Bagadada suna ajabi nasa
Don sun ga irin himma tasa
Suka ce kai wannan ya isa
Har yanzu suna Allah yasa
Su ga Alhaji malam Nasiru
Qadiriyya yai zurfi ciki
Darajarta kwarai yai arziki
Jama'a da yawa duk sun saki
Hairi a gare shi daki-daki
Kuma ga takawa gun Nasiru
Shi gwarz ne mai kokari
Mai kamala mai kyawon shiri
Ga mutunci gashi da hankuri
Ko ina an san shi gari-gari
Kwarjini sai Malam Nasiru
Barka da zuwa Turakar Sha'irai (Hausa Poets Blogspot). An bude wannan Turakar ranar 23 ga Maris 2007 domin yad'a rubutattun wak'ok'in mawak'an Hausa (amma Sha'iran Najeriya, domin ba mu da masaniya game da sha'iran Jamhuriyar Nijar). Muna bukatar ta'aliki da gyara a kan abubuwan da aka gani a wannan Turakar. Allah Ya ba mu sa'a, Amin.
Monday, April 16, 2007
RASHA Abokan Fita Kunya; Daga Mudi Spikin
Wannan waka ta jawowa Malam Mudi dauri a gidan yari. Domin a fahimtar Turawan Mulki wannan wani sako ne da kan iya tunzura talakawa suyi bore, kuma kan iya jefa kasa cikin juyin-juya hali irin na Kwaminisanci. Mudi Spikin ya rubuta wannan waka a 1948. Ga dai wakar
Ya yan'uwa ku zo don ku ji ni
Zan wo bayani akan Rusiya
Gama Ingilishi fa sun tashi haikan
Suka suke yi akan Rusiya
Da babbata hanyarsu don kar a so su
Don kar su zo nan mutan Rusiya
Shine nake so in wo dan bayani
Domin ku gane kasar Rusiya
Kasa ce ta kirki da himma garesu
Da kaunar mutane kasar Rusiya
Wakilinsu Malik sunansa ke nan
Sunan musulmi da ba fariya
Ni dai ace yau zan samu iko
Ni sai in koma kasar Rusiya
Kamar na iya tsunts inje can in Zauna
Idan na tuno su mutan Rusiya
Girmama kowa dabi'arsu ce
Ibada kamar Hajji sai Rusiya
Da son musulunci da bayar da zakka
Yawan azumi sai kasar Rusiya
Kwalta na banza damu bamu samu
Da kafur akeyi acan Rusiya
Da banki na rance idan har kana so
Ko fam Dubu Goma baki daya
Musaki acan sai ya zauna da Gwamna
Wajen shawara babu kin gaskiya
Sa'annan da sauran abubba na kirki
Suna da yawa a kasar Rusiya
Gidaje dubu Goma ne don Musakai
A yau su kasar wane ba ko daya
Akwai Talakawa akwai Tajirai
Kamar dai kasarmu ta Nijeriya
Anan gaba na tabbata babu shakka
Nijeriya zamu zam Rusiya
Mu zam mun fice daga gun Ingilishi
Mutanen daba sa rikon gaskiya
Sun barmu babu kudi babu gona
Babu abin yi cikin gaskiya
Sun shekaru yanzu Hamsin kasarmu
Ba taimako babu son gaskiya
Ta'ala Rahimu kadai taimakemu
Ka kawo mutan Rasha Nijeriya
Idan aka ce wa ya tsara ta waka
Ya bayyana halin mutan Rusiya
Ba zan boye suna ba ko za'a nema
Mudi spikin maso Rusiya
Gama bani tsoro na dauri hakika
Akan Rasha ma sai in bar duniya
Ya yan'uwa ku zo don ku ji ni
Zan wo bayani akan Rusiya
Gama Ingilishi fa sun tashi haikan
Suka suke yi akan Rusiya
Da babbata hanyarsu don kar a so su
Don kar su zo nan mutan Rusiya
Shine nake so in wo dan bayani
Domin ku gane kasar Rusiya
Kasa ce ta kirki da himma garesu
Da kaunar mutane kasar Rusiya
Wakilinsu Malik sunansa ke nan
Sunan musulmi da ba fariya
Ni dai ace yau zan samu iko
Ni sai in koma kasar Rusiya
Kamar na iya tsunts inje can in Zauna
Idan na tuno su mutan Rusiya
Girmama kowa dabi'arsu ce
Ibada kamar Hajji sai Rusiya
Da son musulunci da bayar da zakka
Yawan azumi sai kasar Rusiya
Kwalta na banza damu bamu samu
Da kafur akeyi acan Rusiya
Da banki na rance idan har kana so
Ko fam Dubu Goma baki daya
Musaki acan sai ya zauna da Gwamna
Wajen shawara babu kin gaskiya
Sa'annan da sauran abubba na kirki
Suna da yawa a kasar Rusiya
Gidaje dubu Goma ne don Musakai
A yau su kasar wane ba ko daya
Akwai Talakawa akwai Tajirai
Kamar dai kasarmu ta Nijeriya
Anan gaba na tabbata babu shakka
Nijeriya zamu zam Rusiya
Mu zam mun fice daga gun Ingilishi
Mutanen daba sa rikon gaskiya
Sun barmu babu kudi babu gona
Babu abin yi cikin gaskiya
Sun shekaru yanzu Hamsin kasarmu
Ba taimako babu son gaskiya
Ta'ala Rahimu kadai taimakemu
Ka kawo mutan Rasha Nijeriya
Idan aka ce wa ya tsara ta waka
Ya bayyana halin mutan Rusiya
Ba zan boye suna ba ko za'a nema
Mudi spikin maso Rusiya
Gama bani tsoro na dauri hakika
Akan Rasha ma sai in bar duniya
Karara; daga Malam Mudi Spikin
An haifi Alhaji Mudi Spikin a ran 1 ga watan Oktoba 1930, a unguwar Darma da ke birnin Kano. Yayi karatun qur'ani a hannun Malam Umaru Badamagare. Bai taba zuwa makarantar boko ba, amma duk da haka, ya zauna jarrabawa GCE Ordinary level, ta hanyar yin rijista da wata kwaleji a Ingila, acikin 1960. Ya sami illimin zamani ne a hannun abokansa na gwagwarmayar siyasa irinsu; Malam Sa'adu Zungur, Malam Aminu Kano, da kuma Alhaji Yusuf Maitama Sule. Yana cikin mutanen da suka kafa jam'iyyar kwato yancin talaka wato NEPU a 1950. Ya fara rubuta wakokinsa tun a 1948, ya fara da wakarsa ta "Rasha Abokan Tafiya", da kuma wani raddi da yayiwa malaminsa, wato malam Sa'adu Zungur maitaken "Arewa Jamhuriya Kawai".
A ya jama'a ina tashin
Ku dan ku rage yawan bacci
Ayau na zo gareku da sha
Wara don kara inganci
Mu wo himma mu tashi tsaye
Mu gyara kasa ta san yanci
Mu kawo shawara mai kyau
Mu tashi mu yaki jahilci
Rashin illimi ya sanya yau
Kasar nan ke yawan baci
Fa sai mun tsaya gyara
Na sosai babu jahilci
Sannan zamu san matsayi
Mu tsere wa wulakanci
Idan ba tattali a kasa
Hakika dole ta baci
Idan an zubda hakkin yan
Adam domin wulakanci
Idan masana kwarai an zub
Da su domin rashin yanci
Idan sharia ta zam ciniki
Ana nunnuna bambanci
Idan kuma masu aiki sun
Zamo duk babu inganci
Idan aiki ya zamto ba
Ayi, sai an ciwo hanci
Idan hairi a baki ake
Fada sharri cikin zuci
Idan da akwai yawan hassada
Da bata mutum da iskanci
Idan da akwai yawanta saki
Na aure don wulakanci
Idan ba tanadi wai duk
Wata sai anyi angwanci
Idan aure ya zam a kasa
Ana yi ne da jahilci
Idan kayan biki aka mai
Da su tamkar na dillanci
Idan ga jahilai a kasa
Na kin canji da shashanci
Idan da zama na banza, ba
Sana'a ai ta kakaci
A sa fatala gaban goshi
Da hula wai tsageranci
Ana ta musu ana karta
Ana zance na wawanci
Idan kuma ga yawan zargi
Na banza ga rashin yanci
Idan wani dan'uwa wai yayi
Samu ayi munafunci
Idan sharri ya zo a iza
Nufi dai ayi wulakanci
Idan da akwai yawan camfi
Da bori masu shashanci
Idan da akwai yawan tsegun
Guman banza na jahilci
Idan a kasa ya zam an go
Yi bayan masu lalaci
Idan mai gaskiya ya zamo
A kullum zai ga kaskanci
Idan gata ya sanya wadan
Su yin shirme da shashanci
Idan aka maida wadansu kamar
Ace bayi rashin yanci
Idan yan kasuwa suka zam
Sana'a aita hainici
Idan ga karuwai a kasa
A kullum ai ta fasicci
Idan da giya an ta
Ru kullm nuna iskanci
Idan ba tausayi a kasa
Mutane na ta makirci
Idan kuma har amana tai
Kadan sai nuna ha'inci
Idan har maluma suka bar
Sani i zuwa fagen baci
Idan bidia ta zam an gir
Gina kuma babu sassauci
Idan yaya suna sabon
Mahaifa har da kaskanci
Idan a kasa akwai wannan
Hakika dole ta baci
Fa sai in anyi aiki za
Hiri ba nuna lalaci
Sa'annan zamu san haske
Mu tserewa wulakanci
Abinda na farfadan nanYan
'Uwa da akwai muhimmanci
Fa duk gyaran wadannan na
Garemu cikin batun yanci
Mu daina abinda bashi da kyau
Mu daina biyewa jahilci.
A ya jama'a ina tashin
Ku dan ku rage yawan bacci
Ayau na zo gareku da sha
Wara don kara inganci
Mu wo himma mu tashi tsaye
Mu gyara kasa ta san yanci
Mu kawo shawara mai kyau
Mu tashi mu yaki jahilci
Rashin illimi ya sanya yau
Kasar nan ke yawan baci
Fa sai mun tsaya gyara
Na sosai babu jahilci
Sannan zamu san matsayi
Mu tsere wa wulakanci
Idan ba tattali a kasa
Hakika dole ta baci
Idan an zubda hakkin yan
Adam domin wulakanci
Idan masana kwarai an zub
Da su domin rashin yanci
Idan sharia ta zam ciniki
Ana nunnuna bambanci
Idan kuma masu aiki sun
Zamo duk babu inganci
Idan aiki ya zamto ba
Ayi, sai an ciwo hanci
Idan hairi a baki ake
Fada sharri cikin zuci
Idan da akwai yawan hassada
Da bata mutum da iskanci
Idan da akwai yawanta saki
Na aure don wulakanci
Idan ba tanadi wai duk
Wata sai anyi angwanci
Idan aure ya zam a kasa
Ana yi ne da jahilci
Idan kayan biki aka mai
Da su tamkar na dillanci
Idan ga jahilai a kasa
Na kin canji da shashanci
Idan da zama na banza, ba
Sana'a ai ta kakaci
A sa fatala gaban goshi
Da hula wai tsageranci
Ana ta musu ana karta
Ana zance na wawanci
Idan kuma ga yawan zargi
Na banza ga rashin yanci
Idan wani dan'uwa wai yayi
Samu ayi munafunci
Idan sharri ya zo a iza
Nufi dai ayi wulakanci
Idan da akwai yawan camfi
Da bori masu shashanci
Idan da akwai yawan tsegun
Guman banza na jahilci
Idan a kasa ya zam an go
Yi bayan masu lalaci
Idan mai gaskiya ya zamo
A kullum zai ga kaskanci
Idan gata ya sanya wadan
Su yin shirme da shashanci
Idan aka maida wadansu kamar
Ace bayi rashin yanci
Idan yan kasuwa suka zam
Sana'a aita hainici
Idan ga karuwai a kasa
A kullum ai ta fasicci
Idan da giya an ta
Ru kullm nuna iskanci
Idan ba tausayi a kasa
Mutane na ta makirci
Idan kuma har amana tai
Kadan sai nuna ha'inci
Idan har maluma suka bar
Sani i zuwa fagen baci
Idan bidia ta zam an gir
Gina kuma babu sassauci
Idan yaya suna sabon
Mahaifa har da kaskanci
Idan a kasa akwai wannan
Hakika dole ta baci
Fa sai in anyi aiki za
Hiri ba nuna lalaci
Sa'annan zamu san haske
Mu tserewa wulakanci
Abinda na farfadan nanYan
'Uwa da akwai muhimmanci
Fa duk gyaran wadannan na
Garemu cikin batun yanci
Mu daina abinda bashi da kyau
Mu daina biyewa jahilci.
Tuesday, April 10, 2007
Wakar Kidayar Mutanen Nijeriya 1973; Daga Hajiya Yar Shehu
An haifi Hajiya Yar Shehu a shekara 1937, a garin Dambatta. Ta halarci makarantar Yanmata dake lardin Sakkwato, bayan ta kammala karatun addini a gida. Ta fara aiki a ma'aikatar lafiya ta Kano a 1953, bayan ta koyar a makarantun Firamare. Daga bisani ta koma kamfanin jiragen sama na Kano, a matsayin mai bada hanyar Tarho, inda ta zama jami'ar kula da ma'aikata na ma'aikatar. Haka kuma member ce a shahararriyar kungiyar mawakan nan, wato Hikima Kulob. Ta dai wallafi wakoki da dama, domin fadakarwa, zaburarwa, illimantarwa, wa'azantarwa, da sauransu, wakokinta sun hada da "Waka da Bayani", Wakar Kidaya, Wakar Zamani dss. wadanda insha Allahu zamu kawo muku su, da dai-dai. Ta rubuta wannan waka, domin fadakar da mutane akan kidayar jama'a wato Census da akayi a 1973. Ga dai Wakar;
BismilLah na fara da sunan Rabbana
Allah Ta'ala Jallah Sarkin gaskiya
Kai ne Sami'un Basiru, Mai ji, Mai gani
Ka tsare mu sharrin, masu sharrin duniya
Domin Muhammadu shugaban duka duniya
Har lahira ma, in ka bashi gaba daya
Don Annabawa har Sahabbai Mursalai
Har dukka dangogin Rasulu abin biya
Kayi taimako agareni kai min kangiya
Kai ne katanga wadda bata zagaya
To zanyi tsari dan Kidaya ne yankuna
Ta Arewa harma duk kasarmu gaba daya
Allah Hakimu hikimarka da ta isa
Kasa mu gane don mu bayyana gaskiya
Don kada mu fada ayyukan shibcin gizo
Da ya kasa dauka, sai ya karo kungiya
Ga gargadina gun sarakai malamai
Lalle ku dage don ku kange areriya
Komai idanu bakuna har kunnuwa
Komai ya baci wuyanku ne zai rataya
Ko Shehu Fodiye ku yaba tuta tasa
Har ma amanar dogare gaba daya
Domin hakan nan sai ku tashi ku taimaka
Akan kidayar na jihannunmu gaba daya
Don kadda a kwaso kyankyaso da su kwarkwata
a zazzage mana nan Arewa mu sha wuya
Allah jikansu na baya manya sun wuce
Giwa saka kawo ban Arewa gaba daya
Dan kadda mu ji ta kururuwa rashe idon kuma
Har ma da makirci na mai kin gaskiya
Kuma kadda jahilci ya sa sarkacen tasa
Ya ja kafa kuma har wuyanmu gaba daya
In anka zo kirga ya tabbata mun zaka
Mun bayyana musu dangunanmu gaba daya
Maza da mata har da yara kankana
Har jinjirai ma wanda sun kwana daya
Kuma har da tsofaffi da basu fita waje
Don Allah duk a fade su kar a rage daya
Domin barin wani, baya ba wani taimako
An fidda dashi acikin mutan Nijeriya
Shi bai ga tsuntsu bai ga tarko ya bace
Sai yai nadama nan cikin Nijeriya
Allah tsare mu da yin hakan, ya yan'uwa
Kuma maganin wannan a bayyana gaskiya
Kuyi tir da masu batun na banza kun jiyya
Makiya jiharmu, munafukanta Arewaci Nijeriya
Har ma suna cewa haraj za'a sa
Domin su wargazar da shirin ta areriya
Kuma don a danne tattalinmu na arziki
Har ma a danne komi nan arewa mu sha wuya
Ba'a kidaya kan haraji kun sani
Yara da mata ba'a sa musu kun jiya
Haka ma a zozzowa da tsofaffi duka
Suma haraji ba'a sa musu kun jiya
Wannan kidaya dai nufinta daban yake
Nan dai asan jimlar mutan Nijeriya
Kuma don a san adadin mutanen jihhunan
Jihar da tafi yawa cikin Nijeriya
In an rabo ita zata samu mafi yawa
Ninkin ba ninkin za'a bata kunjiya
Kan duk ku da ayyukan gona duka
Kuma asibitoci makarantu kun jiya
To zasu samu rabo mafi girma duka
To kadda mu cuci jiharmu nan ta arewiya
Duk wanda ycce ma haraji za'a sa
Ce mai haraji arziki ne ka jiya
Mara lafiya da mahaukata basa biya
ashe haraji lafiya ne kun jiya
Sauki gareshi gun manomi kun jiya
Zakkar abinda ya aikata shi ke biya
Yan kasuwa ma sau guda ne shekara
Ma'aikata ne ba iyaka kun jiya
Dukkan wata kullum akan diba ake
Sisi ake diba a kowace fam Daya
Kai malami har malama kuyi anniya
Ku bada sunan yan uwanku gaba daya
Yaya da jikoki da dangi ba ragi
Har wanda basu gida suna wata nahiya
Dada wanda yaki shiga cikin kirga kusan
Shi zaya sha kunya cikin Nijeriya
Sannan ya zam mugu sharari jahili
Mai taimakawa don a cuci arewiya
To malaman Sansan inai muku gargadi
Dan Allah don manzo Rasulu abin biya
Kuma banda kosawa ku dau hakuri kwarai
A wajen kidaya kadda ku dinga tsamiya
Ku bi sannu-sannu a hankali ba firgita
Kuma ba tsanantawa a kowace tambaya
In ko akayi muku tambaya ta rashin sani
Ku bada amsa kadda ku kosa kun jiya
Kuyi ayyukanku da gaskiya bisa ka'ida
Acikin birane, kauyuka har tsangaya
Ahaiyye iyyenanaiyaye yurai yurai
Malam abin ga da niyyi kada kai tambaya
Na barwa Jallah wa'azu sarki mai sani
Ubangiji ya sani kafin ya darsu ga zuciya
To shugaban kirga muna ta sa ido
Muga ayyukan komi yana kan gaskiya
Don kadda azo da ka taho ayi ta gunaguni
Harma takai mu fagen a dinga hatsaniya
kuma kar ta kai ga fagen abin da-na-sani
Ita ko alama ce ta bacin zuciya
Da-na-sani keya a baya take tutur
In an fade ta ku tabbata an sha wuya
Gabas da Yamma, Tsakiya da Arewiya
Muga kan shirin komi ya zam mana bai daya
Don kada a sayar da dubu a kasa sayan daya
Har ma akai ga fagen ace ya rasa kiya
Alhamdu LilLahi ina yin godiya
Agurin Ta'ala Jallah Sarki shi daya
Tamat bi HamdilLahi waka ta tsaya
Waka a gargadinku nan mu gaba daya
a wajen bayani kada ku damu da tambaya
Yar shehu tai wanga tsari kun jiya
In an ka ce adires ku duba ba wuya
Don ni a kofar mata sai kui tambaya
Nagode Allah har Rasulu abin biya
Alai Sahabbai Tabi'ina da Auliya
Baitinta Sittin ba Biyar ba kunjiya
Na rufe da sunan wanda baya fariya
BismilLah na fara da sunan Rabbana
Allah Ta'ala Jallah Sarkin gaskiya
Kai ne Sami'un Basiru, Mai ji, Mai gani
Ka tsare mu sharrin, masu sharrin duniya
Domin Muhammadu shugaban duka duniya
Har lahira ma, in ka bashi gaba daya
Don Annabawa har Sahabbai Mursalai
Har dukka dangogin Rasulu abin biya
Kayi taimako agareni kai min kangiya
Kai ne katanga wadda bata zagaya
To zanyi tsari dan Kidaya ne yankuna
Ta Arewa harma duk kasarmu gaba daya
Allah Hakimu hikimarka da ta isa
Kasa mu gane don mu bayyana gaskiya
Don kada mu fada ayyukan shibcin gizo
Da ya kasa dauka, sai ya karo kungiya
Ga gargadina gun sarakai malamai
Lalle ku dage don ku kange areriya
Komai idanu bakuna har kunnuwa
Komai ya baci wuyanku ne zai rataya
Ko Shehu Fodiye ku yaba tuta tasa
Har ma amanar dogare gaba daya
Domin hakan nan sai ku tashi ku taimaka
Akan kidayar na jihannunmu gaba daya
Don kadda a kwaso kyankyaso da su kwarkwata
a zazzage mana nan Arewa mu sha wuya
Allah jikansu na baya manya sun wuce
Giwa saka kawo ban Arewa gaba daya
Dan kadda mu ji ta kururuwa rashe idon kuma
Har ma da makirci na mai kin gaskiya
Kuma kadda jahilci ya sa sarkacen tasa
Ya ja kafa kuma har wuyanmu gaba daya
In anka zo kirga ya tabbata mun zaka
Mun bayyana musu dangunanmu gaba daya
Maza da mata har da yara kankana
Har jinjirai ma wanda sun kwana daya
Kuma har da tsofaffi da basu fita waje
Don Allah duk a fade su kar a rage daya
Domin barin wani, baya ba wani taimako
An fidda dashi acikin mutan Nijeriya
Shi bai ga tsuntsu bai ga tarko ya bace
Sai yai nadama nan cikin Nijeriya
Allah tsare mu da yin hakan, ya yan'uwa
Kuma maganin wannan a bayyana gaskiya
Kuyi tir da masu batun na banza kun jiyya
Makiya jiharmu, munafukanta Arewaci Nijeriya
Har ma suna cewa haraj za'a sa
Domin su wargazar da shirin ta areriya
Kuma don a danne tattalinmu na arziki
Har ma a danne komi nan arewa mu sha wuya
Ba'a kidaya kan haraji kun sani
Yara da mata ba'a sa musu kun jiya
Haka ma a zozzowa da tsofaffi duka
Suma haraji ba'a sa musu kun jiya
Wannan kidaya dai nufinta daban yake
Nan dai asan jimlar mutan Nijeriya
Kuma don a san adadin mutanen jihhunan
Jihar da tafi yawa cikin Nijeriya
In an rabo ita zata samu mafi yawa
Ninkin ba ninkin za'a bata kunjiya
Kan duk ku da ayyukan gona duka
Kuma asibitoci makarantu kun jiya
To zasu samu rabo mafi girma duka
To kadda mu cuci jiharmu nan ta arewiya
Duk wanda ycce ma haraji za'a sa
Ce mai haraji arziki ne ka jiya
Mara lafiya da mahaukata basa biya
ashe haraji lafiya ne kun jiya
Sauki gareshi gun manomi kun jiya
Zakkar abinda ya aikata shi ke biya
Yan kasuwa ma sau guda ne shekara
Ma'aikata ne ba iyaka kun jiya
Dukkan wata kullum akan diba ake
Sisi ake diba a kowace fam Daya
Kai malami har malama kuyi anniya
Ku bada sunan yan uwanku gaba daya
Yaya da jikoki da dangi ba ragi
Har wanda basu gida suna wata nahiya
Dada wanda yaki shiga cikin kirga kusan
Shi zaya sha kunya cikin Nijeriya
Sannan ya zam mugu sharari jahili
Mai taimakawa don a cuci arewiya
To malaman Sansan inai muku gargadi
Dan Allah don manzo Rasulu abin biya
Kuma banda kosawa ku dau hakuri kwarai
A wajen kidaya kadda ku dinga tsamiya
Ku bi sannu-sannu a hankali ba firgita
Kuma ba tsanantawa a kowace tambaya
In ko akayi muku tambaya ta rashin sani
Ku bada amsa kadda ku kosa kun jiya
Kuyi ayyukanku da gaskiya bisa ka'ida
Acikin birane, kauyuka har tsangaya
Ahaiyye iyyenanaiyaye yurai yurai
Malam abin ga da niyyi kada kai tambaya
Na barwa Jallah wa'azu sarki mai sani
Ubangiji ya sani kafin ya darsu ga zuciya
To shugaban kirga muna ta sa ido
Muga ayyukan komi yana kan gaskiya
Don kadda azo da ka taho ayi ta gunaguni
Harma takai mu fagen a dinga hatsaniya
kuma kar ta kai ga fagen abin da-na-sani
Ita ko alama ce ta bacin zuciya
Da-na-sani keya a baya take tutur
In an fade ta ku tabbata an sha wuya
Gabas da Yamma, Tsakiya da Arewiya
Muga kan shirin komi ya zam mana bai daya
Don kada a sayar da dubu a kasa sayan daya
Har ma akai ga fagen ace ya rasa kiya
Alhamdu LilLahi ina yin godiya
Agurin Ta'ala Jallah Sarki shi daya
Tamat bi HamdilLahi waka ta tsaya
Waka a gargadinku nan mu gaba daya
a wajen bayani kada ku damu da tambaya
Yar shehu tai wanga tsari kun jiya
In an ka ce adires ku duba ba wuya
Don ni a kofar mata sai kui tambaya
Nagode Allah har Rasulu abin biya
Alai Sahabbai Tabi'ina da Auliya
Baitinta Sittin ba Biyar ba kunjiya
Na rufe da sunan wanda baya fariya
Wakar Zuwan An Nasara Kasar Hausa; Daga Sarkin Musulmi Attahiru
Shine dai Sarkin Musulmi na karshe, kafi mulkin Turawa. Ya rasu a Burmi a ran 27 ga watan July 1903, bayan sun kafsa da Turawan mulkin mallaka. Ya ki amincewa da Turawan da kuma tsare-tsaren da suka zo masa da su, a saboda haka nema ya rubuta wannan waka, domin ya fadakar da mutanensa illar zama karkashin mulkin Nasara. Hakan ya jawo bore a kasar Hausa, wanda ya sanya, turawan suka yi fito-na-fito dashi. Ganin hakanne ya sanya ya bar garin Sakkwato, inda yayi niyyar yin Hijira zuwa kasa maitsarki. Ya rasu tare da mutane da dama, kuma an kama jama'u da dama, cikinsu kuwa hadda Sarkin Kano Alu. Ga dai wakar
Gudun mutuwa da son rai aggaremu
Da kau kin kaddara abi Annasara
Ina muka yi da dama da hauni suna
Ku tashi mu sa gabanmu mu tsira tsara
Idan ka ce akwai wahala ga tashi
Lahan duka na ga masu biyan Nasara
Idan iko ka kai kak ko ki tashi
Ina iko shi kai ikon Nasara
Idan sun baka kyauta, kar ka karba
Dafi na sun ka baka guba Nasara
Suna foro garemu mu bar zalama
Mazalunta da kansu diyan Nasara
Bakar fitina garesu da kau makida
Ta bata dinin musulmi Annasara
Halin da mu kai ga yau aka bayyanawa
Dalilin ke ga an ka sako Nasara
Ku bar jin masu cewa ba'a ashi
Ina halin zama ga Annnasara
Mu mai da gabanmu Makka mu zo Madina
Madina da Makka dai ab ba Nasara
Batu na Shehu yai yi shi bashi tashi
Sa'a ta ya fade ta ta Annasara
Muna da nufa idan mun samu iko
Mu ja daga, mu kore Annasara
Idan ko sun kashe mu mu san shahada
Muje aljanna sai mu ishe makara.
Sai dai an samu sabani tsakanin masana, a gameda waye ya rubuta wannan waka. Dandatti Abdukadir ya bayyana hujjar cewa, Sarkin Musulmi Attahiru n ya rubuta ta. Amma A B Yahaya shi yana ganin wani malami ne maisuna Malam Labbo dan Mariya Kwasare ya rubutata, inda yace ya samo wannan hujja ce daga Waziri Junaidu.
Gudun mutuwa da son rai aggaremu
Da kau kin kaddara abi Annasara
Ina muka yi da dama da hauni suna
Ku tashi mu sa gabanmu mu tsira tsara
Idan ka ce akwai wahala ga tashi
Lahan duka na ga masu biyan Nasara
Idan iko ka kai kak ko ki tashi
Ina iko shi kai ikon Nasara
Idan sun baka kyauta, kar ka karba
Dafi na sun ka baka guba Nasara
Suna foro garemu mu bar zalama
Mazalunta da kansu diyan Nasara
Bakar fitina garesu da kau makida
Ta bata dinin musulmi Annasara
Halin da mu kai ga yau aka bayyanawa
Dalilin ke ga an ka sako Nasara
Ku bar jin masu cewa ba'a ashi
Ina halin zama ga Annnasara
Mu mai da gabanmu Makka mu zo Madina
Madina da Makka dai ab ba Nasara
Batu na Shehu yai yi shi bashi tashi
Sa'a ta ya fade ta ta Annasara
Muna da nufa idan mun samu iko
Mu ja daga, mu kore Annasara
Idan ko sun kashe mu mu san shahada
Muje aljanna sai mu ishe makara.
Sai dai an samu sabani tsakanin masana, a gameda waye ya rubuta wannan waka. Dandatti Abdukadir ya bayyana hujjar cewa, Sarkin Musulmi Attahiru n ya rubuta ta. Amma A B Yahaya shi yana ganin wani malami ne maisuna Malam Labbo dan Mariya Kwasare ya rubutata, inda yace ya samo wannan hujja ce daga Waziri Junaidu.
Saturday, April 7, 2007
Wakar Buhari; Daga Wazirin Sakkwato Buhari 1903
Wannan wakar an rubutata ne a lokacin da Daular Usmaniya ta Sakkwato ta shiga cikin wani halin kaka-ni-kayi. A lokacin da Turawan mulki suka tasarwa Daular haikan! Daga kudancin Daular, ga kuma Rabih daga bangaren Gabas, sa'annan ga kuma yake yake acikin daular, tsakanin Tukurawa da Yusufawa a Kano, da kuma wasu sassa na daular. Marubucin dai shine shahararran Wazirin nan na Sakkwato, wato Waziri Buhari dan Gidado, wanda jika ne ga Sarkin Musulmi Muhammadu Bello. Ya nuna takaicinsa game da yadda abubuwa suka tarwatsewa Daular ta fulani, da kuma yadda ya gaza wajen sulhuntawa tsakanin Sarkin Kano Tukur da Yan'uwansa, wanda hakan yayi sanadiyyar Yakin Basasar Kano. Hakan nema ya jawo ya rasa idonsa. Ya dai rayu, har zamanin da turawa suka ci Sakkwato, ya rasu a farkon karni na 20.
Ga dai wakar tasa;
Jama'a da ku ni ke kun ji aqrani
Tsoho da sabubba, dud da yan sabyani
Ku zan fadama na nesa hal jirani
Na tsorata, tsoro mai yawa ikhwani
Ga abubuwanga da niggani ashjani
In kun bideni ku tambaya mi ag garan
Halin da ajjiya yau dabam ya firgitan
Shagala zaman ashraru ya shiga sai kadan
Kowa da kowa yau ya rage sai kadan
Wannan abin ya tsoratani
Ga abinda nijji da nig gani bisa kowane
Abu na cikinmu ku dubi iko ya dune
Ban san shi da wuri waliyya tab bayyane
Tsoronga Maryamu taggani har tat tuni
ajban li dhalika minka aw ajbani
Kaitonmu ya jama'a ku tashi mu fifika
Ga abinda sun kayi ko kadanne mu taimaka
Bisa gwargwadanmu ku dubi sa'a ta cika
umara'una, ulama'una sun sam tuqa
Sulaha'una, shuhada'una naji bayani
Amma in da zato raina nai tuni
Shibka abinda ka turbuda shi kan gani
Bari firgita don juge-jugen zamani
Baka gadi tsoro gunmu hakkan ka sani
Ko mumini mai quwwatu lil imani
Tunda randa kas san wanda yaika mai sama
Samo rashi, khairan da Sharran ya gama
Bamai ije maka dai cikinsu, tsaya ruma
Komi taho maka hankuri zaka yi zama
Ka wakkalawa ubangiji Rahmani
Kai dan'uwa na so ka lura ka rarrabe
Ga abinda yaffi gareka don ka fice kure
Rike gaskiya ka santa me kake lalube
Inda kasan tuba kakan rike gwadabe
Daba kaji tsoro ba don hidhyani
Kullum ina jin wa'azi inda shuyukina
Nazo karatu naji gun ulama'una
Subhana, kin ji yai yawa don son ghina
Madalla Maryamu kin tuna min na tuna
Can da wuri na zauna cin nasyani
Na kasa farga yau da gobe suna zuwa
Ga mutum shi kasa abinda yayi cikin fa wa
Karfi shi kau da gani, shi kau sha mantuwa
Na kasa tuba ga zunubbai sun yawa
Kuma ga shuyukhi ga halin sibyani
Na roki Allah Jalla shi ka isam mini
Ga abinda yas same ni shi ka biya mini
Ga abinda nis so zahiri in badini
Na tuba ya Allahu gafarta mini
Don Shehu nurin zamanin Usmanu
Tun nan da barzakhu lahira a shi taimaka
Aikin da niyyi na gaskiya shi biya garan
Shi hana ni muggun yalla ko da nufa kadan
Astagfurullaha l' azima shi agazan
Don shehu Abdulqadir Jilani
Domin Rufa'i ubangiji ka raba mana
Rokon da nai maka don badai ka isan mana
Haka na Dasuki gare su nan muka dangana
Da zaman kushewa har kiyama Rabbana
Amsar Takardu agazan Mannanu
Ga dai wakar tasa;
Jama'a da ku ni ke kun ji aqrani
Tsoho da sabubba, dud da yan sabyani
Ku zan fadama na nesa hal jirani
Na tsorata, tsoro mai yawa ikhwani
Ga abubuwanga da niggani ashjani
In kun bideni ku tambaya mi ag garan
Halin da ajjiya yau dabam ya firgitan
Shagala zaman ashraru ya shiga sai kadan
Kowa da kowa yau ya rage sai kadan
Wannan abin ya tsoratani
Ga abinda nijji da nig gani bisa kowane
Abu na cikinmu ku dubi iko ya dune
Ban san shi da wuri waliyya tab bayyane
Tsoronga Maryamu taggani har tat tuni
ajban li dhalika minka aw ajbani
Kaitonmu ya jama'a ku tashi mu fifika
Ga abinda sun kayi ko kadanne mu taimaka
Bisa gwargwadanmu ku dubi sa'a ta cika
umara'una, ulama'una sun sam tuqa
Sulaha'una, shuhada'una naji bayani
Amma in da zato raina nai tuni
Shibka abinda ka turbuda shi kan gani
Bari firgita don juge-jugen zamani
Baka gadi tsoro gunmu hakkan ka sani
Ko mumini mai quwwatu lil imani
Tunda randa kas san wanda yaika mai sama
Samo rashi, khairan da Sharran ya gama
Bamai ije maka dai cikinsu, tsaya ruma
Komi taho maka hankuri zaka yi zama
Ka wakkalawa ubangiji Rahmani
Kai dan'uwa na so ka lura ka rarrabe
Ga abinda yaffi gareka don ka fice kure
Rike gaskiya ka santa me kake lalube
Inda kasan tuba kakan rike gwadabe
Daba kaji tsoro ba don hidhyani
Kullum ina jin wa'azi inda shuyukina
Nazo karatu naji gun ulama'una
Subhana, kin ji yai yawa don son ghina
Madalla Maryamu kin tuna min na tuna
Can da wuri na zauna cin nasyani
Na kasa farga yau da gobe suna zuwa
Ga mutum shi kasa abinda yayi cikin fa wa
Karfi shi kau da gani, shi kau sha mantuwa
Na kasa tuba ga zunubbai sun yawa
Kuma ga shuyukhi ga halin sibyani
Na roki Allah Jalla shi ka isam mini
Ga abinda yas same ni shi ka biya mini
Ga abinda nis so zahiri in badini
Na tuba ya Allahu gafarta mini
Don Shehu nurin zamanin Usmanu
Tun nan da barzakhu lahira a shi taimaka
Aikin da niyyi na gaskiya shi biya garan
Shi hana ni muggun yalla ko da nufa kadan
Astagfurullaha l' azima shi agazan
Don shehu Abdulqadir Jilani
Domin Rufa'i ubangiji ka raba mana
Rokon da nai maka don badai ka isan mana
Haka na Dasuki gare su nan muka dangana
Da zaman kushewa har kiyama Rabbana
Amsar Takardu agazan Mannanu
Kogi; Daga Limamin Daura Usman 1899
Wannan Waka dai an rubuta ta ne a daidai lokacin da Turawa suka shigo Arewacin Nijeriya. Limamin Daura Usman ne ya rubutata, domin yayi kira ga Sarakunan Kasar Daura, dasu daina zalunci, ya kuma nusar da talakawan kasar illar zalunci. A dalilin rubuta wakar, sarakunan Fulanin Daura suka kore shi, inda ya tsere zuwa Sakkwato, a daidai lokacin da Turawa suka koro Sarkin Musulmi Attahiru. Ana kyautata zaton, ya mutu aBurmi tare da Sarkin Musulmi Attahiru. Ga dai wakar;
Kusan zulmu zulmatun ne a yaum al qiyamati
Fada ta rasulillahi manzo muhammada
Ku shimfida adalci gabas, duk da Yamma da
Kudu da Arewa, du ga ummar Muhammada
Ina Dogarai har Jeka fada da kwarakwarai
Da mata na fada, ku zo ku saurara fa'ida
Kaza yan lifidda, har da yan bindiga duka
Zagage ku saurara har ku samo fa fa'ida
Kaza yan baraya harda yan garkuwa duka
Da yan figini du da mai so yasan fa'ida
Fa kai kuwa wawa dai na wauta cikin gari
Ka dawo ga hanya kasan rahamar Ahmada
Fa ku kuwa yan sarki ku bar bin garuruwa
kuna kwace amfanin mutane mufassada
Kuna yin Kilisa don leka gidaddaje
Kuna gane matanmu kuna sabawa Muhammada
Fa ku kau talakawa fakirai ku zam ku ji
Saraki na sarki ne, Talakka na rabbana
Ina masu sanya ruwa a nono su sai
A kaisu sa'ira gobe nesa ga Ahmada
Wadansu su sa gawasa da kaya su garwaya
Fa domin su sai da guba, su sabi Muhammada
Wadansu dafare su kan sa su garwaya
Su sai she si don basu kamnar Muhammada
Wadansu da yan kuka su barka su garwaya
Suna shan azaba, gobe nesa ga Ahmada
Wadansu suna sanya ruwa su kara da kankani
Abin na haramun ne na nesa ga Ahmada
Ana masu kanwa? to ku saurara nan fadin
Ku tuba ga algushu, na nesa ga Ahmada
Su dibo fara toka su kawo su garwaya
Su saishe to domin basu kamnar Muhammada
Kusan zulmu zulmatun ne a yaum al qiyamati
Fada ta rasulillahi manzo muhammada
Ku shimfida adalci gabas, duk da Yamma da
Kudu da Arewa, du ga ummar Muhammada
Ina Dogarai har Jeka fada da kwarakwarai
Da mata na fada, ku zo ku saurara fa'ida
Kaza yan lifidda, har da yan bindiga duka
Zagage ku saurara har ku samo fa fa'ida
Kaza yan baraya harda yan garkuwa duka
Da yan figini du da mai so yasan fa'ida
Fa kai kuwa wawa dai na wauta cikin gari
Ka dawo ga hanya kasan rahamar Ahmada
Fa ku kuwa yan sarki ku bar bin garuruwa
kuna kwace amfanin mutane mufassada
Kuna yin Kilisa don leka gidaddaje
Kuna gane matanmu kuna sabawa Muhammada
Fa ku kau talakawa fakirai ku zam ku ji
Saraki na sarki ne, Talakka na rabbana
Ina masu sanya ruwa a nono su sai
A kaisu sa'ira gobe nesa ga Ahmada
Wadansu su sa gawasa da kaya su garwaya
Fa domin su sai da guba, su sabi Muhammada
Wadansu dafare su kan sa su garwaya
Su sai she si don basu kamnar Muhammada
Wadansu da yan kuka su barka su garwaya
Suna shan azaba, gobe nesa ga Ahmada
Wadansu suna sanya ruwa su kara da kankani
Abin na haramun ne na nesa ga Ahmada
Ana masu kanwa? to ku saurara nan fadin
Ku tuba ga algushu, na nesa ga Ahmada
Su dibo fara toka su kawo su garwaya
Su saishe to domin basu kamnar Muhammada
Subscribe to:
Posts (Atom)