Wednesday, April 4, 2007

Wakar Kuyangin Sakkwato; Daga Sandan Baba1900

Acikin wasu Kundayen adana rubutattun wakoki dake National Archives Kaduna, an tsinci wani File mai No O/AR 2, wanda ke dauke da wata wakar ajami, wadda F Edgar ya samo a shekarun farko na karni na 20. Acikin File na 20 ne wannan waka take, wadda aka hakkake an kattama shi acikin shekara 1911. Bisa ga dukkan alamu Edgar ne ya kwafi wakar da hannunsa, cikin wata takarda falle daya, wanda aka tabbatar da cewa, zai wuya a samu inda ya kwafo wakar. Amma duk da haka ya rubuta sunan wanda ya kwafa, ko kuma ya wallafi wakar wanda ya kira da Sandan Baba. Sai dai kuma bai bayyana kowaye shi wannan Sandan Baba ba, ko kuma mutumin ina ne shi, ko a ina ya ganshi, kwafa yayi daga gurinsa, ko kuma reara masa yayi, shi kuma ya rubuta, Allahu a'alamu? Sai dai a wani File mai no 61, wanda aka sanyawa kwanan wata kamar haka; 1909, an rubuta wata waka maisuna "Wakar Yabo/Bege" , daga Sandan Baba mutumin Sakkwato, inda aka bayyana cewa, Sandan Baba ya rerawa wani malami wai shi Malam Bako wakar, shi kuma ya rubuta ta. Wannan ya dan bada haske na gano cewa, Sandan Baba dai ya reara wakar ne, inda Malam Bako da Frank Edgar suka kwafe ta, ko kuma shi malam Bako ya kwafa, shi kuma Edgar ya samu a wurinsa. Bisa ga dukkan alamu, Edgar bai san Sandan Baba ba, amma yana da masaniya akan Malam Bako.
Wakar dai ta kunshi abubuwa uku, akwai Zambo, Habaici da kuma Yabo. Badai takamaiman kowa akewa wadannan abubuwa, ko duk mutum daya ne, ko kuma mutane da dama. Amma dai kusan sanin kan kowane cewa, abune ba sabo ba ga Yanmatan kasar Hausa, su kirkiri waka don Yabo ko Fallasa, da sigar Gada. Don haka tabbas wakar dai ta Yanmata ce, da suka rera, saboda wasu dalilai da dama.
Ga dai wakar yadda take:

Shiririta ararrata
Kare gadon gida yayyo

Bani bukinka da shara
Sai ranar zuwa aiki in baka taro ka futassan

Farin wake na banza ne
Ko an matsu ba'a gumbatai

Bambeni ka gara gije
Kurche gidansu tag gado

Domin Biri a janye kadarko
Bika da shirin tuma yazzo

Kwa bace ni in rama
Don ba shi ka chi san ba

Anini mai kammarSisi
Da tsakka gashi fudajje

Kwabo kau mai kamar Fataka
Da tsakka gashi fudajje

Mai-Gwanja gaton shigifa
Na mallam-dan-majidadi

Mai kyautar dala da dala
Na malam-dan-majidadi

Diyal laka ta banza ta
Don bata zuwa tayo wanka

Diyal Danko ta banza ta
Don bata fita cikin rana

Zancen daka sai mata da miji
Hanyar bisa dole sai tsuntsu

Garar kasa maganin ajiya
Zago mai fanfatse kaya

Bani zuwa ga yanboko
Gara nazo ga yan madara

Dan boko sai hawan doki
Amma ba kudin sati

Mai rai duk masami ne
Zabarma akwai bidar kuddi

Limamin gidan Joji dogo ketare ka ciro
Har ya manta wando nai

Kuku da Boyi sun rantse
Sai sun dauki yar gwari

Tulu dai ka shan yawo
Randa na nan cikin daki

Mai rai duk shi dau himma
Ayi ta batun bidar kuddi

Dan kawo rinin Allah
Madilla masoyina

Namijin kuti mai kafar kwabi
Har ya raina matatai

Randa na cikin daki
Allah shika bata ruwa ta sha

Tukuruwa mai kaya boye
Gawo da kayarka ka girma

Tataka sai aba doki
Nama sai aba Zaki

Tafarnuwa ta faye yaji
Amma ga maganin sanyi

Dabino farkon ka Baure ne
Acan karshe kake zaki

Anini dan mutan Lokoja
Bana yazo kasar Hausa

Kwa doke ni in rama
Don bashi ka tufasan ba.

Ga mai son jin cikakken bayanin wakar sai ya nemi makalar da Grahm Furniss da Yunusa Ibrahim suka gabatar, mai taken; An Early Twentieth Century Song: "Wakar Kuyangin Sakkwato" A mujallar Harsunan Nijeriya, xvi, 1991/92. CSNL Bayero University Kano. Nigeria.

No comments: