga halin sibyani

Na roki Allah Jalla shi ka isam mini
Ga abinda yas same ni shi ka biya mini
Ga abinda nis so zahiri in badini
Na tuba ya Allahu gafarta mini
Don Shehu nurin zamanin Usmanu

Tun nan da barzakhu lahira a shi taimaka
Aikin da niyyi na gaskiya shi biya garan
Shi hana ni muggun yalla ko da nufa kadan
Astagfurullaha l' azima shi agazan
Don shehu Abdulqadir Jilani

Domin Rufa'i ubangiji ka raba mana
Rokon da nai maka don badai ka isan mana
Haka na Dasuki gare su nan muka dangana
Da zaman kushewa har kiyama Rabbana
Amsar Takardu agazan Mannanu

Kogi; Daga Limamin Daura Usman 1899

Wannan Waka dai an rubuta ta ne a daidai lokacin da Turawa suka shigo Arewacin Nijeriya. Limamin Daura Usman ne ya rubutata, domin yayi kira ga Sarakunan Kasar Daura, dasu daina zalunci, ya kuma nusar da talakawan kasar illar zalunci. A dalilin rubuta wakar, sarakunan Fulanin Daura suka kore shi, inda ya tsere zuwa Sakkwato, a daidai lokacin da Turawa suka koro Sarkin Musulmi Attahiru. Ana kyautata zaton, ya mutu aBurmi tare da Sarkin Musulmi Attahiru. Ga dai wakar;

Kusan zulmu zulmatun ne a yaum al qiyamati
Fada ta rasulillahi manzo muhammada

Ku shimfida adalci gabas, duk da Yamma da
Kudu da Arewa, du ga ummar Muhammada

Ina Dogarai har Jeka fada da kwarakwarai
Da mata na fada, ku zo ku saurara fa'ida

Kaza yan lifidda, har da yan bindiga duka
Zagage ku saurara har ku samo fa fa'ida

Kaza yan baraya harda yan garkuwa duka
Da yan figini du da mai so yasan fa'ida

Fa kai kuwa wawa dai na wauta cikin gari
Ka dawo ga hanya kasan rahamar Ahmada

Fa ku kuwa yan sarki ku bar bin garuruwa
kuna kwace amfanin mutane mufassada

Kuna yin Kilisa don leka gidaddaje
Kuna gane matanmu kuna sabawa Muhammada

Fa ku kau talakawa fakirai ku zam ku ji
Saraki na sarki ne, Talakka na rabbana

Ina masu sanya ruwa a nono su sai
A kaisu sa'ira gobe nesa ga Ahmada

Wadansu su sa gawasa da kaya su garwaya
Fa domin su sai da guba, su sabi Muhammada

Wadansu dafare su kan sa su garwaya
Su sai she si don basu kamnar Muhammada

Wadansu da yan kuka su barka su garwaya
Suna shan azaba, gobe nesa ga Ahmada

Wadansu suna sanya ruwa su kara da kankani
Abin na haramun ne na nesa ga Ahmada

Ana masu kanwa? to ku saurara nan fadin
Ku tuba ga algushu, na nesa ga Ahmada

Su dibo fara toka su kawo su garwaya
Su saishe to domin basu kamnar Muhammada