Barka da zuwa Turakar Sha'irai (Hausa Poets Blogspot). An bude wannan Turakar ranar 23 ga Maris 2007 domin yad'a rubutattun wak'ok'in mawak'an Hausa (amma Sha'iran Najeriya, domin ba mu da masaniya game da sha'iran Jamhuriyar Nijar). Muna bukatar ta'aliki da gyara a kan abubuwan da aka gani a wannan Turakar. Allah Ya ba mu sa'a, Amin.
Saturday, December 8, 2012
wakar Begen Muhammadu Daga Malam Nasiru Kabara
wannan waka ce da marigayi Malam Nasiru Kabara ya rubutu, domin nuna tsantsar kaunarsa ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wassallam.
Wakar Begen Muhammad ta Malam Nasiru Kabara
Bismillahir Rahmanir al Rahim
Wa sallalLahu ala nabiyul karim
1. Begen Muhammadu ya cika mani zuciya
acikinta ba sauran muhalli ko daya.
2. Wallahi garwashin bidar sado da shi
ya kona sassan zuciya wayyoniya
3. Naso ka Daha kamar ido ga makauniya
naso inje ni gareka koda sau daya
4. Naso ziyara gani bani da fiffike
kaka nake na gano masoyin zuciya
5. Na so ka son mai wabiya da ta so diya
ko ko maridhi yadda yaso lafiya.
6. Ko san abincin nan ga wanda ya yunwata
ko ko ruwa ga maji kishi zai sha wuya.
7. Mukhtari ka tafi ban gane ka a duniya
kona rabauta inga ko gun kwanciya
8. Acikin mafarki in na samu sai ince
“Allahu Akbar uh uhum wayyo niyya”
9. Begenka ya konan kasha har jijiya
Naman jikina ya zangwanye bai daya
10. Ya kona hanta har da hanjaijai duka
Ya bar hawayen zuciya da idaniya
11. Kaunarka ta kone bukatar zuciya
Duk babu sauran ma bukatar duniya
12. Inma akwai sauran bukatar zuciya
sai ko ganinka da yamma ko ko safiya
13. Ta yada zancen duniya tatsuniya
ta dauki amri wanda ya zam gaskiya.
15. Ta yada zancen zo mu ji ta dake fadi
ta kalmashe gizo ta hana masa kokiya
16. Duk zuciyar da ta so ka Daha da gaskiya
wallahi ta arzurta ba sauran tsiya
17. Tai sutura, ta tufata aluni bam-da-bam
labudda tai shaani irin na hawainiya
18. Wata safiya yayi murmushi wata safiya
Riga fara, wata ran ya sanyo shudiya.
19. Wata ran da alkyabba fara, wata ran kuwa
ya fashe da kuka nai kamar dan saniya .
20. Kaka ni kai da gani cikin nan duniya
wa zani kara gunsa ni wayyo niya
21. Ko nayi kara babu mai ji ko ya zam
kukan amale nake, ace ko jiniya
22. Mukhtaru ka faku ga gani nasa yai wuya
balle ince masa Daha ni na sha wuya
23. Shine abin kara gareshi gani nasa
ya zam kamar koyin farar hankakiya
24. Dan san ganinsa yana da yar farkar wuya
na dauki jure so ina ta dawainiya
25. In babu wanda nake da shi zai taimaka
na sauke kayan zo taya min dauriya
26. Ni dai ganin Makka a bukatar zuciya
inje ni can in samu saukin zuciya
27. Inje mahaifatai in san guri inje
insha ruwan zamzam inai wata gewaya
28. Inje Safa, inje ni Marwa in dawaya
inje musallai, in ziyarci mazan jiya
29. Sannan in dawo in dawafin salama
bayan makaman nan da Daha ya tsaitsaya
30. In wo hajjina kamila in masgaya
ni dai nufina gun mazajan gaskiya
31. Koda ina yan rarrafe in ja jiki
inje Madina garin Habibi Anbiya
32. Inje ni raudhar nan ta Daha in sunkuya
in gaisuwa, in dada da safe in dawaya
33. Ya Rabbi domin Anbiya’I da Auliya
Domin sahabban wanda ya cika duniya
34. Ka bani iko nai ziyarar Anbiya’a
dan Kudubu, dan Gausu, domin anbiya
35. A Ka saukake hanyar zuwanmu Idaibatu
Dan Mujtabai, dan Ni’ima domin Ma’iya
36.Kai agajinka A Rabbu dubi idaniya
Domin Tijjani al Khudubu mai Tijjaniya
37. Dan gimbiya tasa na kira ka A Rabbana
Ka jikan masoyan Daha, rana da safiya
38. Ganar dani Mukhtari Daha Alaniya
Domin ya kore min shuunin Duniya
39. Dauke hijabi Rabbana in gane shi fai
nan duniya ya rabbi ko a manamiya
40. Rahmarka ta gama kowanne balle niya
da na dauka karata ilaika Ilahiya
41. Ya Rabbi nai kara gareka fa kai daya
bayanka waye zaya amsa du’a’I’ya.
42. Ka yi wo salati ga Daha kai Taslimiya
a gareshi ya Rabbil wara, ya Bariya
43. Duk sanda mai bege yace ‘kul’ safiya
sallu ala Mukhtaru koda sau daya
44. Aufan zuwa Tashdiri fi takmilihi
Begen Muhammadu ya cika min zuciya
Thursday, March 12, 2009
Me Zan Fada Ne? Daga Sulaiman I Jahun
Ita wannan waka malam Sulaiman I Jahun ne ya rubutawa wata budurwarsa, a lokacin da suke karatu a jamiár Bayero ta Kano. Bai dai nuna lokacin da yayi ta, bai kuma nuna ko wacece yake yiwa wakar ba. Ga dai wakar.
1] Me zan fada ne wanda zai gamsar da ni
Na sifanta kyanki gami da halayenki.
2] Kyawo na mata dai kina da guda Dubu
Ga jiki da hali ba irin mai naki.
3] Kirar jikinki takan saka ai zautuwa
Kana irin dadin karin bakinki.
4] Lafazi da taushi, kana gashi a kammale
Wallahi ban gajiya da saurarenki.
5] Taushin jikinki kamar dadai ba ko kashi
Kamshi da santsi ba kamar labbanki.
6] Ruwan idonki idan mukai kallo biyu
Sai in kamar in nutse in debi na wanki.
7] Haskensa yafi wata daren sallah fari
Gashin girarsa kamar ciyawar tafki.
8] Abin kamar kullum kina sa tozali
Don kyalkyalin manyan idanun naki.
9] Gashinki ga santsi, abin kuma ga tsawo
Sannan wuluk! da baki, bakin hankaki.
10] Naso in sa kaina ciki inyi lif! da ni
In dunga numfashi ina shafarki.
11] Ki kadan ido in gano fari, in gano baki
Ki kadan, ki tsinkan yau da alámarinki.
12] Goshinki wani Zara yar mowar wata
Haskensa ya wuce alfijir goshinki.
13] Zancen dabiá ko a birnin Sakkwato
Aka reni ya, halinta bai kai naki.
1] Me zan fada ne wanda zai gamsar da ni
Na sifanta kyanki gami da halayenki.
2] Kyawo na mata dai kina da guda Dubu
Ga jiki da hali ba irin mai naki.
3] Kirar jikinki takan saka ai zautuwa
Kana irin dadin karin bakinki.
4] Lafazi da taushi, kana gashi a kammale
Wallahi ban gajiya da saurarenki.
5] Taushin jikinki kamar dadai ba ko kashi
Kamshi da santsi ba kamar labbanki.
6] Ruwan idonki idan mukai kallo biyu
Sai in kamar in nutse in debi na wanki.
7] Haskensa yafi wata daren sallah fari
Gashin girarsa kamar ciyawar tafki.
8] Abin kamar kullum kina sa tozali
Don kyalkyalin manyan idanun naki.
9] Gashinki ga santsi, abin kuma ga tsawo
Sannan wuluk! da baki, bakin hankaki.
10] Naso in sa kaina ciki inyi lif! da ni
In dunga numfashi ina shafarki.
11] Ki kadan ido in gano fari, in gano baki
Ki kadan, ki tsinkan yau da alámarinki.
12] Goshinki wani Zara yar mowar wata
Haskensa ya wuce alfijir goshinki.
13] Zancen dabiá ko a birnin Sakkwato
Aka reni ya, halinta bai kai naki.
Bege Daga Farfesa Bello Salim
Ban taba buga wakokin soyayya ba a wannan zauren, wannan ya faru ne saboda rashin samunsu akan lokaci, to cikin yadda Allah nayi saá na samu littafin Farfesa Bello Saíd, maisuna DAUSAYIN SOYAYYA. Wanda cike yake da wakokin soyayya. Acikin littafin ne na tsakuro muku wannan waka, da Farfesa Bello Salim ya taba rubutawa wata budurwarsa, tun cikin watan Maris na 1977. Wato kusan shekaru talatin da biyu kenan. Bai dai bayyana wa yayiwa wannan waka ba, to amma ya fito da tsintsar soyayyarsa ga wannan baiwar Allah. Ga dai wakar nan.
1] Kin tambayan wai shin me yakan dame ni ne?
Kullum ina zugurum gaban hotonki.
2] Kullum in zauna sai tunani barkatai
Magana kadan sai na kira sunanki.
3] To zo ki zauna zan gaya miki gaskiya
Domin kisan ni bani son in rufe ki.
4] Zan tambayeki ki zayyana mini zahiri
Kin san sifa ta jiki da halayenki.
5] Ko kin sani saurari nawa batu ki san
Nine madubin gane siffofinki
6] Idanuwana sun zamo taga gaman
Ta cikinsu zaki gano irin kirarki.
7] Zan dan bayanin kanki, fuska har wuya
Gangar jiki, ya zuwa ga yan yatsunki.
8] Zan fayyace siffar jikinki gaba daya
In na gama in hado da halayenki.
9] Yawa da santsi, ga tsawo kuma ga baki
Sheki, suna nan duk a gashin kanki.
10] Kuma dubi gashi naki mai daukar ido
Tamkar gilashin nan dake hannuna.
11] Idanuwanki suna sihirtar dan Adam
SEXY Bature kan canewa idonki.
12] Duk wanda yai arba dake ya ganesu to
Sai zuciya tasa ta taállaka gun ki.
13] Hanci da kunne sunyi das! sun zaunu ras!
Kowa ya gansu ko dole yai shaáwarki.
14] Godewa Allah Jallah Sarki Rahimi
Don mustadaá ne gama bakinki.
15] Wuyan barewa shi mukan ce na da kyau
To ai barewace ta kwaikwayi naki
16] Sauko kadan don ki nazar ki yi bincike
Niíma ta Allah wadda ke kirjinki
17] Cikinki shafaffe abin shaáwa kamar
A ce hatsi baya shiga hanjinki
18] Kuturinki zaunanne gwanintar haliku
Shima kawai yasa mutum begenki
19] Cinya da sharaba sumul sun mulmulu
Yannan ki gode Jallah wanda yayi ki.
20] Taka a sannu sarauniya kiyi rangwada
Dan kyan dake sawunki har yatsunki.
21] Zan bar batun kirar jiki zan dakata
Don banda kalmomin siffanta jikinki.
22] Sai dai in gode Jallah sarki Wahidun
Da ya ban idanu har na samu ganinki.
23] A takaice yanzu ki dakata kuma kiy kawai
Saurari sharhina ga halayenki.
24] Hakuri a gunki da hankali kuma ga natso
Tamkar ace mata su zo Kwas gunki.
25] Saurin fushi, tsiwa, fada ko yaudara
Ba ko guda a wajenki gandun kirki.
26] Wadanga siffofi da nai zance bisa
Su sunka sa kullum nake begenki.
27] A ina kike jin zaá san mace kamila
Mai kyan sifa, sannan da halin kirki?
28] Ko an nutsa, an bincika, an rairaye
Sai anyi saá zaá san tamkarki.
29] To shi yasa abadan a kullum safiya
Ni banda tasirin da ya wuce naki.
30] Kuma godiya kullum nake gun Rabbana
Sarkin da yai ikon in ganki, in soki.
31] Kana inyo roko garai Shi mai duka
Yasa ki kaunaci Bello da mai sonki.
1] Kin tambayan wai shin me yakan dame ni ne?
Kullum ina zugurum gaban hotonki.
2] Kullum in zauna sai tunani barkatai
Magana kadan sai na kira sunanki.
3] To zo ki zauna zan gaya miki gaskiya
Domin kisan ni bani son in rufe ki.
4] Zan tambayeki ki zayyana mini zahiri
Kin san sifa ta jiki da halayenki.
5] Ko kin sani saurari nawa batu ki san
Nine madubin gane siffofinki
6] Idanuwana sun zamo taga gaman
Ta cikinsu zaki gano irin kirarki.
7] Zan dan bayanin kanki, fuska har wuya
Gangar jiki, ya zuwa ga yan yatsunki.
8] Zan fayyace siffar jikinki gaba daya
In na gama in hado da halayenki.
9] Yawa da santsi, ga tsawo kuma ga baki
Sheki, suna nan duk a gashin kanki.
10] Kuma dubi gashi naki mai daukar ido
Tamkar gilashin nan dake hannuna.
11] Idanuwanki suna sihirtar dan Adam
SEXY Bature kan canewa idonki.
12] Duk wanda yai arba dake ya ganesu to
Sai zuciya tasa ta taállaka gun ki.
13] Hanci da kunne sunyi das! sun zaunu ras!
Kowa ya gansu ko dole yai shaáwarki.
14] Godewa Allah Jallah Sarki Rahimi
Don mustadaá ne gama bakinki.
15] Wuyan barewa shi mukan ce na da kyau
To ai barewace ta kwaikwayi naki
16] Sauko kadan don ki nazar ki yi bincike
Niíma ta Allah wadda ke kirjinki
17] Cikinki shafaffe abin shaáwa kamar
A ce hatsi baya shiga hanjinki
18] Kuturinki zaunanne gwanintar haliku
Shima kawai yasa mutum begenki
19] Cinya da sharaba sumul sun mulmulu
Yannan ki gode Jallah wanda yayi ki.
20] Taka a sannu sarauniya kiyi rangwada
Dan kyan dake sawunki har yatsunki.
21] Zan bar batun kirar jiki zan dakata
Don banda kalmomin siffanta jikinki.
22] Sai dai in gode Jallah sarki Wahidun
Da ya ban idanu har na samu ganinki.
23] A takaice yanzu ki dakata kuma kiy kawai
Saurari sharhina ga halayenki.
24] Hakuri a gunki da hankali kuma ga natso
Tamkar ace mata su zo Kwas gunki.
25] Saurin fushi, tsiwa, fada ko yaudara
Ba ko guda a wajenki gandun kirki.
26] Wadanga siffofi da nai zance bisa
Su sunka sa kullum nake begenki.
27] A ina kike jin zaá san mace kamila
Mai kyan sifa, sannan da halin kirki?
28] Ko an nutsa, an bincika, an rairaye
Sai anyi saá zaá san tamkarki.
29] To shi yasa abadan a kullum safiya
Ni banda tasirin da ya wuce naki.
30] Kuma godiya kullum nake gun Rabbana
Sarkin da yai ikon in ganki, in soki.
31] Kana inyo roko garai Shi mai duka
Yasa ki kaunaci Bello da mai sonki.
Thursday, November 6, 2008
Wakar Talauci da Wadata; Darho
Al'adal Hausawa su kan rena matsiyaci, su kan yaba mai-dukiya,
suna rena baba matsiyaci, suna yaba yaro mai-kurdi, don haka
wani mutum ya wake halin Hausawa duka, sunansa Darho. Ita ke
nan :
A wannan waka, za'a ga anyi amfani da Hausa mai tsauri, domin kuwa, wannan tsohuwar waka ce. An rubuta ta ba tun yau ba. Ita ma na cikin wakokin da Malam Umar Salga ya baiwa Mischlisch a Kumasi.
1 Muna soma waka da suna na Allah,
Gama za mu tsari na halin tsiya .
2 Muna son kidaya t a halin talauci
Da halin wadata f a don ku jiya .
3 Kamannun talauci baki ne gajere
Da doro da tura da annakiya.
4 Kadan yabi yaro, shi tsofas dashi ,
Shi tantakore shi , shi yi kaman kugiya.
5 Idan ya bi tsofo, shi kan Rarasa shi ,
Shi rame, shi komo kaman tsarkiya .
6 Mutum mai-nagarta, kadan ya talauta ,
A maishe shi mugun, da ba gaskiya.
7 Mutum mai-karimci, kadan ya talauta ,
A ce, bashi kyauta da ko kokiiya.
8 Talakan mutum ba shi zance a taro ,
Fa zancensa sai ko cikin zuciya.
9 Kadan ya yi,zance a kan gaskiyarsa,
A ce masa, karya ka kai mun kiya.
A lalata zancen, a yaryamutsa shi ,
A maishe shi wauta abin dariya .
Fa baba talaka a maishe shi yaro,
A ce masa gebe kaman saniya .
Ace masa raggo, ace bashi lura ,
Ace masa, baban da ba moriya.
Kadan anyi taron buki, baa sa shi ,
Fasai za a watse, a kan tambaya.
Kadan za a taro na suna da amre,
Fa sai anyi nisa , a ce, shiyi biya.
Kadan an yi t aro , kamalsa daban ce,
Da wandonsa tsofo da 'yar Z ariya .
Fushin mai talauci abin dariya ne,
Fushinsa da murnalsa duka dai daya.
Talakan mutum ba shi samun aboki,
Fa wa ke abuta da dan shegiya?
18 Fa mai son talaka f a Allah Ta’alah,
Da ya y i talaka cikin jar wuya.
Fa mugun hali duk shi na gun talaka ,
Kadan dai ana son fadin gaskiya.
kazamta da wauta da bata zumunta
Da rowa da ka r ya da aikin riya .
A mugun jini babu tamkar talaka
Gidan duniyan nana ko mu jiya .
Idan ya y i zance da fara 'a ace mai,
dumi a gare shi cakoikoiniya.
Idan ya y i kawaici, a ce masa
Mugu da keta gare shi cikin zuciya.
Ka san, ba nagarta ga mai-yin talauci ,
Kadan za shi zance, a kan ce: tsaya .
Da zancenka mugu na wofi a duniya,
Zama ba ka zancen, da za’a biya .
Fa dangin talaka su nai masa kushe,
Su ce masa zumu ne, da ba moriya.
Ayyukan talaka dadai ba su kyawu
Ga bakin mutane f a har zuciya.
Idan yai da zaf i , su ce, babu tsabta ,
Yana tsarmatawa ga aiki jiya .
Idan yai da kyawu su ce, babu samri,
Yana da nawa, ya ki yi tun j i y a .
Yawan dariya gun talaka , mutane
Su maishe shi wawa kaman kanikiya .
Idan ya y i kawaici, su ce masa, mugu,
Cikinsa da zurfi kaman tumniya.
Fa inda talauci mutum ne, mutane,
Muna damre mu kekewaya.
Mu j e har bugensa, mu far masa da yaiki,
Mu ci shi , mu kamai, mu sa karkiya .
Mu ti kai mu kayes, mu damre, mu yanka,
Mu ja shi , mu yes can, mu ba maikiya.
35 Fa inda haki ne, muna ciccireshi ,
Shi bushe mu tara mu kone tsiya .
Fa haja ta talaka dadai ba ta kyawu,
Zuma nai a kan ce kaman tsamiya.
Idan yakuwa ce a kan ce da tsami,
Madi nai akance da kunkunniya.
diya tai dadai ba t a kyawu ga kowa,
A kan ce, gajera1 ga mai-cibiya.
Da kai gurgurrare, dada ga kumatu
Kaman diya ne na tumfaf iya.
Da cassa da ganni da kwarfin idanu
Da bakinta dogo kaman tsishiya .
A ce mata da kirci dada babu zama
Da warin jiki , sai ka ce rajiya .
Idan t a f i kyawu, a kan ce, da tsiwa,
Fa bata da kumya kaman shegiya.
Mutane, talauci mu ki shi da gaske,
Zama da talauci shina da wuya.
Idan an y i yunwa, abincin talaka
Fa ganyen rama, dorawa, gasaya.
Da rogo, da taura, da gaude, da tsada '
Da dumya da tafasa da har rojiya .
Da faru da gudai, kadanya, tamaka,
Dada magoraza, ciwo kinciya.
Talaka ana kinta amre gaduniya,
A sa mata aibu a rarrataya .
A ce mata kazama, tana barka zana,
A ce, bata shara f a , babu roriya .
Idan malami yai talauci ya shuda,
A kan ce, tababben ga nan ya biya.
A kan ce, karatunsa ya f irgita shi ,
A maishe shi wawa, abin dariya.
Idan yayi zance da nassi , a kyale,
Idan yayi harda, ace, ku jiya .
52 Fa ya tuna haukansa yau tun da s a f e ,
Makoftasu kan ce, fa ai tun jiya . "
Diya ta talaka idan baka ce,
A kan ce, bakinta da muni, jiya .
Idan kuwa, f arace ace tayi muni,
Farin ya faye, sai ka ce zabiya.
Idan tai gajerta ace babu kyawu,
A ce, dunkulalla kaman makaya.
Idan doguwa ce, akan ce, fatalwa,
Tsawon ya faye, kai , abin da wuya.
Dada kun ji halin talauci ku l u r a ,
Ku kilshe , ku tashi bidal dukiya.
Ku shirga Safara, ka j e har Fatoma,
Ku komo t a Bobo, ku zo Daboya.
Ku juya t a Jije , ku juyo ta Dor i
Ku jirgo ta Moshi ku zo har Kaya
Ku komo t a Salaga, ku j e har Kumashi,
Ku zaga t a Guwa, har Agaya.
Ku j e har Kano babu nisa wuce can,
Wadai kuma ka komo Zariya.
Ka ratse ta Kura ka samo baki can,
Ka komo t a Jega, ''tafo har Gaya.
Biyo har t a Sayi, ka komo t a Mangu,
Ka ratsa Dagomba, ka zo Kobiya.
Bidal dukiya wajibi ne gare mu,
Fa ko don mu kimsa zaman duniya.
Da sadaka da amre da suna da laiya ,
Sayen littafai sai akwai dukiya.
Bari da da haji da ci da marayi,
Wadannan ku san, sai akwai ajiya.
Da sa da karatu da gyaran zumunta
Da tanyon makofta f a duk, kun jiya .
Fa mun roki Allah, ya tsarshe mu tsanani
Na duniya da cuta da yunwa, tsiya .
WADATA
1 Muna soma tsari na halin wadata,
Fa jinsa da dadi cikin zuciya.
2 Mutum mawadaci akwai shi da girma,
Ana sonsa Hausa cikin zuciya.
3 Ana durkusa masa, ana bashi girma,
Ana son zumuntansa don dukiya.
4 Idan ya yi zance a taro a yarda,
Ace gaskiya ka fadi mun jiya .
5 Ku san, mawadaci ya kan kirfa karya ,
A ce babu wawa ku zo ku jiya .
6 Idan dumi nai ga taron mutane,
A kan ce, fa mai-fara'a ne shiya .
7 A ce walwala a gare shi ga duniya,
Ya kan bada labari ana dariya .
8 Idan yai karairansa , babu iyaka,
A yarda, a gyara, a ce gaskiya.
9 Fa shi ke da wayo ku san hankalinsa,
Kaman ya f i kowa cikin duniya.
Dada bambadawa suna yin yabonsa,
Suna ce, da kyawu kaman Utiya .
Ubansa wane, uwatasa wance,
Fa kakansa wane, mutanen jiya .
Da da nasa wane da 'ya tasa wance,
Da jikansa wane, fa to kun jiya.
Shi kan bada kyauta ta riga da wando
Da kurdi da tsaba har saniya.
Yana bada zanua da damma da rago,
Ya kan bada kyauta ta har godiya.
Mutum mai-wadata f a shi ke da kyauta,
Mutane su kan ce, fa ba ya shiya.
Idan ba shi zance, shina damre fuska,
Su ce, mai-kawaici, fa don gaskiya.
Su ce, ba shi zancensa, sai ya kamata,
Mutum mai-nagarta ina ya shiya ?
Diya tai dadai ba ta muni ga kowa,
A kan ce, da kyawu kaman Utiya.
A ce, doguwa ce idanu ya madara
Da fatar jiki sai ka ce maraya.
Ace tayi yatsa ya 'ya'ya na marga,
Ace ga duwawunta fa1 tsakiya .
Da mukurun barage hatsaya ta damra,
Ta sa kwandage munduwa sokiya.
Fa hannunta tafshi zama ta wadata,
Gama ba ta aikin da ya faifaya .
Idan kuwa baka ce, su kan ce, da kyawu,
Gama dai bakinta shina walkiya.
Idan kuwa fara ce, su ce, t a f i kyawu,
Farin nata koka Balarabiya.
Idan tai gajerta , su ce, babu komi,
Tana dai da kyawu, zama ta tsaya.
Gajertalta dai-dai kaman nan a ke so,
Zama tayi hanci da kan cibiya.
Idan doguwa ce, su kan ce, da kyawu,
Tsawon ya kamata, gama tai wuya.
A kan sota , mutum ya f i goma,
Ana ce, diya ce ta mai-dukiya.
Fa ga t a da nono, f a sun cika kirji ,
Idanunta kace idon hazbiya.
Kadan an y i amrenta garalta tari ,
Gama dai diya ce ta cin duniya .
A kan dauki kaya da kurdi da zanua,
A yauci gari, don a tambaya.
Mutum mawadaci akwai shi da girma,
Idan ya yi ado, sai a ce godiya.
Fa matansa, ku san, suna ba shi girma,
Suna boye sunansa don dukiya.
Suna durkusa masa, suna ba shi tur ba ,
Su ratse , suna boye fuska, jiya . "
Kadan ya cane, wanga aiki ku bar shi ,
Zama ba ni so nai , su ce, mun jiya .
36 Ku san bashi diba dukiyarsa, ya ba su
Matan nan gama dai , nufin su gare shi ajiya .
37 Fa tari talaka ya kan c i da mata,
Fa har tafi mata ta mai-dukiya.
38 Fa banza, gama babu saura a daki,
Kaman dai ruwa, an zuba rariya .
39 Kaman nan f a kyautar talaka ga mata,
Fa ko yayi , ba godiya, kun jiya?
40 Kadan dan karatu ya samu wada nan,
A kan ce da shi shaihu ne, ya iya.
41 Karatunsa dadi, rubutunsa sosai,
Hadisi, usuli duk ya biya.
42 Idan ya y i murya, a kan ce da dadi,
Kaman an y i gogen ga mai-tsagiya."
Idan an y i yunwa, mutum mawadaci
Abincinsa anberuwa, t a l i y a .
Da kaki, gurasa da waina da taushe,
Tuwo mai-fari, ga miya har miya.
Da kuskus da shashakaqq an garwaya su
Shinashir yana can cikin jar miya.
Fura kuwa ta gero a dama da nono, '
Zama dai ta safe zuma ya jiya .
Gidan mawadaci idan an gane shi ,
A kan san, wadatalsa ba tambaya.
Da soro ginane da darninsa sabo
Da shifkinsa mai-kyau f a an baibaya.
Gida na talaka kazamin gida ne
Da darni tsutsa , sai haki mai-kaya.
Da dai matsatsi da bununsa tsofo
Da kunkunniya, an dade tafaya .
Mutum mawadaci abokinsa sarki
Da malam da tsofon mutum mai-biya.
52 Mutane ku fuce matsari na waka,
Fa s h i ma talakan f a ne, kun jiya .
53 Fa na goda Allah, da na kare tsari
Na halin wada duk da halin tsiya .
54 Da tsira da girma da so duk da yarda,
Su taru ga manzo uban Rakiya.
suna rena baba matsiyaci, suna yaba yaro mai-kurdi, don haka
wani mutum ya wake halin Hausawa duka, sunansa Darho. Ita ke
nan :
A wannan waka, za'a ga anyi amfani da Hausa mai tsauri, domin kuwa, wannan tsohuwar waka ce. An rubuta ta ba tun yau ba. Ita ma na cikin wakokin da Malam Umar Salga ya baiwa Mischlisch a Kumasi.
1 Muna soma waka da suna na Allah,
Gama za mu tsari na halin tsiya .
2 Muna son kidaya t a halin talauci
Da halin wadata f a don ku jiya .
3 Kamannun talauci baki ne gajere
Da doro da tura da annakiya.
4 Kadan yabi yaro, shi tsofas dashi ,
Shi tantakore shi , shi yi kaman kugiya.
5 Idan ya bi tsofo, shi kan Rarasa shi ,
Shi rame, shi komo kaman tsarkiya .
6 Mutum mai-nagarta, kadan ya talauta ,
A maishe shi mugun, da ba gaskiya.
7 Mutum mai-karimci, kadan ya talauta ,
A ce, bashi kyauta da ko kokiiya.
8 Talakan mutum ba shi zance a taro ,
Fa zancensa sai ko cikin zuciya.
9 Kadan ya yi,zance a kan gaskiyarsa,
A ce masa, karya ka kai mun kiya.
A lalata zancen, a yaryamutsa shi ,
A maishe shi wauta abin dariya .
Fa baba talaka a maishe shi yaro,
A ce masa gebe kaman saniya .
Ace masa raggo, ace bashi lura ,
Ace masa, baban da ba moriya.
Kadan anyi taron buki, baa sa shi ,
Fasai za a watse, a kan tambaya.
Kadan za a taro na suna da amre,
Fa sai anyi nisa , a ce, shiyi biya.
Kadan an yi t aro , kamalsa daban ce,
Da wandonsa tsofo da 'yar Z ariya .
Fushin mai talauci abin dariya ne,
Fushinsa da murnalsa duka dai daya.
Talakan mutum ba shi samun aboki,
Fa wa ke abuta da dan shegiya?
18 Fa mai son talaka f a Allah Ta’alah,
Da ya y i talaka cikin jar wuya.
Fa mugun hali duk shi na gun talaka ,
Kadan dai ana son fadin gaskiya.
kazamta da wauta da bata zumunta
Da rowa da ka r ya da aikin riya .
A mugun jini babu tamkar talaka
Gidan duniyan nana ko mu jiya .
Idan ya y i zance da fara 'a ace mai,
dumi a gare shi cakoikoiniya.
Idan ya y i kawaici, a ce masa
Mugu da keta gare shi cikin zuciya.
Ka san, ba nagarta ga mai-yin talauci ,
Kadan za shi zance, a kan ce: tsaya .
Da zancenka mugu na wofi a duniya,
Zama ba ka zancen, da za’a biya .
Fa dangin talaka su nai masa kushe,
Su ce masa zumu ne, da ba moriya.
Ayyukan talaka dadai ba su kyawu
Ga bakin mutane f a har zuciya.
Idan yai da zaf i , su ce, babu tsabta ,
Yana tsarmatawa ga aiki jiya .
Idan yai da kyawu su ce, babu samri,
Yana da nawa, ya ki yi tun j i y a .
Yawan dariya gun talaka , mutane
Su maishe shi wawa kaman kanikiya .
Idan ya y i kawaici, su ce masa, mugu,
Cikinsa da zurfi kaman tumniya.
Fa inda talauci mutum ne, mutane,
Muna damre mu kekewaya.
Mu j e har bugensa, mu far masa da yaiki,
Mu ci shi , mu kamai, mu sa karkiya .
Mu ti kai mu kayes, mu damre, mu yanka,
Mu ja shi , mu yes can, mu ba maikiya.
35 Fa inda haki ne, muna ciccireshi ,
Shi bushe mu tara mu kone tsiya .
Fa haja ta talaka dadai ba ta kyawu,
Zuma nai a kan ce kaman tsamiya.
Idan yakuwa ce a kan ce da tsami,
Madi nai akance da kunkunniya.
diya tai dadai ba t a kyawu ga kowa,
A kan ce, gajera1 ga mai-cibiya.
Da kai gurgurrare, dada ga kumatu
Kaman diya ne na tumfaf iya.
Da cassa da ganni da kwarfin idanu
Da bakinta dogo kaman tsishiya .
A ce mata da kirci dada babu zama
Da warin jiki , sai ka ce rajiya .
Idan t a f i kyawu, a kan ce, da tsiwa,
Fa bata da kumya kaman shegiya.
Mutane, talauci mu ki shi da gaske,
Zama da talauci shina da wuya.
Idan an y i yunwa, abincin talaka
Fa ganyen rama, dorawa, gasaya.
Da rogo, da taura, da gaude, da tsada '
Da dumya da tafasa da har rojiya .
Da faru da gudai, kadanya, tamaka,
Dada magoraza, ciwo kinciya.
Talaka ana kinta amre gaduniya,
A sa mata aibu a rarrataya .
A ce mata kazama, tana barka zana,
A ce, bata shara f a , babu roriya .
Idan malami yai talauci ya shuda,
A kan ce, tababben ga nan ya biya.
A kan ce, karatunsa ya f irgita shi ,
A maishe shi wawa, abin dariya.
Idan yayi zance da nassi , a kyale,
Idan yayi harda, ace, ku jiya .
52 Fa ya tuna haukansa yau tun da s a f e ,
Makoftasu kan ce, fa ai tun jiya . "
Diya ta talaka idan baka ce,
A kan ce, bakinta da muni, jiya .
Idan kuwa, f arace ace tayi muni,
Farin ya faye, sai ka ce zabiya.
Idan tai gajerta ace babu kyawu,
A ce, dunkulalla kaman makaya.
Idan doguwa ce, akan ce, fatalwa,
Tsawon ya faye, kai , abin da wuya.
Dada kun ji halin talauci ku l u r a ,
Ku kilshe , ku tashi bidal dukiya.
Ku shirga Safara, ka j e har Fatoma,
Ku komo t a Bobo, ku zo Daboya.
Ku juya t a Jije , ku juyo ta Dor i
Ku jirgo ta Moshi ku zo har Kaya
Ku komo t a Salaga, ku j e har Kumashi,
Ku zaga t a Guwa, har Agaya.
Ku j e har Kano babu nisa wuce can,
Wadai kuma ka komo Zariya.
Ka ratse ta Kura ka samo baki can,
Ka komo t a Jega, ''tafo har Gaya.
Biyo har t a Sayi, ka komo t a Mangu,
Ka ratsa Dagomba, ka zo Kobiya.
Bidal dukiya wajibi ne gare mu,
Fa ko don mu kimsa zaman duniya.
Da sadaka da amre da suna da laiya ,
Sayen littafai sai akwai dukiya.
Bari da da haji da ci da marayi,
Wadannan ku san, sai akwai ajiya.
Da sa da karatu da gyaran zumunta
Da tanyon makofta f a duk, kun jiya .
Fa mun roki Allah, ya tsarshe mu tsanani
Na duniya da cuta da yunwa, tsiya .
WADATA
1 Muna soma tsari na halin wadata,
Fa jinsa da dadi cikin zuciya.
2 Mutum mawadaci akwai shi da girma,
Ana sonsa Hausa cikin zuciya.
3 Ana durkusa masa, ana bashi girma,
Ana son zumuntansa don dukiya.
4 Idan ya yi zance a taro a yarda,
Ace gaskiya ka fadi mun jiya .
5 Ku san, mawadaci ya kan kirfa karya ,
A ce babu wawa ku zo ku jiya .
6 Idan dumi nai ga taron mutane,
A kan ce, fa mai-fara'a ne shiya .
7 A ce walwala a gare shi ga duniya,
Ya kan bada labari ana dariya .
8 Idan yai karairansa , babu iyaka,
A yarda, a gyara, a ce gaskiya.
9 Fa shi ke da wayo ku san hankalinsa,
Kaman ya f i kowa cikin duniya.
Dada bambadawa suna yin yabonsa,
Suna ce, da kyawu kaman Utiya .
Ubansa wane, uwatasa wance,
Fa kakansa wane, mutanen jiya .
Da da nasa wane da 'ya tasa wance,
Da jikansa wane, fa to kun jiya.
Shi kan bada kyauta ta riga da wando
Da kurdi da tsaba har saniya.
Yana bada zanua da damma da rago,
Ya kan bada kyauta ta har godiya.
Mutum mai-wadata f a shi ke da kyauta,
Mutane su kan ce, fa ba ya shiya.
Idan ba shi zance, shina damre fuska,
Su ce, mai-kawaici, fa don gaskiya.
Su ce, ba shi zancensa, sai ya kamata,
Mutum mai-nagarta ina ya shiya ?
Diya tai dadai ba ta muni ga kowa,
A kan ce, da kyawu kaman Utiya.
A ce, doguwa ce idanu ya madara
Da fatar jiki sai ka ce maraya.
Ace tayi yatsa ya 'ya'ya na marga,
Ace ga duwawunta fa1 tsakiya .
Da mukurun barage hatsaya ta damra,
Ta sa kwandage munduwa sokiya.
Fa hannunta tafshi zama ta wadata,
Gama ba ta aikin da ya faifaya .
Idan kuwa baka ce, su kan ce, da kyawu,
Gama dai bakinta shina walkiya.
Idan kuwa fara ce, su ce, t a f i kyawu,
Farin nata koka Balarabiya.
Idan tai gajerta , su ce, babu komi,
Tana dai da kyawu, zama ta tsaya.
Gajertalta dai-dai kaman nan a ke so,
Zama tayi hanci da kan cibiya.
Idan doguwa ce, su kan ce, da kyawu,
Tsawon ya kamata, gama tai wuya.
A kan sota , mutum ya f i goma,
Ana ce, diya ce ta mai-dukiya.
Fa ga t a da nono, f a sun cika kirji ,
Idanunta kace idon hazbiya.
Kadan an y i amrenta garalta tari ,
Gama dai diya ce ta cin duniya .
A kan dauki kaya da kurdi da zanua,
A yauci gari, don a tambaya.
Mutum mawadaci akwai shi da girma,
Idan ya yi ado, sai a ce godiya.
Fa matansa, ku san, suna ba shi girma,
Suna boye sunansa don dukiya.
Suna durkusa masa, suna ba shi tur ba ,
Su ratse , suna boye fuska, jiya . "
Kadan ya cane, wanga aiki ku bar shi ,
Zama ba ni so nai , su ce, mun jiya .
36 Ku san bashi diba dukiyarsa, ya ba su
Matan nan gama dai , nufin su gare shi ajiya .
37 Fa tari talaka ya kan c i da mata,
Fa har tafi mata ta mai-dukiya.
38 Fa banza, gama babu saura a daki,
Kaman dai ruwa, an zuba rariya .
39 Kaman nan f a kyautar talaka ga mata,
Fa ko yayi , ba godiya, kun jiya?
40 Kadan dan karatu ya samu wada nan,
A kan ce da shi shaihu ne, ya iya.
41 Karatunsa dadi, rubutunsa sosai,
Hadisi, usuli duk ya biya.
42 Idan ya y i murya, a kan ce da dadi,
Kaman an y i gogen ga mai-tsagiya."
Idan an y i yunwa, mutum mawadaci
Abincinsa anberuwa, t a l i y a .
Da kaki, gurasa da waina da taushe,
Tuwo mai-fari, ga miya har miya.
Da kuskus da shashakaqq an garwaya su
Shinashir yana can cikin jar miya.
Fura kuwa ta gero a dama da nono, '
Zama dai ta safe zuma ya jiya .
Gidan mawadaci idan an gane shi ,
A kan san, wadatalsa ba tambaya.
Da soro ginane da darninsa sabo
Da shifkinsa mai-kyau f a an baibaya.
Gida na talaka kazamin gida ne
Da darni tsutsa , sai haki mai-kaya.
Da dai matsatsi da bununsa tsofo
Da kunkunniya, an dade tafaya .
Mutum mawadaci abokinsa sarki
Da malam da tsofon mutum mai-biya.
52 Mutane ku fuce matsari na waka,
Fa s h i ma talakan f a ne, kun jiya .
53 Fa na goda Allah, da na kare tsari
Na halin wada duk da halin tsiya .
54 Da tsira da girma da so duk da yarda,
Su taru ga manzo uban Rakiya.
Thursday, October 30, 2008
Wakar Abinda
Ita dai wannan wakar, malam Umaru Salga ne ya baiwa Mischlich, wani baturen mulki na kasar Jamus, a yayin da yake kokarin tattara bayanai akan tarihin kasar Hausa, domin manazarta dake can kasar Jamus. A cewarsa, "wani almajiri ne ya auri wata mata maisuna Abinda, amma kuma ita Abinda kazama ce ta kin karawa, to a saboda haka sai ya shirya mata wannan waka. Ka nemi kasidar M. B. Dufill domin samun karin bayani.
1 Abinda kazama ce kwarai, ba kadan na ba.
2 Ina son k i bar halin da duk, bai kamata ba.
3 K i zam yin fa shara, kuma kina dumke farkuwa.
4 Iya t a mutane, duk ba ta bar abin ga ba.
5 Tuwonki k i zam gyara, kisa 'yan ruwa kadan.
6 Tuwon j iya kin bata , shi mu ba mu c i shi ba.
7 Idan kin y i min damun fura , saita yamutse.
8 Fa ko na ji yunwa, ba ni iya shan furalkiba.
9 Abin ga da kumya kuma da haushi ga zuciya.
10 Abinda k i bar halin ga, duka bai kamata ba.
1 Abinda kazama ce kwarai, ba kadan na ba.
2 Ina son k i bar halin da duk, bai kamata ba.
3 K i zam yin fa shara, kuma kina dumke farkuwa.
4 Iya t a mutane, duk ba ta bar abin ga ba.
5 Tuwonki k i zam gyara, kisa 'yan ruwa kadan.
6 Tuwon j iya kin bata , shi mu ba mu c i shi ba.
7 Idan kin y i min damun fura , saita yamutse.
8 Fa ko na ji yunwa, ba ni iya shan furalkiba.
9 Abin ga da kumya kuma da haushi ga zuciya.
10 Abinda k i bar halin ga, duka bai kamata ba.
Wakar Madugu Yahaya; 18th Century
Ita dai wannan wakar wani marokine yayita, shi wannan mawaki da ake kira Yahaya, ba zama yake a gida yana waka ba. A zamanin da ake tafiya fatauci a kasar zuwa, zuwa kasashen ketare, shi sai ya bi ayari, inda duk aka sauka a zango, ya jawo kayan kidansa, yanawa madugai waka. Ba dai takamaiman lokacin da aka yi wannan waka, to amma wanio manazarci da ake kira M. B. Duffill, yayi hasashen cewa, an rubutatane a karshen karni na 18, ko kuma a farkon karni na 19. Ga mai neman cikakken bayani ga wannan waka, sai ya nemi kasidar da M. B. Dufill ya buga a mujallar SOAS, Vol 13, (1986).
Allah ya k aimu Hausa, ba don iya magana ba.
Madugu Yahaya shi bai iya magana ba .
In an tambaya, ya kan ce: Shiga! debi!
Shiga! debi! Borgu, ba zance ne ba.
Yanzu ga Waru zamne, ga washagari.
Ga waga banye, a ce: Shiga! debi!
Madugu Yahaya, shi bai iya tafiya ba.
Zangon azuhur shi kan ce masa hantsi .
Rana faduwa shi kan ce, la'asar ne.
Mai-baki da garatse ' ' kaman bakin gwando.
Kuma baki da garatse namij in yauni.
Ana tashi, ko ana yankan damna?
Miji da kurkunu, ga jak i da alafa .
Ga mata da guragu, '' kuma babu ruwan gora.
Ana yin salla Sayi, ko salon mussar wofi ?
Gurin salla Sayi aka dauke mini wando.
Malam Iyal yana gyaran sage, dada ya ga k irarra .
18 Wanga hannu da gargaza, wancan kuwa ga yauni.
19 Yana ciza gargaza, yana ciza yauni .
20 Yana cewa: Tudun nan muka jida , ko muna kai ga tudun can?
21 Sani dan Muhamman, baban gwani na Jega.
Thursday, May 31, 2007
Ya Ghiyathul Mustagithina; Daga Hayatu bin Sa'id
Hayatu bin Sa'id baya bukatar gabatarwa ga mutane, domin ga wanda yasan tarihin daular Fulani ta Sakkwato, yasan irin gwagwarmayar da aka sha da shi, da kuma yadda yayiwa Daular tawaye. Wanda, bayan hakan yayi mubayi'a ga Muhammad bin Abdullahi al Mahdi,na Sudan. Mahdi ya nada shi a matsayin halifansa a Daular Sakkwato, inda ya nemi Sarkin MUsulmi na wannan lokacin da yayi masa mubayi'a. Rashin samun nasarar hakan ce ta sanya ya koma ya hada kai da Rabih bin Salih (Rabeh). Inda daga baya suka samu sabani, ya dai rasu a wani karo da suka yi da Rabih. Ya rubuta wannan waka ce, a wani shagube da yayiwa yan'uwansa, a saboda irin mummunar fahimtar da suka yi masa.
Ga dai wakar;
1Ya Ghiyathul mustaghithina
2-na wa khairal nasirina
3Agaza ni kadda ka barni
4Ga dibarata ta kaini
5Yi dibara mai dibara
6Rahmanu ka jikaina
6Rabbu dubanni da rahma
7Anta khairil Rahimina
8Rahamakka sabiqata
9Jin kanka wabilina
10Babu mai yi sai da yin ka
11Wanga zance haka nan na
12Kai kayi ba taliki ba
13Taliki kau ajizina
14Rabbu kai ad dai Qadirun
16Jallah Sarki Qadirina
17Babu sarki daga Allah
18Shi fa Sarkin Gaskiyana
19Wanda yai sammai da kassai
20Wanda yayi dare da rana
21Wanda yai duniya da Barzakh
22Bata tsar mai ko ina na
23Wanda yai ran al-Qiyama
24Shi Azizi na gwanina
25Wanda yai wuta yayi al-Jan
26-na hakika Fatirina
27Agaza ni na kiraka
28Don Muhammadu yo i'ana
29Rabbu tsarshen daga kaidin
30Masu kaidi mufsidina
31Masu hasda da Adawa
32Da gamani kha'inina
33Sare kunci duk na makri
34Jallah Khairul makhirina
35Jallah kai ka tsadda Nuhu
36Shi da Hudu ga kafirina
37Jallah kai ka tsadda Ibra
38-him ga kaumun mu'tadina
39Kai fa kacce kana haqqun
40Fika nasarul muminina
41Don Muhammadu ya ilahil
42Arshi tsarshen makiyana
43Bani ikon shafe bid'a
44Bani ikon raya sunna
45Yo ijaba nai salati
46Ga Muhammadu dan Amina
47Hakaza Allai Sahabbai
48Duk jama'a tabi'ina
Ga dai wakar;
1Ya Ghiyathul mustaghithina
2-na wa khairal nasirina
3Agaza ni kadda ka barni
4Ga dibarata ta kaini
5Yi dibara mai dibara
6Rahmanu ka jikaina
6Rabbu dubanni da rahma
7Anta khairil Rahimina
8Rahamakka sabiqata
9Jin kanka wabilina
10Babu mai yi sai da yin ka
11Wanga zance haka nan na
12Kai kayi ba taliki ba
13Taliki kau ajizina
14Rabbu kai ad dai Qadirun
16Jallah Sarki Qadirina
17Babu sarki daga Allah
18Shi fa Sarkin Gaskiyana
19Wanda yai sammai da kassai
20Wanda yayi dare da rana
21Wanda yai duniya da Barzakh
22Bata tsar mai ko ina na
23Wanda yai ran al-Qiyama
24Shi Azizi na gwanina
25Wanda yai wuta yayi al-Jan
26-na hakika Fatirina
27Agaza ni na kiraka
28Don Muhammadu yo i'ana
29Rabbu tsarshen daga kaidin
30Masu kaidi mufsidina
31Masu hasda da Adawa
32Da gamani kha'inina
33Sare kunci duk na makri
34Jallah Khairul makhirina
35Jallah kai ka tsadda Nuhu
36Shi da Hudu ga kafirina
37Jallah kai ka tsadda Ibra
38-him ga kaumun mu'tadina
39Kai fa kacce kana haqqun
40Fika nasarul muminina
41Don Muhammadu ya ilahil
42Arshi tsarshen makiyana
43Bani ikon shafe bid'a
44Bani ikon raya sunna
45Yo ijaba nai salati
46Ga Muhammadu dan Amina
47Hakaza Allai Sahabbai
48Duk jama'a tabi'ina
Sunday, May 13, 2007
Wakar Gyaran Kano; Daga Dr Aliyu Aqilu 1975
Wannan waka an rubuta ta ne a 1975, ya kuma yi tane domin wani hangen nesa da yaga Kantomman Kano na weannan lokaci yayi, wato Dr Uba Adamu. A hirar da nayi da Dr Uba Adamu, a gidansa cikin watan April, ya bayyana mini cewa " Cikin 1974 ne suka yi tunanin, kawo gyara a tsarin zamantakewar birnin Kano. A saboda haka suka kawo wani tsari, wanda hakan ya haifar da gina manyan tituna a Birnin Kano, da yin Kwalbatoci, da kuma wajejen zuba shara. A wannan lokacin ne akayi Manyan titunan da ake amfani dasu har yanzu a birnin Kano. Aka kuma yi musu Kwalbatoci a gefunansu, da kuma wajejen zuba shara". A saboda jin dadin wannan aiki ne, ya sanya Dr Aliyu Aqilu ya yi wannan waka. Ga dai wakar
Zan je ziyarar shugaba
Dattijo Kantoma Uba.
Bazan shiru na kawai ta ba
In ba da na ce Rabbu ba.
Sarki guda daya wahidi
Bazan takaita kiransa ba.
Bayan fadar Allah da gai da
Manzo Muhammadu Mujtaba.
Me zai biyo bayan su ne
Na abin nufi da yake gaba.
Haka ne akwai wani dan batu
Da ba zan ki tunkarar sa ba.
Ga dai bayani dan kadan
A takaice ba dungunsa ba.
Niyar ziyara ce dani
Zancenta yau zan bayyana.
Mai tambaya ya so yaji
Domin ya amfana gaba.
Manufar ziyarar wacce nai
Maganarta tun farko gaba.
Ya zuwa ina wai zani kai
Mai tambaya bai aibu ba.
Zan bayyana masa ne ya ji
Bazan yi kwauro gun sa ba.
Zan dau ziyara ne ni kai
Ta kano gari ba kauye ba.
Wajen masoyina abin
kamna sahihin Shugaba.
Shine Muhammadu Adamu
Kantoma mai lakabi Uba.
Dattijo din nan adali
Mai tausayin jama'a Uba.
Bangon tama ki faduwa
Sha kabra garnakaki Uba.
Matsayinka din nan kai can
Canta da shi malam Uba.
Illimi zalaka ke gare
ka da kwarjini na kwarai Uba.
Ga hattara ga hankali
Kantoma ga hangen gaba.
Illimin makamar zamani
Da sanin sharia tun gaba.
Ka san su ka kuma dandake
Ba yau kawai ka tsire suba.
Birnin Kano da wajenta duk
Ta samu babban cigaba.
A wajen nizafa in ka du
Ba kauyuka ba a bar suba.
Balle cikin birnin fa
Ba wai bane ba inke ba.
Kwatami cakal yau babu shi
Shara butsa bamu ganta ba.
Sarari a hanya ya dadu
Albarkacin himmar Uba.
Duk tarkace an kauda su
Daga ko ina ba a bar shi ba.
Sababi da wane mun ka sami
wannan gimgimemen cigaba.
Mun samu kakkaifan mutum
Mai kokari ba kasa ba.
Gwarzon maza namijin tsaye
Inuwa ba a bisne ki ba.
Kantoma Muhammadu Adamu
Dattijo mai lakabi Uba.
Bompai da Rimin Dada sun
Maka godiya malam Uba.
Sabon gari da Tudun wada
Sun gode mai daraja Uba.
Tarauni su da Giginyu sun
Yi yabo ga mai daraja Uba.
Gandu Sharada da Dorayi
Da Salanta., Calawa gaba.
Jama’ar da ke Fanshekara
Duk sun yi san barka Uba.
Waika da Jajira, Gobira
Wa, sun yi godiya malam Uba.
Kurna, Fagged da Gwagwarwa
sun maka godiya malam Uba.
Na sauka Fanisau mutan
Gama sun game da yabon Uba.
Ungogo, Kunya suna fadar
Madalla-madalla Uba.
Wannan Sadauki adali
Dattijo bai yashe mu ba.
Kub! Dai yawa kuwa lara bugu
Daya ta mace bata tashi ba.
Ya watsa rundunar
Sauro a yau bamu ji shi ba.
Bana nufin guda da dai
Ban daura niyyar yinta ba.
Amma dalili ya saka, ni
Na yi ta ban shiryeta ba.
Domin saboda farin ciki
Dadin zamanmu da kai Uba.
Zai sa ni Kwalla yar kadan
Watakil bakwa zarge niba.
Sirri na kokon zuciya
Fuska bata rasa jin sa ba.
Yururui! A yau na randama
Kodai da ban sabeta.
Amma akwai Magana daban
Da ba zan iya ban yi taba.
Domin ta nai mini kaikayi
Na zo ka sosa wajen Uba.
Najasa da ke yi barkatai
Haka nan butsa! An zuzzuba.
Ba kariya ko yar kadan
Daga baya har ya zuwa gaba.
Ka ga sangamemen saurayi
Bama su yara kanana ba.
Ya yaye al’aura a fi
Li bada jin kunyarsa ba.
Wannan abin bisa gaskiya
Ban samu jin dadinsa ba.
Domin akwai ill agama
Baki ba za su yabe mu ba
Harma sukan zarge mu ne
Ba wai bane, ba inke ba.
Ni naji sanda suke fade
Kuma na gwada na jarraba.
Kasan ni kan fita ne waje
Zancenga ban kage shi ba.
Wannan ta ja mini damuwa
Na tafo ka maganta Uba.
Ai ya kamata ka tsawata
Kuma kar a kara nan gaba.
Nasan ka baka rurumi
Kuma baka lalaci Uba.
Me maida kai kake mai kula
Ga abinda duk ka saka gaba.
Tsuguna da tashi ba’a yin ta
A ofishin malam Uba.
Baka shiri da munafuki
Cece-kuce baka ji shi ba.
Kowa shigo da maganganu
Mara sa shiri a gaban Uba.
Kudarsa zai kuwa dandana
Dadin karon bai ji shi ba.
Su kwaramniya da rigingimu
Da hayaniya an zuzzuba.
Duk dai a karata dole ne
Ayi gaskiya a gaban Uba.
Domin kurum shi kayi shi ji
Kowa abinda ya rattaba.
Suna daban yau zan fada
A gareka yau malam Uba.
Kere kana fasa kan maki
Bin gaskiya baka san shi ba.
In kun tuna nace da ku
Guda bana rika yin ta ba.
Amma fa har haka dan ku ji
Dadi bazai inganta ba.
In banda an ware shi an
Yafa shi an more shi ba.
Kash! Nan wajen zan dakata
In sa alama sai gaba.
Ni ne Aqilu Aliyu na
Gaisheka mai daraja Uba.
Kantoma huta lafiya
Sai lokaci wani nan gaba.
In Rabbana ya kaddara
Mana saduwa ban mata ba.
Bana yawaita maganganu
Sai addu’a zan kattaba.
Ya Rabbi ya Sarki Gwani
Allah ka ja zamanin Uba.
Amin saboda abin biya
Da yabo Muhammadu Mujtaba.
Tamat bi AunilLahi mun
Bidi taimako nasa tun gaba.>
Zan je ziyarar shugaba
Dattijo Kantoma Uba.
Bazan shiru na kawai ta ba
In ba da na ce Rabbu ba.
Sarki guda daya wahidi
Bazan takaita kiransa ba.
Bayan fadar Allah da gai da
Manzo Muhammadu Mujtaba.
Me zai biyo bayan su ne
Na abin nufi da yake gaba.
Haka ne akwai wani dan batu
Da ba zan ki tunkarar sa ba.
Ga dai bayani dan kadan
A takaice ba dungunsa ba.
Niyar ziyara ce dani
Zancenta yau zan bayyana.
Mai tambaya ya so yaji
Domin ya amfana gaba.
Manufar ziyarar wacce nai
Maganarta tun farko gaba.
Ya zuwa ina wai zani kai
Mai tambaya bai aibu ba.
Zan bayyana masa ne ya ji
Bazan yi kwauro gun sa ba.
Zan dau ziyara ne ni kai
Ta kano gari ba kauye ba.
Wajen masoyina abin
kamna sahihin Shugaba.
Shine Muhammadu Adamu
Kantoma mai lakabi Uba.
Dattijo din nan adali
Mai tausayin jama'a Uba.
Bangon tama ki faduwa
Sha kabra garnakaki Uba.
Matsayinka din nan kai can
Canta da shi malam Uba.
Illimi zalaka ke gare
ka da kwarjini na kwarai Uba.
Ga hattara ga hankali
Kantoma ga hangen gaba.
Illimin makamar zamani
Da sanin sharia tun gaba.
Ka san su ka kuma dandake
Ba yau kawai ka tsire suba.
Birnin Kano da wajenta duk
Ta samu babban cigaba.
A wajen nizafa in ka du
Ba kauyuka ba a bar suba.
Balle cikin birnin fa
Ba wai bane ba inke ba.
Kwatami cakal yau babu shi
Shara butsa bamu ganta ba.
Sarari a hanya ya dadu
Albarkacin himmar Uba.
Duk tarkace an kauda su
Daga ko ina ba a bar shi ba.
Sababi da wane mun ka sami
wannan gimgimemen cigaba.
Mun samu kakkaifan mutum
Mai kokari ba kasa ba.
Gwarzon maza namijin tsaye
Inuwa ba a bisne ki ba.
Kantoma Muhammadu Adamu
Dattijo mai lakabi Uba.
Bompai da Rimin Dada sun
Maka godiya malam Uba.
Sabon gari da Tudun wada
Sun gode mai daraja Uba.
Tarauni su da Giginyu sun
Yi yabo ga mai daraja Uba.
Gandu Sharada da Dorayi
Da Salanta., Calawa gaba.
Jama’ar da ke Fanshekara
Duk sun yi san barka Uba.
Waika da Jajira, Gobira
Wa, sun yi godiya malam Uba.
Kurna, Fagged da Gwagwarwa
sun maka godiya malam Uba.
Na sauka Fanisau mutan
Gama sun game da yabon Uba.
Ungogo, Kunya suna fadar
Madalla-madalla Uba.
Wannan Sadauki adali
Dattijo bai yashe mu ba.
Kub! Dai yawa kuwa lara bugu
Daya ta mace bata tashi ba.
Ya watsa rundunar
Sauro a yau bamu ji shi ba.
Bana nufin guda da dai
Ban daura niyyar yinta ba.
Amma dalili ya saka, ni
Na yi ta ban shiryeta ba.
Domin saboda farin ciki
Dadin zamanmu da kai Uba.
Zai sa ni Kwalla yar kadan
Watakil bakwa zarge niba.
Sirri na kokon zuciya
Fuska bata rasa jin sa ba.
Yururui! A yau na randama
Kodai da ban sabeta.
Amma akwai Magana daban
Da ba zan iya ban yi taba.
Domin ta nai mini kaikayi
Na zo ka sosa wajen Uba.
Najasa da ke yi barkatai
Haka nan butsa! An zuzzuba.
Ba kariya ko yar kadan
Daga baya har ya zuwa gaba.
Ka ga sangamemen saurayi
Bama su yara kanana ba.
Ya yaye al’aura a fi
Li bada jin kunyarsa ba.
Wannan abin bisa gaskiya
Ban samu jin dadinsa ba.
Domin akwai ill agama
Baki ba za su yabe mu ba
Harma sukan zarge mu ne
Ba wai bane, ba inke ba.
Ni naji sanda suke fade
Kuma na gwada na jarraba.
Kasan ni kan fita ne waje
Zancenga ban kage shi ba.
Wannan ta ja mini damuwa
Na tafo ka maganta Uba.
Ai ya kamata ka tsawata
Kuma kar a kara nan gaba.
Nasan ka baka rurumi
Kuma baka lalaci Uba.
Me maida kai kake mai kula
Ga abinda duk ka saka gaba.
Tsuguna da tashi ba’a yin ta
A ofishin malam Uba.
Baka shiri da munafuki
Cece-kuce baka ji shi ba.
Kowa shigo da maganganu
Mara sa shiri a gaban Uba.
Kudarsa zai kuwa dandana
Dadin karon bai ji shi ba.
Su kwaramniya da rigingimu
Da hayaniya an zuzzuba.
Duk dai a karata dole ne
Ayi gaskiya a gaban Uba.
Domin kurum shi kayi shi ji
Kowa abinda ya rattaba.
Suna daban yau zan fada
A gareka yau malam Uba.
Kere kana fasa kan maki
Bin gaskiya baka san shi ba.
In kun tuna nace da ku
Guda bana rika yin ta ba.
Amma fa har haka dan ku ji
Dadi bazai inganta ba.
In banda an ware shi an
Yafa shi an more shi ba.
Kash! Nan wajen zan dakata
In sa alama sai gaba.
Ni ne Aqilu Aliyu na
Gaisheka mai daraja Uba.
Kantoma huta lafiya
Sai lokaci wani nan gaba.
In Rabbana ya kaddara
Mana saduwa ban mata ba.
Bana yawaita maganganu
Sai addu’a zan kattaba.
Ya Rabbi ya Sarki Gwani
Allah ka ja zamanin Uba.
Amin saboda abin biya
Da yabo Muhammadu Mujtaba.
Tamat bi AunilLahi mun
Bidi taimako nasa tun gaba.>
Saturday, May 12, 2007
Wakar da ake Sanin Halin mata da ita; Muhammad Dangani Katsina
Wannan waka dai ta shahara a kafafen watsa labarai na Kano da Kaduna,domin akan watsa ta a shirye-shirye da dama.Ga dai wakar.
Bismillahir Rahmanir Rahim
Wasallallahu ala Nabiyul Karim
To bismiLlah Allah Sarki
Mai abu mai komai mai kyauta
Bani zalaka, bani fasaha
Inyi bayani na, a fahimta
Zanyi bayani halin mata
Zani rubuta, don a karanta
Kasan mata sun kasu ukku
Zo kusa in na fada ka rubuta
Akwai mata mai tsoron Allah
Bata nufin kowa da mugunta
Akwai wata ga barna ga gyara
Gata da saukin kai ga cuta
Sai ta ukunsu gadangama kenan
Bata nufin gyara sai cuta
Bata nufin hairi ga mijinta
Baga kiyoshi,ba ga makwabta
Bata nufin gyara sai barna
Sai duk safe ta cuci mijinta
Ya tafi office kokuma kanti
Bata kara zama dakinta
In mai noma ne ko zage
Ya tafi gona, zaure za ta
Tana nema taga masu wucewa
Wai ita dai suga kyan fuskarta
In taga sunki shiga harkarta
Sai kaji tace zata makwabta
Kaji irin halayen mata
Munana,manyan, makwadaita
In mace bata da kunya barta
Kama da miya,in ba gishirinta
In mace bata raga maka barta
Daina nufinta kabar sha'awarta
In mace ta zama bata ragama
Ko ka sota, kana kuma kinta
In mace, shashanci ya gameta
Ba mai kara ganin kirkinta
Bata nufin Allah da Ma'aiki
Sai bidi'a ita ke ka gunta
Taji ana Biko tai mika
Sai kaji tace Biko zata
Ba dangin iya babu na Baba
Ko kace ta bari, can zata
Wannan mace,ba mace ce ba
Dai na nufinta kabar sha'awarta
Natsuwa itace mace,ko yar wace
In kaga ba natsuwa,ka bajeta
Kasan mata sun iya karya
Sun iya yadda suke shirgata
Ba duk mace ke son addini ba
Nufinsu a basu kudi, su bukata
Matar da ta zam bata san Allah ba
Ba ta kara zama dakinta
Sai ta fito a tashar Takatale
Sai tai batsa gaban kanwarta
In kace mata, wance ki lura
Baka hana ni bugun cinyata
Babu ruwanta da kunya faufau
Ga Ashar, ko ciwake yana kunyarta
Sanarwata itace ga mazaje
Kar a yawaita kwadai, a takaita
Aure ba abu ne ba na wasa
Bar neman kyau, nemi nagarta
Ni nasan mace, komi kyaunta
Indai babu hali da nagarta
Kana sha'awarta, kana kuma sonta
Badan Allah ba kana kyale ta
Don haka, tun farko ka tsaya tsaf!
Kai nazari da irin halinta
In mace ta zama, shagiri girbau
Ko ka aureta, baka iyata.
Kun ji mazaje, kar ku kiya man
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai mata na nan su shidda
Zo kusa inna fada ka jimilta
Akwai dibgau! Mai dibge mijinta
Ba ta jira ga fada shi taya ta
Danbago, mai zurfin tumbi
Ba ta takowa sai ta cikinta
Sai shirwa ita dai tayi fige
Kan ta shigo daki sai ta sata
Ratata, sarkin magana ce
Tun daga nesa, kana jin kanta
In maganar mace tayi yawa, kaji
Tun daga nesa, kana jin kanta
Wannan mata, tayi hasara
Sai a nada mata sarki wauta
Sai Malali, ita dai tayi kwance
Ta ki ta tashi, ta nemi na kanta
Ba ta kadi, kuma bata sanaá
Sai na mijinta, ya bata, ta sata
Sai ta cikon shida, mai mulkin kai
Ba mai sa ta, bare shi hana ta
Aure ne, ni nis sa kaina
In ka matsa mani, in tafiyata
To shida ta cika ban kara ba
Akwai saura, amma na takaita
Akwai saura, amma na kaita
Ka shaida akwai mata masu kazanta
In mace ta zam bata da tsafta
wannan kam, ta cuci mijinta
Yin tsafta, ta jiki da tufafi
Shine ke hana yadon cuta
Wadda ta zam, bata wanke tufa ba
Shike shaida, anga kazanta
Zani tuna muku in kun manta
Kashedi, da mata masu kazanta
Sun gaza wanke tufa da tukwane
Sun ki kula da abinci su kyauta
Ta gaza share cikin dakinta
Balle na mijinta, bale fuskatta
Kun ji isharata ku kiyaye
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai barna ga mazaje
Zamu fada musu, don su raga ta
Wadansu maza dauka da ajewa
Sun dauko mace, sai su aje ta
Ba laifin tsaye, babu na zaune
Sai kaga basu zuwa dakinta
Ran aikinta ba zai fara'a ba
Ko magana tai, bashi kulawa
Duk namijin da ya dau kwanan wata
In ya hana mata, don bai son ta
Yaki bsatun Allah da maáiki
ya kashe kansa, saboda mugunta
Mata gunku amanar Allah ce
Don Allah maza ku rike ta
In mace tai maka laifi daure
Sai ka tuna, ai kai ka aje ta
Su mata halinsu mugunta
Sai dai-dai ke, basu da keta
Macce, mijinta ko sarki ne
bata yaba masa, sai in bata
Macce mijinta ko malam ne
Bata yabonsa tace da nagarta
Tana iya cewa miji mataulaci
Koda yayi kudin Dantata
Su ka bugu su riga kai kara
Ba ai magana ba su je su tsirata
In mace ta shirya maka karya
Ko boka kam, bashi iyata
Macce tana shiryawa mijinta
Karya, don ya bari tayi cuta
Tâce mashi zata gidan kanwarta
Ko kuma zata ta gaida uwaye
Ta fita, ta samu ta sulale
Ta shiga yawo santa-santa
Ba ta gidan iya, bata na Baba
Kaji nufinta ta sheke ayarta
Don haka mata, ba'a iya musu
In kaji sun magana ka aje ta
Kowace mata na da halinta
Wadansu da kyau, wasu ko da mugunta
Wata in suka fara fada da mijinta
Sai ta rike shi, tace ya kasheta
In kuma yaki ta kama tufarsa
Ace ta sake shi, tace ya kasheta
Ko kuma yanzu ka bani takarda
In kuma ka ban in ketata
In kuma kace anshi takardar
Sai kaji tace, bani riketa
Ita dai sababi ta ka so ta aza mai
Indai yace bashi sakinta
In ka hada ta da Allah sannan
Tafi matsa maka don tsiwarta
Kai kuma gaka kana jin kunya
Ga shari'a ka zage ka kasheta
Don haka sai kowa yayi sannu
Ya nemi hali mai kyau da nagarta
Ba'a sayan mota don kyanta
Sai kaya, da gudu, da nagarta
To haka ne mace, komi kyaunta.
Indai babu hali da nagarta
Kamar mota take komi kyaunta
Indai ba tafiya, bari sonta
Kyan ladabin mace tai wa mijinta
In taki ya mishi, ta kashe kanta
Kui ladabi mata ku kiyaye
aure ba'a gama shi da bauta
In mace tai ladabi ta kiyaye
Allah sarki, shi ka biyanta
Ku mata ku jiya, ku kiyaye
In kuma kun ki, kui mahukunta
Ran mutuwa, da gamo, da kasawa
Sai a tuna maka, in ka mance
In mace tabi mijinta da gaske
Tayi hakuri ta tsaya dakinta
Bata ganin wani banda mijinta
Allah zai mata, babbar kyauta
Miji babban abune bi mjinki
Dai na ganin waccan da mijinta
Bishi, ki so shi, ki bar raina shi
Ko shine sarkin matalauta
Don ki sani Allah ya aza mai
Shi aza masi, shi zai kyauta
Shi abu duk aikin Allah ne
Allah shike bada wadata
Ya kasa bayi fanni-fanni
Shi yai ma'azurta, yai matalauta
In niyyarki gudun matalauta
Sai ya so sannan ki wadata
Shi Allah ba ai masa wayo
Yanda yaso, haka za shi hukunta
Ki hakuri ki tsaya ga mijinki
In ya wadatu, sai ki wadata
Ya Allahu muna rokonka,
ya Allah ka bamu wadata
Ka bamu abinci ckin suturarmú
Allah kadda ka nufe mu da sata
Duk makiyanmu aza mu akansu
Duk sharrin da su kai da mugunta
Ka daukaka addini bisa komai
Ya Allahu bidia ka kashe ta
Kai tsira ga Muhammadu Ahmadu
Don dakin makka, don siffatai
Sahabi nabiyu, da ahlil baiti
Ahlil abaí kaza makusanta
Bismillahir Rahmanir Rahim
Wasallallahu ala Nabiyul Karim
To bismiLlah Allah Sarki
Mai abu mai komai mai kyauta
Bani zalaka, bani fasaha
Inyi bayani na, a fahimta
Zanyi bayani halin mata
Zani rubuta, don a karanta
Kasan mata sun kasu ukku
Zo kusa in na fada ka rubuta
Akwai mata mai tsoron Allah
Bata nufin kowa da mugunta
Akwai wata ga barna ga gyara
Gata da saukin kai ga cuta
Sai ta ukunsu gadangama kenan
Bata nufin gyara sai cuta
Bata nufin hairi ga mijinta
Baga kiyoshi,ba ga makwabta
Bata nufin gyara sai barna
Sai duk safe ta cuci mijinta
Ya tafi office kokuma kanti
Bata kara zama dakinta
In mai noma ne ko zage
Ya tafi gona, zaure za ta
Tana nema taga masu wucewa
Wai ita dai suga kyan fuskarta
In taga sunki shiga harkarta
Sai kaji tace zata makwabta
Kaji irin halayen mata
Munana,manyan, makwadaita
In mace bata da kunya barta
Kama da miya,in ba gishirinta
In mace bata raga maka barta
Daina nufinta kabar sha'awarta
In mace ta zama bata ragama
Ko ka sota, kana kuma kinta
In mace, shashanci ya gameta
Ba mai kara ganin kirkinta
Bata nufin Allah da Ma'aiki
Sai bidi'a ita ke ka gunta
Taji ana Biko tai mika
Sai kaji tace Biko zata
Ba dangin iya babu na Baba
Ko kace ta bari, can zata
Wannan mace,ba mace ce ba
Dai na nufinta kabar sha'awarta
Natsuwa itace mace,ko yar wace
In kaga ba natsuwa,ka bajeta
Kasan mata sun iya karya
Sun iya yadda suke shirgata
Ba duk mace ke son addini ba
Nufinsu a basu kudi, su bukata
Matar da ta zam bata san Allah ba
Ba ta kara zama dakinta
Sai ta fito a tashar Takatale
Sai tai batsa gaban kanwarta
In kace mata, wance ki lura
Baka hana ni bugun cinyata
Babu ruwanta da kunya faufau
Ga Ashar, ko ciwake yana kunyarta
Sanarwata itace ga mazaje
Kar a yawaita kwadai, a takaita
Aure ba abu ne ba na wasa
Bar neman kyau, nemi nagarta
Ni nasan mace, komi kyaunta
Indai babu hali da nagarta
Kana sha'awarta, kana kuma sonta
Badan Allah ba kana kyale ta
Don haka, tun farko ka tsaya tsaf!
Kai nazari da irin halinta
In mace ta zama, shagiri girbau
Ko ka aureta, baka iyata.
Kun ji mazaje, kar ku kiya man
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai mata na nan su shidda
Zo kusa inna fada ka jimilta
Akwai dibgau! Mai dibge mijinta
Ba ta jira ga fada shi taya ta
Danbago, mai zurfin tumbi
Ba ta takowa sai ta cikinta
Sai shirwa ita dai tayi fige
Kan ta shigo daki sai ta sata
Ratata, sarkin magana ce
Tun daga nesa, kana jin kanta
In maganar mace tayi yawa, kaji
Tun daga nesa, kana jin kanta
Wannan mata, tayi hasara
Sai a nada mata sarki wauta
Sai Malali, ita dai tayi kwance
Ta ki ta tashi, ta nemi na kanta
Ba ta kadi, kuma bata sanaá
Sai na mijinta, ya bata, ta sata
Sai ta cikon shida, mai mulkin kai
Ba mai sa ta, bare shi hana ta
Aure ne, ni nis sa kaina
In ka matsa mani, in tafiyata
To shida ta cika ban kara ba
Akwai saura, amma na takaita
Akwai saura, amma na kaita
Ka shaida akwai mata masu kazanta
In mace ta zam bata da tsafta
wannan kam, ta cuci mijinta
Yin tsafta, ta jiki da tufafi
Shine ke hana yadon cuta
Wadda ta zam, bata wanke tufa ba
Shike shaida, anga kazanta
Zani tuna muku in kun manta
Kashedi, da mata masu kazanta
Sun gaza wanke tufa da tukwane
Sun ki kula da abinci su kyauta
Ta gaza share cikin dakinta
Balle na mijinta, bale fuskatta
Kun ji isharata ku kiyaye
Ku lura da duk farkon maganata
Akwai barna ga mazaje
Zamu fada musu, don su raga ta
Wadansu maza dauka da ajewa
Sun dauko mace, sai su aje ta
Ba laifin tsaye, babu na zaune
Sai kaga basu zuwa dakinta
Ran aikinta ba zai fara'a ba
Ko magana tai, bashi kulawa
Duk namijin da ya dau kwanan wata
In ya hana mata, don bai son ta
Yaki bsatun Allah da maáiki
ya kashe kansa, saboda mugunta
Mata gunku amanar Allah ce
Don Allah maza ku rike ta
In mace tai maka laifi daure
Sai ka tuna, ai kai ka aje ta
Su mata halinsu mugunta
Sai dai-dai ke, basu da keta
Macce, mijinta ko sarki ne
bata yaba masa, sai in bata
Macce mijinta ko malam ne
Bata yabonsa tace da nagarta
Tana iya cewa miji mataulaci
Koda yayi kudin Dantata
Su ka bugu su riga kai kara
Ba ai magana ba su je su tsirata
In mace ta shirya maka karya
Ko boka kam, bashi iyata
Macce tana shiryawa mijinta
Karya, don ya bari tayi cuta
Tâce mashi zata gidan kanwarta
Ko kuma zata ta gaida uwaye
Ta fita, ta samu ta sulale
Ta shiga yawo santa-santa
Ba ta gidan iya, bata na Baba
Kaji nufinta ta sheke ayarta
Don haka mata, ba'a iya musu
In kaji sun magana ka aje ta
Kowace mata na da halinta
Wadansu da kyau, wasu ko da mugunta
Wata in suka fara fada da mijinta
Sai ta rike shi, tace ya kasheta
In kuma yaki ta kama tufarsa
Ace ta sake shi, tace ya kasheta
Ko kuma yanzu ka bani takarda
In kuma ka ban in ketata
In kuma kace anshi takardar
Sai kaji tace, bani riketa
Ita dai sababi ta ka so ta aza mai
Indai yace bashi sakinta
In ka hada ta da Allah sannan
Tafi matsa maka don tsiwarta
Kai kuma gaka kana jin kunya
Ga shari'a ka zage ka kasheta
Don haka sai kowa yayi sannu
Ya nemi hali mai kyau da nagarta
Ba'a sayan mota don kyanta
Sai kaya, da gudu, da nagarta
To haka ne mace, komi kyaunta.
Indai babu hali da nagarta
Kamar mota take komi kyaunta
Indai ba tafiya, bari sonta
Kyan ladabin mace tai wa mijinta
In taki ya mishi, ta kashe kanta
Kui ladabi mata ku kiyaye
aure ba'a gama shi da bauta
In mace tai ladabi ta kiyaye
Allah sarki, shi ka biyanta
Ku mata ku jiya, ku kiyaye
In kuma kun ki, kui mahukunta
Ran mutuwa, da gamo, da kasawa
Sai a tuna maka, in ka mance
In mace tabi mijinta da gaske
Tayi hakuri ta tsaya dakinta
Bata ganin wani banda mijinta
Allah zai mata, babbar kyauta
Miji babban abune bi mjinki
Dai na ganin waccan da mijinta
Bishi, ki so shi, ki bar raina shi
Ko shine sarkin matalauta
Don ki sani Allah ya aza mai
Shi aza masi, shi zai kyauta
Shi abu duk aikin Allah ne
Allah shike bada wadata
Ya kasa bayi fanni-fanni
Shi yai ma'azurta, yai matalauta
In niyyarki gudun matalauta
Sai ya so sannan ki wadata
Shi Allah ba ai masa wayo
Yanda yaso, haka za shi hukunta
Ki hakuri ki tsaya ga mijinki
In ya wadatu, sai ki wadata
Ya Allahu muna rokonka,
ya Allah ka bamu wadata
Ka bamu abinci ckin suturarmú
Allah kadda ka nufe mu da sata
Duk makiyanmu aza mu akansu
Duk sharrin da su kai da mugunta
Ka daukaka addini bisa komai
Ya Allahu bidia ka kashe ta
Kai tsira ga Muhammadu Ahmadu
Don dakin makka, don siffatai
Sahabi nabiyu, da ahlil baiti
Ahlil abaí kaza makusanta
Wednesday, April 18, 2007
MAIGANJI; Daga Malam Muhammadu Namaiganji
Ba dai wani takamaimiyar magana, akan kowanene Malam Muhammadu Na Maiganji, ba kuma tabbacin lokacin da ya rubutata. Amma insha Allah, zan kawo cikakken bayani a gameda wakar ta Maiganji. A yanzu dai ga wakar Maiganji
Bi Bismillah ni bawa, na far yabo ga mai baiwa
Arrahmani baiwarsa, gamamma ce ga dan kowa
Rahmani ya kebe baiwarsa, baya yiwa majusawa
Allahu yai dadin tsira, ga Ahmadu shugaban kowa
Baicin ambaton Allah, nufina gargadin kowa
2]Wanda ya yada addini, baya tambayar kowa
Girman kai ya debe shi, ya sashi ya fandare wawa
Yaku yan uwa dangi, Allah ya halicce mu
Domin tsaida addini, Tawhidi kaza Sallah
Musan Azumi da Zakkarmu, kaza Hajji wajibin kowa
3]Mu sansu, mu sanda yayanmu, kaza matanmu bayinmu
Kanko mun ki sanasshe su, ranar lahira ka sani
Acan aka tambayar kowa, akan doran siradinsa
Ga kaifi, ga makonansa, Kama nan za'a tsaishe ka
Idan yazo dasu ya shige, idan bai zo da kome ba
Wa'ila sai su turo shi, cikin zurfin wuta wawa
4]Bayi na ciki su cane, ya kaitonka kai bawa
Ina halinku ma'aikinku, ya kance 'sun isar da sani'
Iyaye sun ka bashe mu, suna aikin majusawa
Kan ance da su su bari, su kance 'mu iyayenmu
Mun same su sun aika, abinda su kanyi shi zamu bi, bama jin fadar kowa
5]Ka duba can ga kakanku, , Adamu, Nuhu, Idrisu
Da Ibrahim uban kowa, Manyan Annabawa ne
Sun bi fada ta Allahu, tazo har kan ma'aikinmu
Kowak ki ta ya ratse, yabi fadar Yahudawa
6]Yahudu, Nasara sun ratse, shaidani ya rude su
Yace ku tsaya a nushe ku, ga aikin iyayenkuAbin bautarsu su gunki, gama shine mashasharku
Kar ku bi annabin kowaYa jama'a ta addini, bin Allah farillansa
Bin manzo cikin sunna, wanda ya yada bin sunna
Kamar bai aika komai ba, kamar dai wanda yai sallah
Bai zakka ba ya tabe, cikin bin Jallah mai baiwa
7]Wanda ya bauta Allahu, yana sabon iyayensa
Bai karba ba sarkinmu, ka tuba ka bisu kai wawa
Ya mai bauta Allahu, nemi halas abar cinka
Kan ko tabe, haramun wanda ya cita
Misalin gwargwadon lauma
Kwana Arba'in za ai, yana bauta ga sarkinmu
Bai karba Allahu, Jallah ubangijin kowa
8]Ina Malam, Ina Malam Malam tsorci Allahu
Kabar tsoron mutanenka, fada musu gaskiya hakkan
Kan sun bita ka huta, kan sun ki ta ka kubuta
Wurin Sarkinmu Allahu, Jallah Karimu mai baiwa
9]Zan muku gargadi dangi
Ku kai yayanku gun malam
Karatu wajibin kowa
10]Wanda ya samu da nasa, Yaki ya kai shi gun malam
Ya dau alhakin dan sa, Yahudu, Nasara sun samu
Kaza suma majusawa, Kowanne da
Ka haifeshi, duk jama'ar Ma'aikine
Sai babansa yaki shi, yakan koma Nasarawa
11]Malam nemi sarkinka, kace masa yai fadan bidi'a
Bidi'a kishiyar Sunna, kowab bita y rates
Yabi fada ta shaidani, yaki fadar ma'aikinmu
Muhammadu Annabin kowa, wanda yabar fadar MammanYana nushe shi kan turba, Yana kimso cikin jeji, yana yawo kamar giwa
12]Mai yawo cikin jeji, kan yaje cikin jama'a
Mazaje masu bin Allah, suna taro gidan malam
Ko jam'a ta yin sallah, baka ga shi baya sheka yana cigiyar, bata wawa
Koda nace, da ko daji, ba daji na kura ba
13]Ko acikin gidnsa yake, yaki yaje gidan malam
Shi san Allah, bazai Sallah, kace masa
Mai shiga jeji, zaya bace cikin njeji, Babu gudunmawar kowa
Maza mata ku nemi, fada tasa shugaban kowa
14]Wanda ya bar fadar Mamman, yaki fada ta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, Wanda yabar fadar Allahu
Ya kafirta ya watse, yabi safun
Abu Jahalin, Abu Lahabin da wansunsu
Yana koyi da su wawa
15] Ya jama'ar musulminmu, mai kaunar yasan Rahma
Yabar aure cikin idda, Allah bai hallata ba
Ma'aiki bai halatta ba, Malam ya cane ka bari
Kana yi kaito kai wawa
Mutum uku munji sun rates, limamin da ya daura
16]Waliyin wanda ya aiko, da mai nema cikin idda
Sun ko sun ki bin turba, Ta annabi shugaban kowa
Su duka mun ji sun ratse, da wadda ta karkace idda
Har jama'ar da tai shaidar, asasu wuta
Cikin karfe, su kuna ba ruwan kowa
17]Inai muku gargadi dani, maso jinkai
Ya same shi, Yai auren halaliya
Ya dauki ruwa da gammonsa, ko ya saya
Da kurdinsa, Ruwan wankanta ko sallah
Hadisin shugaban kowa.
18]Wajibne ga da namiji, yai bauta ga matansa
Kadan yalwa ta same shi, kadda su durkusa
Dutse, Ni fan day a bare mai yawa
Fadar nan duk da nayita, nib a shisshigi
Nai ba, ka bi ta kabar batun kowa
19]Wanda ya kama matansa, da cinsu da shansu ya dauka
Yana yi gwargwadon iko
Tamkar wanda yai sadaka, har ma yafi mai sadaka
Wurin sarkinmu Allahu
Jalla karimu mai baiwa
20]Ka nemi halas ka cishe su, Allah zai biya kowa
Kadda ka nan haraminya, kowac cita ya kuna
Sai ya tuba ya barta, Rahimu ya maida jinkansa
Allah Rahimin kowa
Yaku masu bin bidi'a, da kun tuba kun barta
21]Kun bi fadar ma'aikinmu, bin farali da bin sunna
Kowa mai hana ku barin, Yalwa sai ta same ku
Dabbobi sa wadaceku, Kishirwa babu
Ko yunwa, bare yafi ya daukeka
Bare bautar Nasarawa
22]Ku shirya zasu bashe ku, kui damara ta bin
Mamman, ku tserewa Nasarawa
Ku bar waka ta shaidani, kui zikiri na bin Allah
Halshe an halitta shi, dan zikiri
Da yin kalma, ku bar zagin ubankowa
23]Ku bar zambon iyayenku, Gwarabjawa
Da Maiganji, ku tuba ku bar gamin kowa
Mai zagin iyayensa, mu mun sami labari
Can a wutar Yahudawa
24]Mu mun sami labariAcan a can a wutar Yahudawa
Macizai har kunaminta, suna dako su cije shi
Kan sun sami bakinsa
Sukan kama suna yago,
Su kan taye kamar yawa.
25]Kunaminta na harbi dubu saba'in,
Karin nasu gaba daya zsu soke shi
Su zarta jikin maki Allah, masabin dan Kuraishawa
Muhammadu wanda yaki ka, shi darajarsa ta tauy
Anan duniya gidan Darbashan, inda Dayyanu mai sakawa dan kowa
26]Ina makadi maki Allah, da shi da ubansa shaidani
Da mai murnar abinda su kai, Allah ya la'ance su
Ma'aiki ya la'ance su, Mala'iku na Allah suma
Sun la'ance su, mutane masu bin sunna
Suma sun la'ance su
27]Kifi maigida a ruwa, shima ya la'ance su
Tsuntsu maigida a sama, shima ya la'ance su
Duk bayio na Allahu, basu san su
Domin kinsu bin Allah
Ta'ala wanda yai kowa
28]Mai ganga maki Allah, kan ya dauki Gangarsa,
Ya kanje dandali nasa
Shaidani yakan tashi, yana gayya gidan kowa
Kowa amsa gayyarsa, can zai kaishi gun gayyu
Shiko Gayyu Zaza ne, cikin zurfin wuta wawa
29]Kowa tuba ya huta, Allah rahimin kowa
Ku tuba ku daina yin bidi'a, Allah ya jikan kowa
Ina makadi uban bidi'a, mai sababinka kin Allah
Yai maka hannu da kafa, ya baka idanu da kafa
Da baki duk da kunnenka, wa zai kirga baiwarsa da yai maka ja'iri wawa
30]Kaki ka gode baiwarsa, menene tsakaninku
Kana bijirar da bayinsa, kana ta kidi suna waka
Kana bauta ga shaidani, kun ki ku bauta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, ku bar bauta ga shaidani
Nufinsa yaje ya yashe ku, ya kai ku cikin wuta wawa
31]Ina makadi uban bidi'a, da kun tuba kun bit
Allah sai ya yafe ku, Rahimu Ubangijin kowa
Kan ance su bar Bidi'a, su kan ce tun iyayensu
Da kakanni ake yinta, shi sabonsa
Tun nan, basa jin fadar kowa
32]Ku duba tun iyayenku, da kakannin iyayenku
Sha sabon karatun nan, suka tarda shi wawa
Ina jin tausayin dangi, basa tausayin kansu
Sun ki su kama bin turbar
Muhammdu shugaban kowa
33]Fitar mata zuwa jeji
Suna nema da dan gyaftoSuna cin kasuwar lahadi...........
34]Yaya ne ka auro su, ba bayi ka auro ba
Kabar su suke fita yawo, tsorci
Ubangiji Allah, Ta'ala wanda yai kow
Ko bayi ka same su, kanka bukace su
Auransu kadda ka bar su su yawo, fada ta ubangijin kowa
35]Kuna cewa iyayenku, basu bada su da ka-
Kanninku, Addini na Ibrahim, yai tsari ga matansa
Sahhabai dukka sunyi tsari, dan kakanku yaki tsari
Ba sauki akai masa ba
Shi ne yaki bin turbar Annabin kowa
36]Fadar Allah Ta'ala ce, zaman mata cikin daki
Kun ki fada ta Allahu, kuke fusshesu gun narko
Bar kallon fadar Allah, ko sarkin kasa ya fadi
Kan ka ki ta ka tashi, gidanka
Da shi da gonarka, don ka barshi bayanka
37]Ka sheka kana yawo, cikin ZazzauKaza
Katsina, ko birnin Kazaurawa
Kamarka mutum kakewa gudu
Ka rasa zamna gidanka
In ka ki fadar Allah, ina magudarka kai wawa?
38]Mala'iku su kamo ka su saka
A sasarin karfe, a sundukin bakin karfe
Sai ka tuba ka barsu, kai hakuri
Da noman so, Allah sai ya yafe ka
Domin bin uban Kasim, jikin Hashimiyawa
39]Ina mai annamimanci, da mai hassada
Da mai ruwa, da mai zina ja'iri bawa
Da mai suka ga addini, da mai gaba
Da malumma, da mai karya cikin jama'a
Da mai zuku yana tazidu............
40]Mai zina ya shiga ya shiga uku, radda ka tada yan adam
Da aljannai da wansunsu, du da mala'ikun Allah
Ana kallonsa duk jama'a, yayi baki bakin zunubi
Kai kace bakin wawa
Da shi da abokiyar la'ana, gabanta kamar ruwan miki
41]Tana yoyo cikin jama'a, kamar randa data burme
Ga doyi kamar kuna
Kaman nan zai kusance ta
Yana lasa da bakinsa
Kamar lasar kare wawa
42]Jahannama can tana dako
Akai mata jairin bawa, maki sarkinmu Allahu
Maki jin gargadin kowa
Mai riya zamu zancansa, maki zancen
Ma'aikinmu, maki jin gargadin kowa
43]Manzo ya cane ya bari, Shirka ce wurin Allah
Shiko yaki mai shirka
Wanda ya bada kayansa, don a fada a cane
Wane, jikan wane, dan wane
Shaidani ya rude shi, don ya batar da shi Wawa
44]Shi bai nemi lada ba, wurin sarkinmu Allahu
Shi dai duniya ta fadi, suit a yabonsa yan
Adam, sun ace ba kamar wane, domin
Sunga wawa ne, shi bai san da karya ba
A’a ya sani it ace, yake bautar kwanikawa.
45]Ina wawa maki turba, fahimci abinda za
Ni fadi, Allah ya halitto ka, dan bautarsa
Ka ki sani, kana neman taro da kwabo
Kaki ka nan shinan Sallah, bar kallon taro da Kwabo
Ko kasan Sule da Dala, ko rumbu guda ka cika, sai wata ran mala’ika, ya dauke ran yabar gawa.
46]Su kai ka su sa cikin rami rami, su lullube
Yar kasa su rufe, su juya can wurin karfe
Suna ta raba sub a naka, Anini guda
Basa baka, Kwabo ma yafi karfinka
Kanan shinan Sallah sai itace, wurin bawa cikin kabarinsa kai wawa
47]Ku san neman taro da kwabo, halaline wurin Allah
Kan ka san shinan Sallah, kadan ko ba shinan
Sallah, haramunce gad an kowa
Allah yayi wo bawa, dan bautarsa kai wawa
Kai ko ka ki bautarsa, dan neman taro da kwabo, ka duba arzikin bawa
47]Rababbe ne wurin Allah, abinda ya bashi ya bashi
Da zai hau samaniya yana neman dadi
Babu yace ya gode mai baiwa
Godewa ga sarkinmu, bin sa da
Bin ma’aikinmu, da bin ulama’u kai wawa
48]Lura fadar da nai bawa, kan ka kita ka tabe
Ba azumi bare sallah, duk aikin addininka
Ba lada wurin Allah, sai ka tambayo malam
Allah yaki addinin
Da ba’a tambayar kowa
48]Azaba can tana dako, ga bawa wanda yaki sani
Kamanan wanda yayi sani, baya aiki da shi
Wawa ku bar wasa ku nemi sani
Said a sani ake samun gidan Rahma
Wurin Sarkinmu Allahu, Ta’alas wanda yai kowa
49]Ana wa’azin bakin bawa, dillalin bakin bawa
Wanda yaje cikin kurmi, yana yawo da ka-
Yansa, kan ace da shi ya cira, yakan ce
Yafi karfinka abinda akan tayi goma, yakan ce Sha Biyar ka taya,
Ba tsoro bare kunya, yaki fadar ma’aikinmu, bare maganar ubankowa.
50]Kiyayi riba haramunce, wanda ya cita zai kone
Ka tsoraci ubangiji Allkah, Tabaraka wanda yai kowa
Karya ma haramunce, kabar san yenta kai wawa
Mai karya cikin jama’a, shi kan keta bakinsa
Yakan je har zuwa keya, kadan karyarsa ta shahara
51]Allah ya la’ance shi, a sa la’ana a goshinsa
Kowag ganshi ya san shi
Duk dabbar gida da dawa, kan tag an shi ta san shi
Ta ce Alhamdu lilLahi ni nagode sarkinmu
Tunda yayi ni ni dabba, naïf makaryacin bawa, mugu fajiri wawa
52]Ina bawan dake hassada, ya tuba ya daina yin hassada
Kan ko yaki ya kone, yana haushin
Rabon Allah, zato nasa ja’iri wawa
Zani yabon ma’aikinmu, tsattsarka uban Kasim
Baban Fadima Zahra, mai hakuri uban dayyabu, Sidi Balaraben kowa
53]Mai haske da kyau Mamman, Mai saje da kyawun
Fuska, gashi da kyan bakin gashi, bashi da furfura
Da yawa, cikin sajensa har gemu
Kan ka san guda goma, kana neman biyar ka dada
Baka samu ba sai ka tsaya, kana kallon wushiryarsa
54]Ga haske yana tashi, turare ma yana tashi
Kamshi ya buche kowa
Ana ajabi da sawunsa, Kan ya taka kan dutse
Wurin takun yakan gurbi, kan ya taka
Rairansa, baka gurin ba yai gurbi, hukumcin Jalla mai baiwa
55]Dadai ka gani bawa, yadda ka tsaida yan adam
Wurin ikonsa Sarkinmu, ranar kaga jayayya
Iyayensu da yayansu, mazaje su da matansu
Sarki shi da fadawa, dogarrai da sauransu
Har da yace da babansa, kai ka batar dani Turba
56]Kana ji na ina ihu, nakan zallko ina juya
Kai ko ka ki yin tsawa
Kowa ya kira dansa, yana nusheshi
Bin turba, kai ko ka ki nushe ni
Bare nabi annabin kowa
57]Ina Magana ga dattijo, tunda ya bar fadar Mamman
Ya ki fada ta Allahu, jallah ubangijin kowa
Yara su da manyansu, kan suka dubi kankanci
Su kance Rabbu sarkinmu, mun bi ta
Shugabanninmu, su suka bi damu turba
58]Rabbu ka fara bashes u, sui nisa da jinkanka
Jallah ubangijin kowa
Wadanga da su da manyansu, jayayya takan
Rude, sukan ce mu musulmi ne
Bad an ku ba manyanmu, su suka ce da su a’a, …………
59]Sukan ce ba Kaman nan ba, ko kace mu bar turba
Mui bautar wanin Allah, ace fa su daina jayayya
Akai su wutar Nasarawa, fadar wa’azi da nai dangi
Don mai hankali na fadi, koda nace daku waka
Tunda ya sa dani acikin, musulmi masu san baiwa
60]Acikin mutane masu yin Sallah
Suna karbar fadar Mamman, Sidi balaraben kowa
Salatin Lahi Sarkinmu, ya tabbata
Ya tabbata nan ga manzonmu
Muhammdu mai dubun baiwa
61]Da aloli da as’habu, damu mabiya umarninsa
Ana ranar dab a bawa, mai debe kewa
Kan ance daku waka, wanene matsarinta
Ku ce masu kankanin bawa, malacin gayyi
Aikin karatu ya buwaye shi, na Qur’ani kaza ilimu, sai sururi abin wawa
62]Cikakken hankalin bawa, yai sauki da surutu
Sakankance da wautarsa,
kan ya yawaita surutu
cikin taro, wajen jama’a
Ku taru gidan zaka wawa.
Bi Bismillah ni bawa, na far yabo ga mai baiwa
Arrahmani baiwarsa, gamamma ce ga dan kowa
Rahmani ya kebe baiwarsa, baya yiwa majusawa
Allahu yai dadin tsira, ga Ahmadu shugaban kowa
Baicin ambaton Allah, nufina gargadin kowa
2]Wanda ya yada addini, baya tambayar kowa
Girman kai ya debe shi, ya sashi ya fandare wawa
Yaku yan uwa dangi, Allah ya halicce mu
Domin tsaida addini, Tawhidi kaza Sallah
Musan Azumi da Zakkarmu, kaza Hajji wajibin kowa
3]Mu sansu, mu sanda yayanmu, kaza matanmu bayinmu
Kanko mun ki sanasshe su, ranar lahira ka sani
Acan aka tambayar kowa, akan doran siradinsa
Ga kaifi, ga makonansa, Kama nan za'a tsaishe ka
Idan yazo dasu ya shige, idan bai zo da kome ba
Wa'ila sai su turo shi, cikin zurfin wuta wawa
4]Bayi na ciki su cane, ya kaitonka kai bawa
Ina halinku ma'aikinku, ya kance 'sun isar da sani'
Iyaye sun ka bashe mu, suna aikin majusawa
Kan ance da su su bari, su kance 'mu iyayenmu
Mun same su sun aika, abinda su kanyi shi zamu bi, bama jin fadar kowa
5]Ka duba can ga kakanku, , Adamu, Nuhu, Idrisu
Da Ibrahim uban kowa, Manyan Annabawa ne
Sun bi fada ta Allahu, tazo har kan ma'aikinmu
Kowak ki ta ya ratse, yabi fadar Yahudawa
6]Yahudu, Nasara sun ratse, shaidani ya rude su
Yace ku tsaya a nushe ku, ga aikin iyayenkuAbin bautarsu su gunki, gama shine mashasharku
Kar ku bi annabin kowaYa jama'a ta addini, bin Allah farillansa
Bin manzo cikin sunna, wanda ya yada bin sunna
Kamar bai aika komai ba, kamar dai wanda yai sallah
Bai zakka ba ya tabe, cikin bin Jallah mai baiwa
7]Wanda ya bauta Allahu, yana sabon iyayensa
Bai karba ba sarkinmu, ka tuba ka bisu kai wawa
Ya mai bauta Allahu, nemi halas abar cinka
Kan ko tabe, haramun wanda ya cita
Misalin gwargwadon lauma
Kwana Arba'in za ai, yana bauta ga sarkinmu
Bai karba Allahu, Jallah ubangijin kowa
8]Ina Malam, Ina Malam Malam tsorci Allahu
Kabar tsoron mutanenka, fada musu gaskiya hakkan
Kan sun bita ka huta, kan sun ki ta ka kubuta
Wurin Sarkinmu Allahu, Jallah Karimu mai baiwa
9]Zan muku gargadi dangi
Ku kai yayanku gun malam
Karatu wajibin kowa
10]Wanda ya samu da nasa, Yaki ya kai shi gun malam
Ya dau alhakin dan sa, Yahudu, Nasara sun samu
Kaza suma majusawa, Kowanne da
Ka haifeshi, duk jama'ar Ma'aikine
Sai babansa yaki shi, yakan koma Nasarawa
11]Malam nemi sarkinka, kace masa yai fadan bidi'a
Bidi'a kishiyar Sunna, kowab bita y rates
Yabi fada ta shaidani, yaki fadar ma'aikinmu
Muhammadu Annabin kowa, wanda yabar fadar MammanYana nushe shi kan turba, Yana kimso cikin jeji, yana yawo kamar giwa
12]Mai yawo cikin jeji, kan yaje cikin jama'a
Mazaje masu bin Allah, suna taro gidan malam
Ko jam'a ta yin sallah, baka ga shi baya sheka yana cigiyar, bata wawa
Koda nace, da ko daji, ba daji na kura ba
13]Ko acikin gidnsa yake, yaki yaje gidan malam
Shi san Allah, bazai Sallah, kace masa
Mai shiga jeji, zaya bace cikin njeji, Babu gudunmawar kowa
Maza mata ku nemi, fada tasa shugaban kowa
14]Wanda ya bar fadar Mamman, yaki fada ta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, Wanda yabar fadar Allahu
Ya kafirta ya watse, yabi safun
Abu Jahalin, Abu Lahabin da wansunsu
Yana koyi da su wawa
15] Ya jama'ar musulminmu, mai kaunar yasan Rahma
Yabar aure cikin idda, Allah bai hallata ba
Ma'aiki bai halatta ba, Malam ya cane ka bari
Kana yi kaito kai wawa
Mutum uku munji sun rates, limamin da ya daura
16]Waliyin wanda ya aiko, da mai nema cikin idda
Sun ko sun ki bin turba, Ta annabi shugaban kowa
Su duka mun ji sun ratse, da wadda ta karkace idda
Har jama'ar da tai shaidar, asasu wuta
Cikin karfe, su kuna ba ruwan kowa
17]Inai muku gargadi dani, maso jinkai
Ya same shi, Yai auren halaliya
Ya dauki ruwa da gammonsa, ko ya saya
Da kurdinsa, Ruwan wankanta ko sallah
Hadisin shugaban kowa.
18]Wajibne ga da namiji, yai bauta ga matansa
Kadan yalwa ta same shi, kadda su durkusa
Dutse, Ni fan day a bare mai yawa
Fadar nan duk da nayita, nib a shisshigi
Nai ba, ka bi ta kabar batun kowa
19]Wanda ya kama matansa, da cinsu da shansu ya dauka
Yana yi gwargwadon iko
Tamkar wanda yai sadaka, har ma yafi mai sadaka
Wurin sarkinmu Allahu
Jalla karimu mai baiwa
20]Ka nemi halas ka cishe su, Allah zai biya kowa
Kadda ka nan haraminya, kowac cita ya kuna
Sai ya tuba ya barta, Rahimu ya maida jinkansa
Allah Rahimin kowa
Yaku masu bin bidi'a, da kun tuba kun barta
21]Kun bi fadar ma'aikinmu, bin farali da bin sunna
Kowa mai hana ku barin, Yalwa sai ta same ku
Dabbobi sa wadaceku, Kishirwa babu
Ko yunwa, bare yafi ya daukeka
Bare bautar Nasarawa
22]Ku shirya zasu bashe ku, kui damara ta bin
Mamman, ku tserewa Nasarawa
Ku bar waka ta shaidani, kui zikiri na bin Allah
Halshe an halitta shi, dan zikiri
Da yin kalma, ku bar zagin ubankowa
23]Ku bar zambon iyayenku, Gwarabjawa
Da Maiganji, ku tuba ku bar gamin kowa
Mai zagin iyayensa, mu mun sami labari
Can a wutar Yahudawa
24]Mu mun sami labariAcan a can a wutar Yahudawa
Macizai har kunaminta, suna dako su cije shi
Kan sun sami bakinsa
Sukan kama suna yago,
Su kan taye kamar yawa.
25]Kunaminta na harbi dubu saba'in,
Karin nasu gaba daya zsu soke shi
Su zarta jikin maki Allah, masabin dan Kuraishawa
Muhammadu wanda yaki ka, shi darajarsa ta tauy
Anan duniya gidan Darbashan, inda Dayyanu mai sakawa dan kowa
26]Ina makadi maki Allah, da shi da ubansa shaidani
Da mai murnar abinda su kai, Allah ya la'ance su
Ma'aiki ya la'ance su, Mala'iku na Allah suma
Sun la'ance su, mutane masu bin sunna
Suma sun la'ance su
27]Kifi maigida a ruwa, shima ya la'ance su
Tsuntsu maigida a sama, shima ya la'ance su
Duk bayio na Allahu, basu san su
Domin kinsu bin Allah
Ta'ala wanda yai kowa
28]Mai ganga maki Allah, kan ya dauki Gangarsa,
Ya kanje dandali nasa
Shaidani yakan tashi, yana gayya gidan kowa
Kowa amsa gayyarsa, can zai kaishi gun gayyu
Shiko Gayyu Zaza ne, cikin zurfin wuta wawa
29]Kowa tuba ya huta, Allah rahimin kowa
Ku tuba ku daina yin bidi'a, Allah ya jikan kowa
Ina makadi uban bidi'a, mai sababinka kin Allah
Yai maka hannu da kafa, ya baka idanu da kafa
Da baki duk da kunnenka, wa zai kirga baiwarsa da yai maka ja'iri wawa
30]Kaki ka gode baiwarsa, menene tsakaninku
Kana bijirar da bayinsa, kana ta kidi suna waka
Kana bauta ga shaidani, kun ki ku bauta Allahu
Ta'ala wanda yai kowa, ku bar bauta ga shaidani
Nufinsa yaje ya yashe ku, ya kai ku cikin wuta wawa
31]Ina makadi uban bidi'a, da kun tuba kun bit
Allah sai ya yafe ku, Rahimu Ubangijin kowa
Kan ance su bar Bidi'a, su kan ce tun iyayensu
Da kakanni ake yinta, shi sabonsa
Tun nan, basa jin fadar kowa
32]Ku duba tun iyayenku, da kakannin iyayenku
Sha sabon karatun nan, suka tarda shi wawa
Ina jin tausayin dangi, basa tausayin kansu
Sun ki su kama bin turbar
Muhammdu shugaban kowa
33]Fitar mata zuwa jeji
Suna nema da dan gyaftoSuna cin kasuwar lahadi...........
34]Yaya ne ka auro su, ba bayi ka auro ba
Kabar su suke fita yawo, tsorci
Ubangiji Allah, Ta'ala wanda yai kow
Ko bayi ka same su, kanka bukace su
Auransu kadda ka bar su su yawo, fada ta ubangijin kowa
35]Kuna cewa iyayenku, basu bada su da ka-
Kanninku, Addini na Ibrahim, yai tsari ga matansa
Sahhabai dukka sunyi tsari, dan kakanku yaki tsari
Ba sauki akai masa ba
Shi ne yaki bin turbar Annabin kowa
36]Fadar Allah Ta'ala ce, zaman mata cikin daki
Kun ki fada ta Allahu, kuke fusshesu gun narko
Bar kallon fadar Allah, ko sarkin kasa ya fadi
Kan ka ki ta ka tashi, gidanka
Da shi da gonarka, don ka barshi bayanka
37]Ka sheka kana yawo, cikin ZazzauKaza
Katsina, ko birnin Kazaurawa
Kamarka mutum kakewa gudu
Ka rasa zamna gidanka
In ka ki fadar Allah, ina magudarka kai wawa?
38]Mala'iku su kamo ka su saka
A sasarin karfe, a sundukin bakin karfe
Sai ka tuba ka barsu, kai hakuri
Da noman so, Allah sai ya yafe ka
Domin bin uban Kasim, jikin Hashimiyawa
39]Ina mai annamimanci, da mai hassada
Da mai ruwa, da mai zina ja'iri bawa
Da mai suka ga addini, da mai gaba
Da malumma, da mai karya cikin jama'a
Da mai zuku yana tazidu............
40]Mai zina ya shiga ya shiga uku, radda ka tada yan adam
Da aljannai da wansunsu, du da mala'ikun Allah
Ana kallonsa duk jama'a, yayi baki bakin zunubi
Kai kace bakin wawa
Da shi da abokiyar la'ana, gabanta kamar ruwan miki
41]Tana yoyo cikin jama'a, kamar randa data burme
Ga doyi kamar kuna
Kaman nan zai kusance ta
Yana lasa da bakinsa
Kamar lasar kare wawa
42]Jahannama can tana dako
Akai mata jairin bawa, maki sarkinmu Allahu
Maki jin gargadin kowa
Mai riya zamu zancansa, maki zancen
Ma'aikinmu, maki jin gargadin kowa
43]Manzo ya cane ya bari, Shirka ce wurin Allah
Shiko yaki mai shirka
Wanda ya bada kayansa, don a fada a cane
Wane, jikan wane, dan wane
Shaidani ya rude shi, don ya batar da shi Wawa
44]Shi bai nemi lada ba, wurin sarkinmu Allahu
Shi dai duniya ta fadi, suit a yabonsa yan
Adam, sun ace ba kamar wane, domin
Sunga wawa ne, shi bai san da karya ba
A’a ya sani it ace, yake bautar kwanikawa.
45]Ina wawa maki turba, fahimci abinda za
Ni fadi, Allah ya halitto ka, dan bautarsa
Ka ki sani, kana neman taro da kwabo
Kaki ka nan shinan Sallah, bar kallon taro da Kwabo
Ko kasan Sule da Dala, ko rumbu guda ka cika, sai wata ran mala’ika, ya dauke ran yabar gawa.
46]Su kai ka su sa cikin rami rami, su lullube
Yar kasa su rufe, su juya can wurin karfe
Suna ta raba sub a naka, Anini guda
Basa baka, Kwabo ma yafi karfinka
Kanan shinan Sallah sai itace, wurin bawa cikin kabarinsa kai wawa
47]Ku san neman taro da kwabo, halaline wurin Allah
Kan ka san shinan Sallah, kadan ko ba shinan
Sallah, haramunce gad an kowa
Allah yayi wo bawa, dan bautarsa kai wawa
Kai ko ka ki bautarsa, dan neman taro da kwabo, ka duba arzikin bawa
47]Rababbe ne wurin Allah, abinda ya bashi ya bashi
Da zai hau samaniya yana neman dadi
Babu yace ya gode mai baiwa
Godewa ga sarkinmu, bin sa da
Bin ma’aikinmu, da bin ulama’u kai wawa
48]Lura fadar da nai bawa, kan ka kita ka tabe
Ba azumi bare sallah, duk aikin addininka
Ba lada wurin Allah, sai ka tambayo malam
Allah yaki addinin
Da ba’a tambayar kowa
48]Azaba can tana dako, ga bawa wanda yaki sani
Kamanan wanda yayi sani, baya aiki da shi
Wawa ku bar wasa ku nemi sani
Said a sani ake samun gidan Rahma
Wurin Sarkinmu Allahu, Ta’alas wanda yai kowa
49]Ana wa’azin bakin bawa, dillalin bakin bawa
Wanda yaje cikin kurmi, yana yawo da ka-
Yansa, kan ace da shi ya cira, yakan ce
Yafi karfinka abinda akan tayi goma, yakan ce Sha Biyar ka taya,
Ba tsoro bare kunya, yaki fadar ma’aikinmu, bare maganar ubankowa.
50]Kiyayi riba haramunce, wanda ya cita zai kone
Ka tsoraci ubangiji Allkah, Tabaraka wanda yai kowa
Karya ma haramunce, kabar san yenta kai wawa
Mai karya cikin jama’a, shi kan keta bakinsa
Yakan je har zuwa keya, kadan karyarsa ta shahara
51]Allah ya la’ance shi, a sa la’ana a goshinsa
Kowag ganshi ya san shi
Duk dabbar gida da dawa, kan tag an shi ta san shi
Ta ce Alhamdu lilLahi ni nagode sarkinmu
Tunda yayi ni ni dabba, naïf makaryacin bawa, mugu fajiri wawa
52]Ina bawan dake hassada, ya tuba ya daina yin hassada
Kan ko yaki ya kone, yana haushin
Rabon Allah, zato nasa ja’iri wawa
Zani yabon ma’aikinmu, tsattsarka uban Kasim
Baban Fadima Zahra, mai hakuri uban dayyabu, Sidi Balaraben kowa
53]Mai haske da kyau Mamman, Mai saje da kyawun
Fuska, gashi da kyan bakin gashi, bashi da furfura
Da yawa, cikin sajensa har gemu
Kan ka san guda goma, kana neman biyar ka dada
Baka samu ba sai ka tsaya, kana kallon wushiryarsa
54]Ga haske yana tashi, turare ma yana tashi
Kamshi ya buche kowa
Ana ajabi da sawunsa, Kan ya taka kan dutse
Wurin takun yakan gurbi, kan ya taka
Rairansa, baka gurin ba yai gurbi, hukumcin Jalla mai baiwa
55]Dadai ka gani bawa, yadda ka tsaida yan adam
Wurin ikonsa Sarkinmu, ranar kaga jayayya
Iyayensu da yayansu, mazaje su da matansu
Sarki shi da fadawa, dogarrai da sauransu
Har da yace da babansa, kai ka batar dani Turba
56]Kana ji na ina ihu, nakan zallko ina juya
Kai ko ka ki yin tsawa
Kowa ya kira dansa, yana nusheshi
Bin turba, kai ko ka ki nushe ni
Bare nabi annabin kowa
57]Ina Magana ga dattijo, tunda ya bar fadar Mamman
Ya ki fada ta Allahu, jallah ubangijin kowa
Yara su da manyansu, kan suka dubi kankanci
Su kance Rabbu sarkinmu, mun bi ta
Shugabanninmu, su suka bi damu turba
58]Rabbu ka fara bashes u, sui nisa da jinkanka
Jallah ubangijin kowa
Wadanga da su da manyansu, jayayya takan
Rude, sukan ce mu musulmi ne
Bad an ku ba manyanmu, su suka ce da su a’a, …………
59]Sukan ce ba Kaman nan ba, ko kace mu bar turba
Mui bautar wanin Allah, ace fa su daina jayayya
Akai su wutar Nasarawa, fadar wa’azi da nai dangi
Don mai hankali na fadi, koda nace daku waka
Tunda ya sa dani acikin, musulmi masu san baiwa
60]Acikin mutane masu yin Sallah
Suna karbar fadar Mamman, Sidi balaraben kowa
Salatin Lahi Sarkinmu, ya tabbata
Ya tabbata nan ga manzonmu
Muhammdu mai dubun baiwa
61]Da aloli da as’habu, damu mabiya umarninsa
Ana ranar dab a bawa, mai debe kewa
Kan ance daku waka, wanene matsarinta
Ku ce masu kankanin bawa, malacin gayyi
Aikin karatu ya buwaye shi, na Qur’ani kaza ilimu, sai sururi abin wawa
62]Cikakken hankalin bawa, yai sauki da surutu
Sakankance da wautarsa,
kan ya yawaita surutu
cikin taro, wajen jama’a
Ku taru gidan zaka wawa.
Tuesday, April 17, 2007
TABARKOKO; Daga Sarkin Zazzau Aliyu Dansidi
Wannan dai itace wakar Tabarkoko, wadda sarkin Zazzau Aliyu Dansidi ya wallafa. Wakar dai gugar zana ce, ko kuma ince shagube da bai nuna wanda yake yiwa ba. Amma ana zaton ko yayi tane domin yiwa fadawansa shagube, game da yadda suke tafiyar da rayuwarsu.
Aboka zo nan mu bata
ka dubi dan dai ga wata
wada daban da batta
Haske na rana da wata
Ba zasu zam daidai ba
He dubi dai tsettsewa
Ya samu kifi a wuya
shina zaton babu kaya
Inta kafe mai ga wuya
ba zasu debe mai ba
He dubi dai irame
Can tai gida a rame
Can dauri kau ta rame
kyaushe mijin Irame
gallonsu ba zaki ba
Abin ga dai gama na
kare shi tono magana
zai iske kura a hana
ba dun akwai wata magana
da bai fito rannan ba
Ai ga fage ga doki
Noman fako ba taki
ai maganan ta sake
da dan kare da na doki
ba zasu zam daidai ba
Mu namu ga ta da taki
babu biri ba zaki
barde dubu mai doki
da zamanin kai taki
da bamu samu nai ba
Saura garin ya waye
duk kokuwan tai kaye
Damu ga yan tawaye
da masu da da maye
zamansu bai zam dai ba
Karya take zabira
bata zama gurara
Iska daban da sarara
matar maza da bera
kudinsu bai zam dai ba
Na ganshi duk ya kwabe
Yayi tabo ya tabe
yayi bago ya rabe
Neman jini ga babe
Ba za'a samu nai ba
Zo ka taba dai ka jiya
Yau muke koko jiya?
Haure ka ciwo ijiya
in yayi sai ayi jinya
ba za'a debewa ba
Ko ka iso, ko ka tsaya
Taunan aya ko ka iya?
Amale cimansa kaya
Jaki, da sa, ko akuya
Ba zasu taunawa ba
Kaya ga Rakumi shike
Takarkari sai taiki
Saimo akanwa taki
Tsaiko akanwa daki
bukka ba ta dauka ba.
Makaryata, mahassada
basu iya komi da guda
na yanzu ba ko da na da
tara su dai duk ka gwada
ba su zamo daidai ba
Babba da jaka ya zaka
Yana bidan kifi tsaka
gulbin da dorina tsaka
Gefen kadanni ya saka
kafansa ba zai kai ba
Yada guda ka dau guda
Duk ka fasa su ba guda
hanya mararraba guda
gaba-gaba akan guda
cikinsu bai ba daya ba
Ga kutu ga Tabarkoko
Ga dole-dole tai hako
ni naga tana ga fako
kai mai bago shiga sako
Wurin ba'a zo mai ba
Kwaddo ina kadangare
Naji kafarsa ta kare
ya bar diyanshi gangare
in yayi nan sai a tare
ni ban gano zai kai ba
Ko kaga mai digirgire
wuya awa gadar zare
Takuna zance hantsare
da zamanin bakin zare
da basu sa riga ba
Ga tsada mai dan tashi
kullum ta dau albashi
ba ta ci bata hana bashi
ran da safiya tai fashi
ba za'a koka mai ba
Ga wani tantalwashi
na biyunsu mai kan bashi
na ukkunsu bashi da nashi
Da dai ana tuna bashi
da basu sa riga ba
Nazundu mai zaka fada
kullum ka gana da rada
roko awa dan makada
a baka bashi a dada
ba zashi fasawa ba
Ga wani wai shi ya iya
yaje ya jawo igiya
ta nannade mai a wuya
yana kira da waiwaya
ba za'a debe mai ba
Shin me ya samu shamuwa
na ga tana ta dimuwa
naga ruwan da kainuwa
ba dun kasan da kaguwa
da bata sauka anan ba
Da kunkuru da bushiyta
halinsu dai noke wuya
ga zamani na waiwaya
da zamanin mazan jiya
ni naga da basu kai ba
Debi yawa, sam ma kadan
yanzu yawa ta zam kadan
a hankali kadan-kadan
Gidan yawa kan yi kadan
Abinga ba banza ba
Nai muku waka ta batu
ku zo ku nemi yan batu
awa su lugegen batu
tara fasihai na batu
ba zasu ganewa ba
Mai wagga waka ta batu
Ali Amiru wan Shatu
Shine abokin Warqatu
Dadai da sirri na batu
Da bashi boyewa ba
Allahu shi yai mu duka
Baki fari yai su duka
Shudi da Korensu duka
Da Ja da Rawaya duka
Shi dai kayi ba wani ba
Zama fa shi dai ya iya
Shi yo mutum shi tafiya
Wadansu ko shi yi su tsaya
Shi yai itace da kaya
Nufinsa ne ba wani ba
Shi yai dawa da karkara
Shi yai dawa da karkara
Shi yai kwai, yai zakara
Yai zabuwa, yai fakara
Shi ad damu ba wani ba
Bautanmu dai hasana'u
Zam haufu, duk dada rija'u
Ku lura ko asma'u
Nisa'u masu gina'u
Sha'aninsu ba karko ba
Asma'u an sanki da dai
Halinki ki ne ko can dadai
Shirinki kullum na kwadai
Maso biyu,bashi da dai
Batun ga ba karyaba
Ywaita rokon Jalla
Ka wakkale ga Allah
Ka zam kula da Salla
A baka ni'ima walla
Anan da can ba waiba
Muyi zikiri da salati
Mu karkare afati
Gobe mu san najjati
Ga shugaban hajati
Muhammadu bawani ba
Aboka zo nan mu bata
ka dubi dan dai ga wata
wada daban da batta
Haske na rana da wata
Ba zasu zam daidai ba
He dubi dai tsettsewa
Ya samu kifi a wuya
shina zaton babu kaya
Inta kafe mai ga wuya
ba zasu debe mai ba
He dubi dai irame
Can tai gida a rame
Can dauri kau ta rame
kyaushe mijin Irame
gallonsu ba zaki ba
Abin ga dai gama na
kare shi tono magana
zai iske kura a hana
ba dun akwai wata magana
da bai fito rannan ba
Ai ga fage ga doki
Noman fako ba taki
ai maganan ta sake
da dan kare da na doki
ba zasu zam daidai ba
Mu namu ga ta da taki
babu biri ba zaki
barde dubu mai doki
da zamanin kai taki
da bamu samu nai ba
Saura garin ya waye
duk kokuwan tai kaye
Damu ga yan tawaye
da masu da da maye
zamansu bai zam dai ba
Karya take zabira
bata zama gurara
Iska daban da sarara
matar maza da bera
kudinsu bai zam dai ba
Na ganshi duk ya kwabe
Yayi tabo ya tabe
yayi bago ya rabe
Neman jini ga babe
Ba za'a samu nai ba
Zo ka taba dai ka jiya
Yau muke koko jiya?
Haure ka ciwo ijiya
in yayi sai ayi jinya
ba za'a debewa ba
Ko ka iso, ko ka tsaya
Taunan aya ko ka iya?
Amale cimansa kaya
Jaki, da sa, ko akuya
Ba zasu taunawa ba
Kaya ga Rakumi shike
Takarkari sai taiki
Saimo akanwa taki
Tsaiko akanwa daki
bukka ba ta dauka ba.
Makaryata, mahassada
basu iya komi da guda
na yanzu ba ko da na da
tara su dai duk ka gwada
ba su zamo daidai ba
Babba da jaka ya zaka
Yana bidan kifi tsaka
gulbin da dorina tsaka
Gefen kadanni ya saka
kafansa ba zai kai ba
Yada guda ka dau guda
Duk ka fasa su ba guda
hanya mararraba guda
gaba-gaba akan guda
cikinsu bai ba daya ba
Ga kutu ga Tabarkoko
Ga dole-dole tai hako
ni naga tana ga fako
kai mai bago shiga sako
Wurin ba'a zo mai ba
Kwaddo ina kadangare
Naji kafarsa ta kare
ya bar diyanshi gangare
in yayi nan sai a tare
ni ban gano zai kai ba
Ko kaga mai digirgire
wuya awa gadar zare
Takuna zance hantsare
da zamanin bakin zare
da basu sa riga ba
Ga tsada mai dan tashi
kullum ta dau albashi
ba ta ci bata hana bashi
ran da safiya tai fashi
ba za'a koka mai ba
Ga wani tantalwashi
na biyunsu mai kan bashi
na ukkunsu bashi da nashi
Da dai ana tuna bashi
da basu sa riga ba
Nazundu mai zaka fada
kullum ka gana da rada
roko awa dan makada
a baka bashi a dada
ba zashi fasawa ba
Ga wani wai shi ya iya
yaje ya jawo igiya
ta nannade mai a wuya
yana kira da waiwaya
ba za'a debe mai ba
Shin me ya samu shamuwa
na ga tana ta dimuwa
naga ruwan da kainuwa
ba dun kasan da kaguwa
da bata sauka anan ba
Da kunkuru da bushiyta
halinsu dai noke wuya
ga zamani na waiwaya
da zamanin mazan jiya
ni naga da basu kai ba
Debi yawa, sam ma kadan
yanzu yawa ta zam kadan
a hankali kadan-kadan
Gidan yawa kan yi kadan
Abinga ba banza ba
Nai muku waka ta batu
ku zo ku nemi yan batu
awa su lugegen batu
tara fasihai na batu
ba zasu ganewa ba
Mai wagga waka ta batu
Ali Amiru wan Shatu
Shine abokin Warqatu
Dadai da sirri na batu
Da bashi boyewa ba
Allahu shi yai mu duka
Baki fari yai su duka
Shudi da Korensu duka
Da Ja da Rawaya duka
Shi dai kayi ba wani ba
Zama fa shi dai ya iya
Shi yo mutum shi tafiya
Wadansu ko shi yi su tsaya
Shi yai itace da kaya
Nufinsa ne ba wani ba
Shi yai dawa da karkara
Shi yai dawa da karkara
Shi yai kwai, yai zakara
Yai zabuwa, yai fakara
Shi ad damu ba wani ba
Bautanmu dai hasana'u
Zam haufu, duk dada rija'u
Ku lura ko asma'u
Nisa'u masu gina'u
Sha'aninsu ba karko ba
Asma'u an sanki da dai
Halinki ki ne ko can dadai
Shirinki kullum na kwadai
Maso biyu,bashi da dai
Batun ga ba karyaba
Ywaita rokon Jalla
Ka wakkale ga Allah
Ka zam kula da Salla
A baka ni'ima walla
Anan da can ba waiba
Muyi zikiri da salati
Mu karkare afati
Gobe mu san najjati
Ga shugaban hajati
Muhammadu bawani ba
Monday, April 16, 2007
Wasiyya Sipikiyya; Daga Mudi Spikin
Ta'ala ina rokonka ranar da zan cika
Kasa in cika Allah cikin daki na
Gaban duk iyali na da 'ya'ya da 'yan'uwa
Allah ina rokon ka sai a gidana
Idan na cika yan'uwa na gaya muku
Da kun ji cikawata ku taru gidana
Idan har da rana abin yazo ko cikin dare
Batun jinkiri kar dai ya faru wurina
Idan anyi sallah an gama kar a dakata
A dauka kawai hanyar zuwa kabarina
Idan anka je da zuwa a sani ciki kawai
Cikin hankali domin tuno lamarina
Kasar kabarin kuma kar a ware daban-daban
A turo gaba daya duk ta watsu a kaina
Idan aka kare gini da an tashi an gama
Ku koma wajen harkarku ya jama'ata
Batun sadakar Uku, ko Bakwai, ko ta Arba'in
Kaza shekara wallahi babu ruwana
Irin masu kukan nan da ihu da razana
Don Allah na roke ku kar kuyi kaina
Ina tausayin ku kwarai zuwa gun jana'iza
Kaza wahalar tafiya hakan kabarina
Kaza wahalar wanka da dauko ni don zuwa
Cikin makara tafiya zuwa karshe na
Hakika a rannan da da ikon da zan iya
Ya sa tausayin a wajen dukan jama'ana
Anan zan tsaya domin wasiyarmu ta tsaya
Mudi Spikin ne uba ga Amina
Kasa in cika Allah cikin daki na
Gaban duk iyali na da 'ya'ya da 'yan'uwa
Allah ina rokon ka sai a gidana
Idan na cika yan'uwa na gaya muku
Da kun ji cikawata ku taru gidana
Idan har da rana abin yazo ko cikin dare
Batun jinkiri kar dai ya faru wurina
Idan anyi sallah an gama kar a dakata
A dauka kawai hanyar zuwa kabarina
Idan anka je da zuwa a sani ciki kawai
Cikin hankali domin tuno lamarina
Kasar kabarin kuma kar a ware daban-daban
A turo gaba daya duk ta watsu a kaina
Idan aka kare gini da an tashi an gama
Ku koma wajen harkarku ya jama'ata
Batun sadakar Uku, ko Bakwai, ko ta Arba'in
Kaza shekara wallahi babu ruwana
Irin masu kukan nan da ihu da razana
Don Allah na roke ku kar kuyi kaina
Ina tausayin ku kwarai zuwa gun jana'iza
Kaza wahalar tafiya hakan kabarina
Kaza wahalar wanka da dauko ni don zuwa
Cikin makara tafiya zuwa karshe na
Hakika a rannan da da ikon da zan iya
Ya sa tausayin a wajen dukan jama'ana
Anan zan tsaya domin wasiyarmu ta tsaya
Mudi Spikin ne uba ga Amina
Wakar Shehu malam Nasara Kabara; Daga Mudi Spikin
Bagadada suna ajabi nasa
Don sun ga irin himma tasa
Suka ce kai wannan ya isa
Har yanzu suna Allah yasa
Su ga Alhaji malam Nasiru
Qadiriyya yai zurfi ciki
Darajarta kwarai yai arziki
Jama'a da yawa duk sun saki
Hairi a gare shi daki-daki
Kuma ga takawa gun Nasiru
Shi gwarz ne mai kokari
Mai kamala mai kyawon shiri
Ga mutunci gashi da hankuri
Ko ina an san shi gari-gari
Kwarjini sai Malam Nasiru
Don sun ga irin himma tasa
Suka ce kai wannan ya isa
Har yanzu suna Allah yasa
Su ga Alhaji malam Nasiru
Qadiriyya yai zurfi ciki
Darajarta kwarai yai arziki
Jama'a da yawa duk sun saki
Hairi a gare shi daki-daki
Kuma ga takawa gun Nasiru
Shi gwarz ne mai kokari
Mai kamala mai kyawon shiri
Ga mutunci gashi da hankuri
Ko ina an san shi gari-gari
Kwarjini sai Malam Nasiru
RASHA Abokan Fita Kunya; Daga Mudi Spikin
Wannan waka ta jawowa Malam Mudi dauri a gidan yari. Domin a fahimtar Turawan Mulki wannan wani sako ne da kan iya tunzura talakawa suyi bore, kuma kan iya jefa kasa cikin juyin-juya hali irin na Kwaminisanci. Mudi Spikin ya rubuta wannan waka a 1948. Ga dai wakar
Ya yan'uwa ku zo don ku ji ni
Zan wo bayani akan Rusiya
Gama Ingilishi fa sun tashi haikan
Suka suke yi akan Rusiya
Da babbata hanyarsu don kar a so su
Don kar su zo nan mutan Rusiya
Shine nake so in wo dan bayani
Domin ku gane kasar Rusiya
Kasa ce ta kirki da himma garesu
Da kaunar mutane kasar Rusiya
Wakilinsu Malik sunansa ke nan
Sunan musulmi da ba fariya
Ni dai ace yau zan samu iko
Ni sai in koma kasar Rusiya
Kamar na iya tsunts inje can in Zauna
Idan na tuno su mutan Rusiya
Girmama kowa dabi'arsu ce
Ibada kamar Hajji sai Rusiya
Da son musulunci da bayar da zakka
Yawan azumi sai kasar Rusiya
Kwalta na banza damu bamu samu
Da kafur akeyi acan Rusiya
Da banki na rance idan har kana so
Ko fam Dubu Goma baki daya
Musaki acan sai ya zauna da Gwamna
Wajen shawara babu kin gaskiya
Sa'annan da sauran abubba na kirki
Suna da yawa a kasar Rusiya
Gidaje dubu Goma ne don Musakai
A yau su kasar wane ba ko daya
Akwai Talakawa akwai Tajirai
Kamar dai kasarmu ta Nijeriya
Anan gaba na tabbata babu shakka
Nijeriya zamu zam Rusiya
Mu zam mun fice daga gun Ingilishi
Mutanen daba sa rikon gaskiya
Sun barmu babu kudi babu gona
Babu abin yi cikin gaskiya
Sun shekaru yanzu Hamsin kasarmu
Ba taimako babu son gaskiya
Ta'ala Rahimu kadai taimakemu
Ka kawo mutan Rasha Nijeriya
Idan aka ce wa ya tsara ta waka
Ya bayyana halin mutan Rusiya
Ba zan boye suna ba ko za'a nema
Mudi spikin maso Rusiya
Gama bani tsoro na dauri hakika
Akan Rasha ma sai in bar duniya
Ya yan'uwa ku zo don ku ji ni
Zan wo bayani akan Rusiya
Gama Ingilishi fa sun tashi haikan
Suka suke yi akan Rusiya
Da babbata hanyarsu don kar a so su
Don kar su zo nan mutan Rusiya
Shine nake so in wo dan bayani
Domin ku gane kasar Rusiya
Kasa ce ta kirki da himma garesu
Da kaunar mutane kasar Rusiya
Wakilinsu Malik sunansa ke nan
Sunan musulmi da ba fariya
Ni dai ace yau zan samu iko
Ni sai in koma kasar Rusiya
Kamar na iya tsunts inje can in Zauna
Idan na tuno su mutan Rusiya
Girmama kowa dabi'arsu ce
Ibada kamar Hajji sai Rusiya
Da son musulunci da bayar da zakka
Yawan azumi sai kasar Rusiya
Kwalta na banza damu bamu samu
Da kafur akeyi acan Rusiya
Da banki na rance idan har kana so
Ko fam Dubu Goma baki daya
Musaki acan sai ya zauna da Gwamna
Wajen shawara babu kin gaskiya
Sa'annan da sauran abubba na kirki
Suna da yawa a kasar Rusiya
Gidaje dubu Goma ne don Musakai
A yau su kasar wane ba ko daya
Akwai Talakawa akwai Tajirai
Kamar dai kasarmu ta Nijeriya
Anan gaba na tabbata babu shakka
Nijeriya zamu zam Rusiya
Mu zam mun fice daga gun Ingilishi
Mutanen daba sa rikon gaskiya
Sun barmu babu kudi babu gona
Babu abin yi cikin gaskiya
Sun shekaru yanzu Hamsin kasarmu
Ba taimako babu son gaskiya
Ta'ala Rahimu kadai taimakemu
Ka kawo mutan Rasha Nijeriya
Idan aka ce wa ya tsara ta waka
Ya bayyana halin mutan Rusiya
Ba zan boye suna ba ko za'a nema
Mudi spikin maso Rusiya
Gama bani tsoro na dauri hakika
Akan Rasha ma sai in bar duniya
Karara; daga Malam Mudi Spikin
An haifi Alhaji Mudi Spikin a ran 1 ga watan Oktoba 1930, a unguwar Darma da ke birnin Kano. Yayi karatun qur'ani a hannun Malam Umaru Badamagare. Bai taba zuwa makarantar boko ba, amma duk da haka, ya zauna jarrabawa GCE Ordinary level, ta hanyar yin rijista da wata kwaleji a Ingila, acikin 1960. Ya sami illimin zamani ne a hannun abokansa na gwagwarmayar siyasa irinsu; Malam Sa'adu Zungur, Malam Aminu Kano, da kuma Alhaji Yusuf Maitama Sule. Yana cikin mutanen da suka kafa jam'iyyar kwato yancin talaka wato NEPU a 1950. Ya fara rubuta wakokinsa tun a 1948, ya fara da wakarsa ta "Rasha Abokan Tafiya", da kuma wani raddi da yayiwa malaminsa, wato malam Sa'adu Zungur maitaken "Arewa Jamhuriya Kawai".
A ya jama'a ina tashin
Ku dan ku rage yawan bacci
Ayau na zo gareku da sha
Wara don kara inganci
Mu wo himma mu tashi tsaye
Mu gyara kasa ta san yanci
Mu kawo shawara mai kyau
Mu tashi mu yaki jahilci
Rashin illimi ya sanya yau
Kasar nan ke yawan baci
Fa sai mun tsaya gyara
Na sosai babu jahilci
Sannan zamu san matsayi
Mu tsere wa wulakanci
Idan ba tattali a kasa
Hakika dole ta baci
Idan an zubda hakkin yan
Adam domin wulakanci
Idan masana kwarai an zub
Da su domin rashin yanci
Idan sharia ta zam ciniki
Ana nunnuna bambanci
Idan kuma masu aiki sun
Zamo duk babu inganci
Idan aiki ya zamto ba
Ayi, sai an ciwo hanci
Idan hairi a baki ake
Fada sharri cikin zuci
Idan da akwai yawan hassada
Da bata mutum da iskanci
Idan da akwai yawanta saki
Na aure don wulakanci
Idan ba tanadi wai duk
Wata sai anyi angwanci
Idan aure ya zam a kasa
Ana yi ne da jahilci
Idan kayan biki aka mai
Da su tamkar na dillanci
Idan ga jahilai a kasa
Na kin canji da shashanci
Idan da zama na banza, ba
Sana'a ai ta kakaci
A sa fatala gaban goshi
Da hula wai tsageranci
Ana ta musu ana karta
Ana zance na wawanci
Idan kuma ga yawan zargi
Na banza ga rashin yanci
Idan wani dan'uwa wai yayi
Samu ayi munafunci
Idan sharri ya zo a iza
Nufi dai ayi wulakanci
Idan da akwai yawan camfi
Da bori masu shashanci
Idan da akwai yawan tsegun
Guman banza na jahilci
Idan a kasa ya zam an go
Yi bayan masu lalaci
Idan mai gaskiya ya zamo
A kullum zai ga kaskanci
Idan gata ya sanya wadan
Su yin shirme da shashanci
Idan aka maida wadansu kamar
Ace bayi rashin yanci
Idan yan kasuwa suka zam
Sana'a aita hainici
Idan ga karuwai a kasa
A kullum ai ta fasicci
Idan da giya an ta
Ru kullm nuna iskanci
Idan ba tausayi a kasa
Mutane na ta makirci
Idan kuma har amana tai
Kadan sai nuna ha'inci
Idan har maluma suka bar
Sani i zuwa fagen baci
Idan bidia ta zam an gir
Gina kuma babu sassauci
Idan yaya suna sabon
Mahaifa har da kaskanci
Idan a kasa akwai wannan
Hakika dole ta baci
Fa sai in anyi aiki za
Hiri ba nuna lalaci
Sa'annan zamu san haske
Mu tserewa wulakanci
Abinda na farfadan nanYan
'Uwa da akwai muhimmanci
Fa duk gyaran wadannan na
Garemu cikin batun yanci
Mu daina abinda bashi da kyau
Mu daina biyewa jahilci.
A ya jama'a ina tashin
Ku dan ku rage yawan bacci
Ayau na zo gareku da sha
Wara don kara inganci
Mu wo himma mu tashi tsaye
Mu gyara kasa ta san yanci
Mu kawo shawara mai kyau
Mu tashi mu yaki jahilci
Rashin illimi ya sanya yau
Kasar nan ke yawan baci
Fa sai mun tsaya gyara
Na sosai babu jahilci
Sannan zamu san matsayi
Mu tsere wa wulakanci
Idan ba tattali a kasa
Hakika dole ta baci
Idan an zubda hakkin yan
Adam domin wulakanci
Idan masana kwarai an zub
Da su domin rashin yanci
Idan sharia ta zam ciniki
Ana nunnuna bambanci
Idan kuma masu aiki sun
Zamo duk babu inganci
Idan aiki ya zamto ba
Ayi, sai an ciwo hanci
Idan hairi a baki ake
Fada sharri cikin zuci
Idan da akwai yawan hassada
Da bata mutum da iskanci
Idan da akwai yawanta saki
Na aure don wulakanci
Idan ba tanadi wai duk
Wata sai anyi angwanci
Idan aure ya zam a kasa
Ana yi ne da jahilci
Idan kayan biki aka mai
Da su tamkar na dillanci
Idan ga jahilai a kasa
Na kin canji da shashanci
Idan da zama na banza, ba
Sana'a ai ta kakaci
A sa fatala gaban goshi
Da hula wai tsageranci
Ana ta musu ana karta
Ana zance na wawanci
Idan kuma ga yawan zargi
Na banza ga rashin yanci
Idan wani dan'uwa wai yayi
Samu ayi munafunci
Idan sharri ya zo a iza
Nufi dai ayi wulakanci
Idan da akwai yawan camfi
Da bori masu shashanci
Idan da akwai yawan tsegun
Guman banza na jahilci
Idan a kasa ya zam an go
Yi bayan masu lalaci
Idan mai gaskiya ya zamo
A kullum zai ga kaskanci
Idan gata ya sanya wadan
Su yin shirme da shashanci
Idan aka maida wadansu kamar
Ace bayi rashin yanci
Idan yan kasuwa suka zam
Sana'a aita hainici
Idan ga karuwai a kasa
A kullum ai ta fasicci
Idan da giya an ta
Ru kullm nuna iskanci
Idan ba tausayi a kasa
Mutane na ta makirci
Idan kuma har amana tai
Kadan sai nuna ha'inci
Idan har maluma suka bar
Sani i zuwa fagen baci
Idan bidia ta zam an gir
Gina kuma babu sassauci
Idan yaya suna sabon
Mahaifa har da kaskanci
Idan a kasa akwai wannan
Hakika dole ta baci
Fa sai in anyi aiki za
Hiri ba nuna lalaci
Sa'annan zamu san haske
Mu tserewa wulakanci
Abinda na farfadan nanYan
'Uwa da akwai muhimmanci
Fa duk gyaran wadannan na
Garemu cikin batun yanci
Mu daina abinda bashi da kyau
Mu daina biyewa jahilci.
Tuesday, April 10, 2007
Wakar Kidayar Mutanen Nijeriya 1973; Daga Hajiya Yar Shehu
An haifi Hajiya Yar Shehu a shekara 1937, a garin Dambatta. Ta halarci makarantar Yanmata dake lardin Sakkwato, bayan ta kammala karatun addini a gida. Ta fara aiki a ma'aikatar lafiya ta Kano a 1953, bayan ta koyar a makarantun Firamare. Daga bisani ta koma kamfanin jiragen sama na Kano, a matsayin mai bada hanyar Tarho, inda ta zama jami'ar kula da ma'aikata na ma'aikatar. Haka kuma member ce a shahararriyar kungiyar mawakan nan, wato Hikima Kulob. Ta dai wallafi wakoki da dama, domin fadakarwa, zaburarwa, illimantarwa, wa'azantarwa, da sauransu, wakokinta sun hada da "Waka da Bayani", Wakar Kidaya, Wakar Zamani dss. wadanda insha Allahu zamu kawo muku su, da dai-dai. Ta rubuta wannan waka, domin fadakar da mutane akan kidayar jama'a wato Census da akayi a 1973. Ga dai Wakar;
BismilLah na fara da sunan Rabbana
Allah Ta'ala Jallah Sarkin gaskiya
Kai ne Sami'un Basiru, Mai ji, Mai gani
Ka tsare mu sharrin, masu sharrin duniya
Domin Muhammadu shugaban duka duniya
Har lahira ma, in ka bashi gaba daya
Don Annabawa har Sahabbai Mursalai
Har dukka dangogin Rasulu abin biya
Kayi taimako agareni kai min kangiya
Kai ne katanga wadda bata zagaya
To zanyi tsari dan Kidaya ne yankuna
Ta Arewa harma duk kasarmu gaba daya
Allah Hakimu hikimarka da ta isa
Kasa mu gane don mu bayyana gaskiya
Don kada mu fada ayyukan shibcin gizo
Da ya kasa dauka, sai ya karo kungiya
Ga gargadina gun sarakai malamai
Lalle ku dage don ku kange areriya
Komai idanu bakuna har kunnuwa
Komai ya baci wuyanku ne zai rataya
Ko Shehu Fodiye ku yaba tuta tasa
Har ma amanar dogare gaba daya
Domin hakan nan sai ku tashi ku taimaka
Akan kidayar na jihannunmu gaba daya
Don kadda a kwaso kyankyaso da su kwarkwata
a zazzage mana nan Arewa mu sha wuya
Allah jikansu na baya manya sun wuce
Giwa saka kawo ban Arewa gaba daya
Dan kadda mu ji ta kururuwa rashe idon kuma
Har ma da makirci na mai kin gaskiya
Kuma kadda jahilci ya sa sarkacen tasa
Ya ja kafa kuma har wuyanmu gaba daya
In anka zo kirga ya tabbata mun zaka
Mun bayyana musu dangunanmu gaba daya
Maza da mata har da yara kankana
Har jinjirai ma wanda sun kwana daya
Kuma har da tsofaffi da basu fita waje
Don Allah duk a fade su kar a rage daya
Domin barin wani, baya ba wani taimako
An fidda dashi acikin mutan Nijeriya
Shi bai ga tsuntsu bai ga tarko ya bace
Sai yai nadama nan cikin Nijeriya
Allah tsare mu da yin hakan, ya yan'uwa
Kuma maganin wannan a bayyana gaskiya
Kuyi tir da masu batun na banza kun jiyya
Makiya jiharmu, munafukanta Arewaci Nijeriya
Har ma suna cewa haraj za'a sa
Domin su wargazar da shirin ta areriya
Kuma don a danne tattalinmu na arziki
Har ma a danne komi nan arewa mu sha wuya
Ba'a kidaya kan haraji kun sani
Yara da mata ba'a sa musu kun jiya
Haka ma a zozzowa da tsofaffi duka
Suma haraji ba'a sa musu kun jiya
Wannan kidaya dai nufinta daban yake
Nan dai asan jimlar mutan Nijeriya
Kuma don a san adadin mutanen jihhunan
Jihar da tafi yawa cikin Nijeriya
In an rabo ita zata samu mafi yawa
Ninkin ba ninkin za'a bata kunjiya
Kan duk ku da ayyukan gona duka
Kuma asibitoci makarantu kun jiya
To zasu samu rabo mafi girma duka
To kadda mu cuci jiharmu nan ta arewiya
Duk wanda ycce ma haraji za'a sa
Ce mai haraji arziki ne ka jiya
Mara lafiya da mahaukata basa biya
ashe haraji lafiya ne kun jiya
Sauki gareshi gun manomi kun jiya
Zakkar abinda ya aikata shi ke biya
Yan kasuwa ma sau guda ne shekara
Ma'aikata ne ba iyaka kun jiya
Dukkan wata kullum akan diba ake
Sisi ake diba a kowace fam Daya
Kai malami har malama kuyi anniya
Ku bada sunan yan uwanku gaba daya
Yaya da jikoki da dangi ba ragi
Har wanda basu gida suna wata nahiya
Dada wanda yaki shiga cikin kirga kusan
Shi zaya sha kunya cikin Nijeriya
Sannan ya zam mugu sharari jahili
Mai taimakawa don a cuci arewiya
To malaman Sansan inai muku gargadi
Dan Allah don manzo Rasulu abin biya
Kuma banda kosawa ku dau hakuri kwarai
A wajen kidaya kadda ku dinga tsamiya
Ku bi sannu-sannu a hankali ba firgita
Kuma ba tsanantawa a kowace tambaya
In ko akayi muku tambaya ta rashin sani
Ku bada amsa kadda ku kosa kun jiya
Kuyi ayyukanku da gaskiya bisa ka'ida
Acikin birane, kauyuka har tsangaya
Ahaiyye iyyenanaiyaye yurai yurai
Malam abin ga da niyyi kada kai tambaya
Na barwa Jallah wa'azu sarki mai sani
Ubangiji ya sani kafin ya darsu ga zuciya
To shugaban kirga muna ta sa ido
Muga ayyukan komi yana kan gaskiya
Don kadda azo da ka taho ayi ta gunaguni
Harma takai mu fagen a dinga hatsaniya
kuma kar ta kai ga fagen abin da-na-sani
Ita ko alama ce ta bacin zuciya
Da-na-sani keya a baya take tutur
In an fade ta ku tabbata an sha wuya
Gabas da Yamma, Tsakiya da Arewiya
Muga kan shirin komi ya zam mana bai daya
Don kada a sayar da dubu a kasa sayan daya
Har ma akai ga fagen ace ya rasa kiya
Alhamdu LilLahi ina yin godiya
Agurin Ta'ala Jallah Sarki shi daya
Tamat bi HamdilLahi waka ta tsaya
Waka a gargadinku nan mu gaba daya
a wajen bayani kada ku damu da tambaya
Yar shehu tai wanga tsari kun jiya
In an ka ce adires ku duba ba wuya
Don ni a kofar mata sai kui tambaya
Nagode Allah har Rasulu abin biya
Alai Sahabbai Tabi'ina da Auliya
Baitinta Sittin ba Biyar ba kunjiya
Na rufe da sunan wanda baya fariya
BismilLah na fara da sunan Rabbana
Allah Ta'ala Jallah Sarkin gaskiya
Kai ne Sami'un Basiru, Mai ji, Mai gani
Ka tsare mu sharrin, masu sharrin duniya
Domin Muhammadu shugaban duka duniya
Har lahira ma, in ka bashi gaba daya
Don Annabawa har Sahabbai Mursalai
Har dukka dangogin Rasulu abin biya
Kayi taimako agareni kai min kangiya
Kai ne katanga wadda bata zagaya
To zanyi tsari dan Kidaya ne yankuna
Ta Arewa harma duk kasarmu gaba daya
Allah Hakimu hikimarka da ta isa
Kasa mu gane don mu bayyana gaskiya
Don kada mu fada ayyukan shibcin gizo
Da ya kasa dauka, sai ya karo kungiya
Ga gargadina gun sarakai malamai
Lalle ku dage don ku kange areriya
Komai idanu bakuna har kunnuwa
Komai ya baci wuyanku ne zai rataya
Ko Shehu Fodiye ku yaba tuta tasa
Har ma amanar dogare gaba daya
Domin hakan nan sai ku tashi ku taimaka
Akan kidayar na jihannunmu gaba daya
Don kadda a kwaso kyankyaso da su kwarkwata
a zazzage mana nan Arewa mu sha wuya
Allah jikansu na baya manya sun wuce
Giwa saka kawo ban Arewa gaba daya
Dan kadda mu ji ta kururuwa rashe idon kuma
Har ma da makirci na mai kin gaskiya
Kuma kadda jahilci ya sa sarkacen tasa
Ya ja kafa kuma har wuyanmu gaba daya
In anka zo kirga ya tabbata mun zaka
Mun bayyana musu dangunanmu gaba daya
Maza da mata har da yara kankana
Har jinjirai ma wanda sun kwana daya
Kuma har da tsofaffi da basu fita waje
Don Allah duk a fade su kar a rage daya
Domin barin wani, baya ba wani taimako
An fidda dashi acikin mutan Nijeriya
Shi bai ga tsuntsu bai ga tarko ya bace
Sai yai nadama nan cikin Nijeriya
Allah tsare mu da yin hakan, ya yan'uwa
Kuma maganin wannan a bayyana gaskiya
Kuyi tir da masu batun na banza kun jiyya
Makiya jiharmu, munafukanta Arewaci Nijeriya
Har ma suna cewa haraj za'a sa
Domin su wargazar da shirin ta areriya
Kuma don a danne tattalinmu na arziki
Har ma a danne komi nan arewa mu sha wuya
Ba'a kidaya kan haraji kun sani
Yara da mata ba'a sa musu kun jiya
Haka ma a zozzowa da tsofaffi duka
Suma haraji ba'a sa musu kun jiya
Wannan kidaya dai nufinta daban yake
Nan dai asan jimlar mutan Nijeriya
Kuma don a san adadin mutanen jihhunan
Jihar da tafi yawa cikin Nijeriya
In an rabo ita zata samu mafi yawa
Ninkin ba ninkin za'a bata kunjiya
Kan duk ku da ayyukan gona duka
Kuma asibitoci makarantu kun jiya
To zasu samu rabo mafi girma duka
To kadda mu cuci jiharmu nan ta arewiya
Duk wanda ycce ma haraji za'a sa
Ce mai haraji arziki ne ka jiya
Mara lafiya da mahaukata basa biya
ashe haraji lafiya ne kun jiya
Sauki gareshi gun manomi kun jiya
Zakkar abinda ya aikata shi ke biya
Yan kasuwa ma sau guda ne shekara
Ma'aikata ne ba iyaka kun jiya
Dukkan wata kullum akan diba ake
Sisi ake diba a kowace fam Daya
Kai malami har malama kuyi anniya
Ku bada sunan yan uwanku gaba daya
Yaya da jikoki da dangi ba ragi
Har wanda basu gida suna wata nahiya
Dada wanda yaki shiga cikin kirga kusan
Shi zaya sha kunya cikin Nijeriya
Sannan ya zam mugu sharari jahili
Mai taimakawa don a cuci arewiya
To malaman Sansan inai muku gargadi
Dan Allah don manzo Rasulu abin biya
Kuma banda kosawa ku dau hakuri kwarai
A wajen kidaya kadda ku dinga tsamiya
Ku bi sannu-sannu a hankali ba firgita
Kuma ba tsanantawa a kowace tambaya
In ko akayi muku tambaya ta rashin sani
Ku bada amsa kadda ku kosa kun jiya
Kuyi ayyukanku da gaskiya bisa ka'ida
Acikin birane, kauyuka har tsangaya
Ahaiyye iyyenanaiyaye yurai yurai
Malam abin ga da niyyi kada kai tambaya
Na barwa Jallah wa'azu sarki mai sani
Ubangiji ya sani kafin ya darsu ga zuciya
To shugaban kirga muna ta sa ido
Muga ayyukan komi yana kan gaskiya
Don kadda azo da ka taho ayi ta gunaguni
Harma takai mu fagen a dinga hatsaniya
kuma kar ta kai ga fagen abin da-na-sani
Ita ko alama ce ta bacin zuciya
Da-na-sani keya a baya take tutur
In an fade ta ku tabbata an sha wuya
Gabas da Yamma, Tsakiya da Arewiya
Muga kan shirin komi ya zam mana bai daya
Don kada a sayar da dubu a kasa sayan daya
Har ma akai ga fagen ace ya rasa kiya
Alhamdu LilLahi ina yin godiya
Agurin Ta'ala Jallah Sarki shi daya
Tamat bi HamdilLahi waka ta tsaya
Waka a gargadinku nan mu gaba daya
a wajen bayani kada ku damu da tambaya
Yar shehu tai wanga tsari kun jiya
In an ka ce adires ku duba ba wuya
Don ni a kofar mata sai kui tambaya
Nagode Allah har Rasulu abin biya
Alai Sahabbai Tabi'ina da Auliya
Baitinta Sittin ba Biyar ba kunjiya
Na rufe da sunan wanda baya fariya
Wakar Zuwan An Nasara Kasar Hausa; Daga Sarkin Musulmi Attahiru
Shine dai Sarkin Musulmi na karshe, kafi mulkin Turawa. Ya rasu a Burmi a ran 27 ga watan July 1903, bayan sun kafsa da Turawan mulkin mallaka. Ya ki amincewa da Turawan da kuma tsare-tsaren da suka zo masa da su, a saboda haka nema ya rubuta wannan waka, domin ya fadakar da mutanensa illar zama karkashin mulkin Nasara. Hakan ya jawo bore a kasar Hausa, wanda ya sanya, turawan suka yi fito-na-fito dashi. Ganin hakanne ya sanya ya bar garin Sakkwato, inda yayi niyyar yin Hijira zuwa kasa maitsarki. Ya rasu tare da mutane da dama, kuma an kama jama'u da dama, cikinsu kuwa hadda Sarkin Kano Alu. Ga dai wakar
Gudun mutuwa da son rai aggaremu
Da kau kin kaddara abi Annasara
Ina muka yi da dama da hauni suna
Ku tashi mu sa gabanmu mu tsira tsara
Idan ka ce akwai wahala ga tashi
Lahan duka na ga masu biyan Nasara
Idan iko ka kai kak ko ki tashi
Ina iko shi kai ikon Nasara
Idan sun baka kyauta, kar ka karba
Dafi na sun ka baka guba Nasara
Suna foro garemu mu bar zalama
Mazalunta da kansu diyan Nasara
Bakar fitina garesu da kau makida
Ta bata dinin musulmi Annasara
Halin da mu kai ga yau aka bayyanawa
Dalilin ke ga an ka sako Nasara
Ku bar jin masu cewa ba'a ashi
Ina halin zama ga Annnasara
Mu mai da gabanmu Makka mu zo Madina
Madina da Makka dai ab ba Nasara
Batu na Shehu yai yi shi bashi tashi
Sa'a ta ya fade ta ta Annasara
Muna da nufa idan mun samu iko
Mu ja daga, mu kore Annasara
Idan ko sun kashe mu mu san shahada
Muje aljanna sai mu ishe makara.
Sai dai an samu sabani tsakanin masana, a gameda waye ya rubuta wannan waka. Dandatti Abdukadir ya bayyana hujjar cewa, Sarkin Musulmi Attahiru n ya rubuta ta. Amma A B Yahaya shi yana ganin wani malami ne maisuna Malam Labbo dan Mariya Kwasare ya rubutata, inda yace ya samo wannan hujja ce daga Waziri Junaidu.
Gudun mutuwa da son rai aggaremu
Da kau kin kaddara abi Annasara
Ina muka yi da dama da hauni suna
Ku tashi mu sa gabanmu mu tsira tsara
Idan ka ce akwai wahala ga tashi
Lahan duka na ga masu biyan Nasara
Idan iko ka kai kak ko ki tashi
Ina iko shi kai ikon Nasara
Idan sun baka kyauta, kar ka karba
Dafi na sun ka baka guba Nasara
Suna foro garemu mu bar zalama
Mazalunta da kansu diyan Nasara
Bakar fitina garesu da kau makida
Ta bata dinin musulmi Annasara
Halin da mu kai ga yau aka bayyanawa
Dalilin ke ga an ka sako Nasara
Ku bar jin masu cewa ba'a ashi
Ina halin zama ga Annnasara
Mu mai da gabanmu Makka mu zo Madina
Madina da Makka dai ab ba Nasara
Batu na Shehu yai yi shi bashi tashi
Sa'a ta ya fade ta ta Annasara
Muna da nufa idan mun samu iko
Mu ja daga, mu kore Annasara
Idan ko sun kashe mu mu san shahada
Muje aljanna sai mu ishe makara.
Sai dai an samu sabani tsakanin masana, a gameda waye ya rubuta wannan waka. Dandatti Abdukadir ya bayyana hujjar cewa, Sarkin Musulmi Attahiru n ya rubuta ta. Amma A B Yahaya shi yana ganin wani malami ne maisuna Malam Labbo dan Mariya Kwasare ya rubutata, inda yace ya samo wannan hujja ce daga Waziri Junaidu.
Saturday, April 7, 2007
Wakar Buhari; Daga Wazirin Sakkwato Buhari 1903
Wannan wakar an rubutata ne a lokacin da Daular Usmaniya ta Sakkwato ta shiga cikin wani halin kaka-ni-kayi. A lokacin da Turawan mulki suka tasarwa Daular haikan! Daga kudancin Daular, ga kuma Rabih daga bangaren Gabas, sa'annan ga kuma yake yake acikin daular, tsakanin Tukurawa da Yusufawa a Kano, da kuma wasu sassa na daular. Marubucin dai shine shahararran Wazirin nan na Sakkwato, wato Waziri Buhari dan Gidado, wanda jika ne ga Sarkin Musulmi Muhammadu Bello. Ya nuna takaicinsa game da yadda abubuwa suka tarwatsewa Daular ta fulani, da kuma yadda ya gaza wajen sulhuntawa tsakanin Sarkin Kano Tukur da Yan'uwansa, wanda hakan yayi sanadiyyar Yakin Basasar Kano. Hakan nema ya jawo ya rasa idonsa. Ya dai rayu, har zamanin da turawa suka ci Sakkwato, ya rasu a farkon karni na 20.
Ga dai wakar tasa;
Jama'a da ku ni ke kun ji aqrani
Tsoho da sabubba, dud da yan sabyani
Ku zan fadama na nesa hal jirani
Na tsorata, tsoro mai yawa ikhwani
Ga abubuwanga da niggani ashjani
In kun bideni ku tambaya mi ag garan
Halin da ajjiya yau dabam ya firgitan
Shagala zaman ashraru ya shiga sai kadan
Kowa da kowa yau ya rage sai kadan
Wannan abin ya tsoratani
Ga abinda nijji da nig gani bisa kowane
Abu na cikinmu ku dubi iko ya dune
Ban san shi da wuri waliyya tab bayyane
Tsoronga Maryamu taggani har tat tuni
ajban li dhalika minka aw ajbani
Kaitonmu ya jama'a ku tashi mu fifika
Ga abinda sun kayi ko kadanne mu taimaka
Bisa gwargwadanmu ku dubi sa'a ta cika
umara'una, ulama'una sun sam tuqa
Sulaha'una, shuhada'una naji bayani
Amma in da zato raina nai tuni
Shibka abinda ka turbuda shi kan gani
Bari firgita don juge-jugen zamani
Baka gadi tsoro gunmu hakkan ka sani
Ko mumini mai quwwatu lil imani
Tunda randa kas san wanda yaika mai sama
Samo rashi, khairan da Sharran ya gama
Bamai ije maka dai cikinsu, tsaya ruma
Komi taho maka hankuri zaka yi zama
Ka wakkalawa ubangiji Rahmani
Kai dan'uwa na so ka lura ka rarrabe
Ga abinda yaffi gareka don ka fice kure
Rike gaskiya ka santa me kake lalube
Inda kasan tuba kakan rike gwadabe
Daba kaji tsoro ba don hidhyani
Kullum ina jin wa'azi inda shuyukina
Nazo karatu naji gun ulama'una
Subhana, kin ji yai yawa don son ghina
Madalla Maryamu kin tuna min na tuna
Can da wuri na zauna cin nasyani
Na kasa farga yau da gobe suna zuwa
Ga mutum shi kasa abinda yayi cikin fa wa
Karfi shi kau da gani, shi kau sha mantuwa
Na kasa tuba ga zunubbai sun yawa
Kuma ga shuyukhi ga halin sibyani
Na roki Allah Jalla shi ka isam mini
Ga abinda yas same ni shi ka biya mini
Ga abinda nis so zahiri in badini
Na tuba ya Allahu gafarta mini
Don Shehu nurin zamanin Usmanu
Tun nan da barzakhu lahira a shi taimaka
Aikin da niyyi na gaskiya shi biya garan
Shi hana ni muggun yalla ko da nufa kadan
Astagfurullaha l' azima shi agazan
Don shehu Abdulqadir Jilani
Domin Rufa'i ubangiji ka raba mana
Rokon da nai maka don badai ka isan mana
Haka na Dasuki gare su nan muka dangana
Da zaman kushewa har kiyama Rabbana
Amsar Takardu agazan Mannanu
Ga dai wakar tasa;
Jama'a da ku ni ke kun ji aqrani
Tsoho da sabubba, dud da yan sabyani
Ku zan fadama na nesa hal jirani
Na tsorata, tsoro mai yawa ikhwani
Ga abubuwanga da niggani ashjani
In kun bideni ku tambaya mi ag garan
Halin da ajjiya yau dabam ya firgitan
Shagala zaman ashraru ya shiga sai kadan
Kowa da kowa yau ya rage sai kadan
Wannan abin ya tsoratani
Ga abinda nijji da nig gani bisa kowane
Abu na cikinmu ku dubi iko ya dune
Ban san shi da wuri waliyya tab bayyane
Tsoronga Maryamu taggani har tat tuni
ajban li dhalika minka aw ajbani
Kaitonmu ya jama'a ku tashi mu fifika
Ga abinda sun kayi ko kadanne mu taimaka
Bisa gwargwadanmu ku dubi sa'a ta cika
umara'una, ulama'una sun sam tuqa
Sulaha'una, shuhada'una naji bayani
Amma in da zato raina nai tuni
Shibka abinda ka turbuda shi kan gani
Bari firgita don juge-jugen zamani
Baka gadi tsoro gunmu hakkan ka sani
Ko mumini mai quwwatu lil imani
Tunda randa kas san wanda yaika mai sama
Samo rashi, khairan da Sharran ya gama
Bamai ije maka dai cikinsu, tsaya ruma
Komi taho maka hankuri zaka yi zama
Ka wakkalawa ubangiji Rahmani
Kai dan'uwa na so ka lura ka rarrabe
Ga abinda yaffi gareka don ka fice kure
Rike gaskiya ka santa me kake lalube
Inda kasan tuba kakan rike gwadabe
Daba kaji tsoro ba don hidhyani
Kullum ina jin wa'azi inda shuyukina
Nazo karatu naji gun ulama'una
Subhana, kin ji yai yawa don son ghina
Madalla Maryamu kin tuna min na tuna
Can da wuri na zauna cin nasyani
Na kasa farga yau da gobe suna zuwa
Ga mutum shi kasa abinda yayi cikin fa wa
Karfi shi kau da gani, shi kau sha mantuwa
Na kasa tuba ga zunubbai sun yawa
Kuma ga shuyukhi ga halin sibyani
Na roki Allah Jalla shi ka isam mini
Ga abinda yas same ni shi ka biya mini
Ga abinda nis so zahiri in badini
Na tuba ya Allahu gafarta mini
Don Shehu nurin zamanin Usmanu
Tun nan da barzakhu lahira a shi taimaka
Aikin da niyyi na gaskiya shi biya garan
Shi hana ni muggun yalla ko da nufa kadan
Astagfurullaha l' azima shi agazan
Don shehu Abdulqadir Jilani
Domin Rufa'i ubangiji ka raba mana
Rokon da nai maka don badai ka isan mana
Haka na Dasuki gare su nan muka dangana
Da zaman kushewa har kiyama Rabbana
Amsar Takardu agazan Mannanu
Kogi; Daga Limamin Daura Usman 1899
Wannan Waka dai an rubuta ta ne a daidai lokacin da Turawa suka shigo Arewacin Nijeriya. Limamin Daura Usman ne ya rubutata, domin yayi kira ga Sarakunan Kasar Daura, dasu daina zalunci, ya kuma nusar da talakawan kasar illar zalunci. A dalilin rubuta wakar, sarakunan Fulanin Daura suka kore shi, inda ya tsere zuwa Sakkwato, a daidai lokacin da Turawa suka koro Sarkin Musulmi Attahiru. Ana kyautata zaton, ya mutu aBurmi tare da Sarkin Musulmi Attahiru. Ga dai wakar;
Kusan zulmu zulmatun ne a yaum al qiyamati
Fada ta rasulillahi manzo muhammada
Ku shimfida adalci gabas, duk da Yamma da
Kudu da Arewa, du ga ummar Muhammada
Ina Dogarai har Jeka fada da kwarakwarai
Da mata na fada, ku zo ku saurara fa'ida
Kaza yan lifidda, har da yan bindiga duka
Zagage ku saurara har ku samo fa fa'ida
Kaza yan baraya harda yan garkuwa duka
Da yan figini du da mai so yasan fa'ida
Fa kai kuwa wawa dai na wauta cikin gari
Ka dawo ga hanya kasan rahamar Ahmada
Fa ku kuwa yan sarki ku bar bin garuruwa
kuna kwace amfanin mutane mufassada
Kuna yin Kilisa don leka gidaddaje
Kuna gane matanmu kuna sabawa Muhammada
Fa ku kau talakawa fakirai ku zam ku ji
Saraki na sarki ne, Talakka na rabbana
Ina masu sanya ruwa a nono su sai
A kaisu sa'ira gobe nesa ga Ahmada
Wadansu su sa gawasa da kaya su garwaya
Fa domin su sai da guba, su sabi Muhammada
Wadansu dafare su kan sa su garwaya
Su sai she si don basu kamnar Muhammada
Wadansu da yan kuka su barka su garwaya
Suna shan azaba, gobe nesa ga Ahmada
Wadansu suna sanya ruwa su kara da kankani
Abin na haramun ne na nesa ga Ahmada
Ana masu kanwa? to ku saurara nan fadin
Ku tuba ga algushu, na nesa ga Ahmada
Su dibo fara toka su kawo su garwaya
Su saishe to domin basu kamnar Muhammada
Kusan zulmu zulmatun ne a yaum al qiyamati
Fada ta rasulillahi manzo muhammada
Ku shimfida adalci gabas, duk da Yamma da
Kudu da Arewa, du ga ummar Muhammada
Ina Dogarai har Jeka fada da kwarakwarai
Da mata na fada, ku zo ku saurara fa'ida
Kaza yan lifidda, har da yan bindiga duka
Zagage ku saurara har ku samo fa fa'ida
Kaza yan baraya harda yan garkuwa duka
Da yan figini du da mai so yasan fa'ida
Fa kai kuwa wawa dai na wauta cikin gari
Ka dawo ga hanya kasan rahamar Ahmada
Fa ku kuwa yan sarki ku bar bin garuruwa
kuna kwace amfanin mutane mufassada
Kuna yin Kilisa don leka gidaddaje
Kuna gane matanmu kuna sabawa Muhammada
Fa ku kau talakawa fakirai ku zam ku ji
Saraki na sarki ne, Talakka na rabbana
Ina masu sanya ruwa a nono su sai
A kaisu sa'ira gobe nesa ga Ahmada
Wadansu su sa gawasa da kaya su garwaya
Fa domin su sai da guba, su sabi Muhammada
Wadansu dafare su kan sa su garwaya
Su sai she si don basu kamnar Muhammada
Wadansu da yan kuka su barka su garwaya
Suna shan azaba, gobe nesa ga Ahmada
Wadansu suna sanya ruwa su kara da kankani
Abin na haramun ne na nesa ga Ahmada
Ana masu kanwa? to ku saurara nan fadin
Ku tuba ga algushu, na nesa ga Ahmada
Su dibo fara toka su kawo su garwaya
Su saishe to domin basu kamnar Muhammada
Thursday, April 5, 2007
Wakar Zuwa Birnin Kano; Daga Aliyu Dansidi Sarkin Zazzau
Sarkin Zazzau Aliyu Dan Sidi shahararren Sarkin ne a Arewacin Nigeria, yayi fice saboda irin fasaharsa da illiminsa, shi kuma ne sarkin Zazzau na farko da Turawa suka nada. Turawanne kuma suka sauke shi, bayan sun samu sabanin ra'ayi akan wasu sauye-sauyen zamani. Ya zama sarki yana da Shekara Sitiin da hudu (64), yayi sarautar Zazzau daga 1903-1920 . Jikan Sarkin Zazzau Musa ne, Bamalli. Wani abin sha'awa gameda da tarihinsa shine, shi dai bai taso a gidan Sarautar Zazzau ba, ya taso a gidan malanta ne, a hannun malaminsa Limamin Durum wato malam Abubakar. Ya taba samun sabani da Sarkin Zazzau Kwasau (Mai kogin Jini dan Sambo), wanda hakan ya sanya bar Kasar Zazzau, ya shiga yawace-yawace, inda har ya Zauna a kasar Kwantagora a zamanin Sarkin Kwantagora Ibrahim Nagwamatse. Ya wallafi wakoki da dama, cikinsu kuwa akwai Tabarkoko, Saudul Kulubi, Wakar Diga da kuma wannan waka ta Birnin Kano.
Ance wannan waka yayi tane, yayi wata Dabar bankwana da Sarakunan Arewacin Nijeriya suka shiryawa Gwamna Arewacin na Zamanin Turawa wato sir Hugh Clifford, a Birnin na Kano acikin shekara 1914. A zamaninsa akan masa kirari da "Aliyu na Awwa mai iya Sarki" . Sarkin Zazzau Aliyu dan Sidi Batijjane ne na kwarai, domin mun kawo muku wakarsa da yayiwa Shehun Darikar ta Tijjaniya wato Shehu Ahmad Tijjani, ga mai so sai ya duba cikin kudayen Turaka wato Archives. Ga dai Malam Aliyu dan Sidi a Birnin Kano.
Muna gode Allah da yayi nufi
Yasa muka taru a kofar Kano
Muna yin Salati bisa ga Muhammad
Dalilinsa anka yi mu akayi Kano
Mu kara salati bisa ga sahabbai
Mu sami dalilinsu komi anu
Zama hali ma nahnu shi muka zance
Da niy yi shiri zani birnin Kano
Diya min Muharram ga ran Lahadi
Na hau bisa jirgi zuwa na Kano
Ga Chalawa ni kwana guda muka tashi
Muna gaisuwa da dawakan Kano
Dawaki na baki kaza yan gari
Fa har muka sadu da Sarkin Kano
Da fa muka gaisa ya juya na bishi
Dada har ya kaini masauki Kano
Ina gaida masu zuwa daga nesa
Da shaihu na Kukawa ga shi Kano
Da Mahoni Laraba Gaidan Kano
Kaza Lamido Adamawa a birnin Kano
Katagum, Hadejia, kaza duk da Gombe
Misau Jama'are a birnin Kano
Da Zazzau da Bauchi, kaza Katsina
Da Daura, Gumel gasu birnin Kano
Kazaure da kau Sakkwato har da Gwandu
Kabawa da Argungu birnin Kano
Mutan Gwadabawa da Kwanni da Yabo
Gamuwa da Anka a birnin Kano
Da Meri da Augi mutanen Yamma
Mutan Jega ga su a birnin Kano
Mutan Wukari, mutanen Ibi
Da Loko da Lokoja a birnin Kano
Da Yawuri har Kwantagora Rijau
Mutan Wushishi da Bussa a Birnin Kano
Kushurki da Kunguna har Kuriga
da Gwari na Waki a taron Kano
Mutanen Maginga mtan Kanbuwa
Na Sulame gasu a birnin Kano
Illori, Nufawa, Lafai, Agaye
Fa hatta Abuja a birnin Kano
Fa har Tunkiya gata ga Damisa
Mashayansu dai sunyi kiwo Kano
Kutawa mutanen Kafi, Lafiya
Da jam'an ta Baroro a birnin Kano
Da Mahmudu Ningi da Sarkin Bura
Da Sarkin na Bassa a birnin Kano
Ina gaida Sarkin Kano Yayi Aiki
da anka yi taro garinsa Kano
Gidaje na sabka dada har liyafa
Da taryan sarakai su sabka Kano
Da sabkan farare da sabkan bakake
da birni da kauye a birnin Kano
dalili gareni in san yayi aiki
Zama nayi ko da nika je Kano
Da shi da ya sabkar da su masu sabka
Ta'ala shi bamu sawaba Kano
Fa naje da yare iri da yawa
Da busa da ganga a taron Kano
Fitawa da doki dako Feluwa
Da sayi suna sukuwa nan Kano
Mutane da doki da niz zo dasu
jimillansu hamsa zuwana Kano
Kurama, Katab har da Cawai duka
Fa duk sunyi wasa a taron Kano
Da Jaba da Gwari mutan Rumaya
Kadara fa na kai su taron Kano
Ga babban suka na dawakan saraki
Na Zazzau fa sun ka ci taron Kano
Da anka yi wasa fage ya hadu
Muhudanmu sun yi ado nan Kano
Ka rarra, ka Kabra, ku san tumkiya
Bata iya kabra ba Kano
Da tauri da tsauri idan anka goga
Guda sai shi yanke guda a Kano
Ba'an gwada karfe ba, sai inda karfe
Duwatsu fashewa su kai a Kano
Ka zaga Kano har kasan dan Kano
Na birnin Kano wanda yasan Kano
Ka kau tambaye shi tsakani da Allah
Ya bayyana maka taron Kano
Na yawata Kano gani ga dan Kano
Dada har nasan anguwa a Kano
akwai anguwan madawkin Kano
Da sunanta Yola a birnin Kano
Daneji, da Soron dinki akwai su
akwai Lungunawa da Sheshe Kano
Da Marmara duk unguwa ce duka
da Kunduke Kwankwaso duk a Kano
Akwai Wudilawa akwai Na'ibawa
Da Ibadi Fasa-keya a birnin Kano.
Caranci, Gudundi, akkwai Jarkasa
Makankari, Garko duk a Kano
Kusura, Kudancin Kano da Wazirci
Da Siradi akwai ta Kano
Karofi na Wanka da Shuni akwaisu
Madatai da Daushi akwai su Kano
Karofi na Sudawa, Zangon Ciki
Da Dandago, Diso akwai su Kano
Akwai unguwar Durunmin Kaigama
Da Bulbulas, Guntu akwai su Kano
Da Yalwa da Dala, Madaboo duka
Suna nan Arewa da Kurmin Kano
Akwai wata ko unguwa Masaka
Da Sarari da Sagagi Birnin Kano
Awai unguwa Waitaka a Kano
Akwai Durumin Dakata min Kano
Mahanga, Kutumbawa duk unguwa ce
Da Damtsenka Tsage a Birnin Kano
Akwai Cediya ta Kuda unguwa ce
Akwai Kalaman Dusu duk a Kano
Da Lallokin Lemu, da kau Makwarari
Makwalla fa duk unguwa ce Kano
Dabinon Awansu da Mandawari
Da Alfindiki Kwalwa duk a Kano
Tsaya in gajarta guda don kau yawaita
In kawo wurinta da niyyi Kano
Fa har muka kare naje Nasarawa
Garin makarantan su Sambon Kano
Akwai makaranta karatun Bature
Acan Nasarawa ta kofar Kano
akwai yara masu Karatu na allo
Akwai masallaci ginanne Kano
AKwai Makaranta ta al Kur'ani
Da litattafanmu a birnin Kano
Akwai wani dakin zaman masu ciwo
Akwai matsarinsu a kofan Kano
Masaka, madunka, da mai Sassaka
Gidansu guda makarantan Kano
Makera, Badukai da masu kudi
Cikin makaranta ta kofar Kano
Cikin shekara goma sha dai ga daula
Aliyu binu Sidi zuwanshi Kano
Ya wake ta yan baya domin su ji
Su san wakacin tafiyanshi Kano.
Ance wannan waka yayi tane, yayi wata Dabar bankwana da Sarakunan Arewacin Nijeriya suka shiryawa Gwamna Arewacin na Zamanin Turawa wato sir Hugh Clifford, a Birnin na Kano acikin shekara 1914. A zamaninsa akan masa kirari da "Aliyu na Awwa mai iya Sarki" . Sarkin Zazzau Aliyu dan Sidi Batijjane ne na kwarai, domin mun kawo muku wakarsa da yayiwa Shehun Darikar ta Tijjaniya wato Shehu Ahmad Tijjani, ga mai so sai ya duba cikin kudayen Turaka wato Archives. Ga dai Malam Aliyu dan Sidi a Birnin Kano.
Muna gode Allah da yayi nufi
Yasa muka taru a kofar Kano
Muna yin Salati bisa ga Muhammad
Dalilinsa anka yi mu akayi Kano
Mu kara salati bisa ga sahabbai
Mu sami dalilinsu komi anu
Zama hali ma nahnu shi muka zance
Da niy yi shiri zani birnin Kano
Diya min Muharram ga ran Lahadi
Na hau bisa jirgi zuwa na Kano
Ga Chalawa ni kwana guda muka tashi
Muna gaisuwa da dawakan Kano
Dawaki na baki kaza yan gari
Fa har muka sadu da Sarkin Kano
Da fa muka gaisa ya juya na bishi
Dada har ya kaini masauki Kano
Ina gaida masu zuwa daga nesa
Da shaihu na Kukawa ga shi Kano
Da Mahoni Laraba Gaidan Kano
Kaza Lamido Adamawa a birnin Kano
Katagum, Hadejia, kaza duk da Gombe
Misau Jama'are a birnin Kano
Da Zazzau da Bauchi, kaza Katsina
Da Daura, Gumel gasu birnin Kano
Kazaure da kau Sakkwato har da Gwandu
Kabawa da Argungu birnin Kano
Mutan Gwadabawa da Kwanni da Yabo
Gamuwa da Anka a birnin Kano
Da Meri da Augi mutanen Yamma
Mutan Jega ga su a birnin Kano
Mutan Wukari, mutanen Ibi
Da Loko da Lokoja a birnin Kano
Da Yawuri har Kwantagora Rijau
Mutan Wushishi da Bussa a Birnin Kano
Kushurki da Kunguna har Kuriga
da Gwari na Waki a taron Kano
Mutanen Maginga mtan Kanbuwa
Na Sulame gasu a birnin Kano
Illori, Nufawa, Lafai, Agaye
Fa hatta Abuja a birnin Kano
Fa har Tunkiya gata ga Damisa
Mashayansu dai sunyi kiwo Kano
Kutawa mutanen Kafi, Lafiya
Da jam'an ta Baroro a birnin Kano
Da Mahmudu Ningi da Sarkin Bura
Da Sarkin na Bassa a birnin Kano
Ina gaida Sarkin Kano Yayi Aiki
da anka yi taro garinsa Kano
Gidaje na sabka dada har liyafa
Da taryan sarakai su sabka Kano
Da sabkan farare da sabkan bakake
da birni da kauye a birnin Kano
dalili gareni in san yayi aiki
Zama nayi ko da nika je Kano
Da shi da ya sabkar da su masu sabka
Ta'ala shi bamu sawaba Kano
Fa naje da yare iri da yawa
Da busa da ganga a taron Kano
Fitawa da doki dako Feluwa
Da sayi suna sukuwa nan Kano
Mutane da doki da niz zo dasu
jimillansu hamsa zuwana Kano
Kurama, Katab har da Cawai duka
Fa duk sunyi wasa a taron Kano
Da Jaba da Gwari mutan Rumaya
Kadara fa na kai su taron Kano
Ga babban suka na dawakan saraki
Na Zazzau fa sun ka ci taron Kano
Da anka yi wasa fage ya hadu
Muhudanmu sun yi ado nan Kano
Ka rarra, ka Kabra, ku san tumkiya
Bata iya kabra ba Kano
Da tauri da tsauri idan anka goga
Guda sai shi yanke guda a Kano
Ba'an gwada karfe ba, sai inda karfe
Duwatsu fashewa su kai a Kano
Ka zaga Kano har kasan dan Kano
Na birnin Kano wanda yasan Kano
Ka kau tambaye shi tsakani da Allah
Ya bayyana maka taron Kano
Na yawata Kano gani ga dan Kano
Dada har nasan anguwa a Kano
akwai anguwan madawkin Kano
Da sunanta Yola a birnin Kano
Daneji, da Soron dinki akwai su
akwai Lungunawa da Sheshe Kano
Da Marmara duk unguwa ce duka
da Kunduke Kwankwaso duk a Kano
Akwai Wudilawa akwai Na'ibawa
Da Ibadi Fasa-keya a birnin Kano.
Caranci, Gudundi, akkwai Jarkasa
Makankari, Garko duk a Kano
Kusura, Kudancin Kano da Wazirci
Da Siradi akwai ta Kano
Karofi na Wanka da Shuni akwaisu
Madatai da Daushi akwai su Kano
Karofi na Sudawa, Zangon Ciki
Da Dandago, Diso akwai su Kano
Akwai unguwar Durunmin Kaigama
Da Bulbulas, Guntu akwai su Kano
Da Yalwa da Dala, Madaboo duka
Suna nan Arewa da Kurmin Kano
Akwai wata ko unguwa Masaka
Da Sarari da Sagagi Birnin Kano
Awai unguwa Waitaka a Kano
Akwai Durumin Dakata min Kano
Mahanga, Kutumbawa duk unguwa ce
Da Damtsenka Tsage a Birnin Kano
Akwai Cediya ta Kuda unguwa ce
Akwai Kalaman Dusu duk a Kano
Da Lallokin Lemu, da kau Makwarari
Makwalla fa duk unguwa ce Kano
Dabinon Awansu da Mandawari
Da Alfindiki Kwalwa duk a Kano
Tsaya in gajarta guda don kau yawaita
In kawo wurinta da niyyi Kano
Fa har muka kare naje Nasarawa
Garin makarantan su Sambon Kano
Akwai makaranta karatun Bature
Acan Nasarawa ta kofar Kano
akwai yara masu Karatu na allo
Akwai masallaci ginanne Kano
AKwai Makaranta ta al Kur'ani
Da litattafanmu a birnin Kano
Akwai wani dakin zaman masu ciwo
Akwai matsarinsu a kofan Kano
Masaka, madunka, da mai Sassaka
Gidansu guda makarantan Kano
Makera, Badukai da masu kudi
Cikin makaranta ta kofar Kano
Cikin shekara goma sha dai ga daula
Aliyu binu Sidi zuwanshi Kano
Ya wake ta yan baya domin su ji
Su san wakacin tafiyanshi Kano.
Subscribe to:
Posts (Atom)